Showing 45001 words to 48000 words out of 388021 words

Chapter 16 - Tarko Book Complete Book by Zainab Makawa.doc

24 Sep 2025

8223

aman na da wanan auren da zaiyi a birni ba acikin gida ba,
Amma yadda zasu yi don dole suka ja bankin su sukai shiru,
Baba Hamza da Baba samaila da Baba yahayya sune zasu tafi sai wani makwabcin su wanda shima anan cikin unguwar shiyar sarakuna yake da zama akusan shakuwar gidajen biyu ya koma zumunta, sosa,,,,

****** ******** ******
Tun da safe take kokarin kiran layin wayan shi amma not reachable ake ce mata,
Har zuwa yanzu da wayan mobile din ta ya nuna mata karfe biyar da rabi na marance,
Don haka ta sake kiran layin shi din don taji ko zai shiga,
A cikin sa,a ta ji layin yana ringing alamar kiran na shiga,
Allah Allah salawatu takeyi ya dauki wayan amna sai ba,a dauka ba,
Wanan abin ne ya tayar mata da hankali sosai har ya sa ta shiga wani dan hali,
Azaton Salawatu ko a gida iyayyen Abubakar sun yi rejected din zancen ta da shi ne,
Dole badon taso ba ta dai,na kiran shi acikin damuwa take sosai ,
Sai musalin karfe takwas na dare ne taji call a wayan ta tana dubawa taga ashe Abubakar ne a layin
Cikin zumudi ta dauki wayan tana mai kashe murya, ta,
Da sallama yafara zance kamar kullun don hakan akidar shi ce shi,
Ina,shiga gari da,zun naga kiran wayan ki a lokacin a kwai go slow sosai a hanya,
Ya hanya Sir ya mutanen gida,?
Ya kabar su mama da sauran jama,a,
Sosai yaji dadin wanan maganar da takeyi mai don ta nuna mai kulawar ta akan yan uwan shi,
Shiru ne yadan biyo bayan hirar nasu sai ita salawa din ce ta kau da shirun tana tambayan aka maganar da ta kai shi gida,
Dariya yai mata inda yaje cewa ai nasan cewa shine dalilin kiranki haka tunda,zun,
Cikin jin kunya tace No sir ba hakana bane ,
Saidai dama don ina son inji ko zasu yarda dani ne in zama surukar su ko
Nan dai ya ce mata gajar ce ki zauna ashiri don anytime zamu iya ganin parents di na agarin nan akan issue din mu,,
Wani irin dadi ne ya ziyarci zuciyar salawatu a lokacin,
Inda harda dan ihun ta don jin dadi wanda har ta kasa boyewa,
Murmushi Abubakar yayi a bangaren shi don dai shi dariya ta bashi sosai,

****** ******** ******
Saye take a cikkn rigar barcin ta wani mai ruwan ja, jajir,
Kanta yana daure da ribon wanda ta kama kan tun daren jiya da zata kwanta,
Kitchen din ta shiga don ta kama ma mummy girkin safe kasan cewar itace da girki yau kuma tana dakin maigidan
Idan abin ta mummy bazata fito ba sai rana ya haska sosai,
Wayan ta dake gefe guda gurin da take tsaye tana fere dankalin turawa,
Idanun ta kawai ta dora akan screen din wayan ba tare da ta dauka ba,
Dan uwa tagani a rubuce, kan screen din wayan nata,
Wani lalausar murmushi ta sake, a lokaci guda tare da saurin kokarin aje yukan da ke a hannun ta na firar dankalin da takeyi
Bayan ta ta jingina da abin zinc din dake cikin kitchen din,
Fuskanta dauke da murmushi tace Assalamu Alaikum
Tankar Abdulhamed din ya na gurin a lokacin
Meenat wacs haduwar ta da Abdul ya kawo mata wasu sauyin ra,ayi da dama, yanzu,,,
A cikin wanan zazzakar muryan nata tai masa sallama tare da lumshe ido,
Abdull wanda a lokacin yana tsaye da yar three quarter wando yana kallon Birch daga masaukin su,
Bayan sun gaisa ne take cewa cikin muryan nata mai sanyi,
Ya hanya dan uwa da fatan ka isa lafiya dai ko ya gajiya da jama,a
Gajiya Alhamdullah sai dai ta kasa samun sukuni saboda ke Meena,
Kai dan uwa saboda ni fa kace. ?
Murmshi ta sake mai tare da cewa kai dan uwa fadi dai gaskiya ko dai gajiyar wanan dogon hanya da ka sha,
Au to baka yarda ba to bari ki ji da kunnuwar ki ko zaki gaskan ta,
No barshi kawai ai na yarda don nasan baka fada min karya
Murmushi yai mata don yardan da tayi a lokacin guda
Tabbas yasan cewa meena tana son shi sosai kamar yadda shima yake sonta,,
Hira sosai sukayi na ina kwana ya gajiya ya kewan dan uwa ?
Daga karshe take fada mai cewa tana kitchen zata hada break fast ne, don haka ya kyale ta badon yaso ba,

****** ******** ******

Dukkan su hudu a vikin shigar manyar riguna suke, don girmamawa,
Sun isa garin lafiya cikin gajiya, don haka masaukin da Abubakar yai masu a wani hotel da aida nisa da uguwar dasuke,
Sai dai su basu so hakan ba tun ma dai da aka ce wai har abinci duk na hotel zasuci,
Baba hamza ne yafara magana yana cewa gaskiya Abubakar ka tona muna asiri
yanzu a ce abinci da kafirai sunka dafa shina zamu,
Baba Samaila wanda yake kokarin nade hannun rigar shi yace cikin shirin daura alwala,
Don yin sallolin dake gaban su tun rana,.suke saman hanya,
Washe gari ne da safe suka je yin abinda ya kawo su watsu ne man aure,
Tun kafin su shiga suka fara ganin abin assha aciki don yawanci a cikin shi
Duk jikin su ba sitirun karai ga kuma gidan da kazanta,
Sai kuma babu wani babba mai tsayayye a gurin du taron yara ne,
Duk a matse suke da su bargida don basuga wani sbin kwarai ba da har dan su zai so hada zuria da irin wa yan nsn mutane ,
Daidai da zasu wuce shi baba hamza ke tambayar wacece sarakuwar tashi,
Wata babban mace da ke saye da dogon rigar atamfa ya dan dane mata jiki wai itace dan nasu ke so hada zuria da ita ,
Tun a hanyar su ta dawowa masauki suke suka fara sauke numfashi an rasa wanda zai fara magana daga cikin su,,,,
Shiko Abubakar din sai jin dadi yakeyi Salawatu ta kusa dawowa hannun shi,
Zai zama tankar kamar kowani magidanci shima yayi yadda masu aure keyi,
Sam idon shi ya rufe bai hango abinda iyayyen shi suka hango mai ba,
Baba yahaya yace ko shi dai da yake uba ga Abzai kwashi wanan tsohuwar mace ba wai mata,
Baba Samaila ne yai masu magana akan su daina don komai ra,ayine,,


ZEEE MAKAWA YELWA
[7/13, 9:54 PM] MAKAWA: =?x?=?x?=?x?TARKO=?x?=?x?=?x?
=?x?=?x?=?x?=?x?=?x?=?x?
2? 0?
ZAINAB IDRIS MAKAWA


ALLAH AL-JABBAAR

Duk kan su hudu ne zaune cikin ladabi a gaban malam,
Dawowar su ke nan ko gida basu shigaba a lokacin ,
Sun tsaya don su sanar wa da malam sakon gabacin da aka,aike su yi, a can
Baba Sanaila ne yai saurin tare yan uwan nashi don gudun kada su aiban ta zancen a gaban malam mahaifin su kamar yadda su ksi tayi a can,
Dafarko ya fara cewa malam Allah ya dawo damu lafiya,
Abubakar da iyalinshi su na gashe ka kwarai da gaske,
Ya ce muyi masa godiya sosai a gurin ka kafin yazo,
Can kuma gidan ita matar muntafi gaskiya sun karbe mu hannu bibiyu sun kuma yi munar sosai, don haka muma muka gabatar da komai kamar yadda ya kamata ayi,
Baba Hamza' cikin wani irin kallo da yakewa dan uwan shi ya kasa hakkuri yace,
Haba samaila may zai sa ka boyewa malam gaskiyan zancen,
Tunda tura mu yayi don mu wakilci gidan mu, mun kuma je munga akasi a gara mu fada mai don ya san yadda za,a bullowa abin ko ?
Haba yaya Hamza' haka bai dace a gare mu a matsayin mu na iyayye ga Abubakar ,
Ganin yadda suka fara kaulewa da gardama yasa malam tsoho dakatar da su a cikin daga hannu irin na manya,
Inda ya ce haba ba aiken ku nayi ba,aigara ku tsaya ku fada min gaskiya don kar sai abu ya baci adawo kuma ana da,an sani,,,
Gaskiya kan inji wanan dattijon guda da suka tafi tarr da shi Abuja, watau makwabcin su,
Yanzu kai malam sani fada min duk yadda akai don Allah saboda hakan ne ai na hada ka da su,
Gyara murya malam sani yayi yafara da cewa to a gaskiya malam ba irin arziki za a dauko a gidan ka ba,
Darajan gidan ka da mutuncin gidan ka bai,dace a ce yaron irin wanan zirian ya auro mace irin wancan matar da muka gani don sam babu tarbiya,
Baba yahaya ne yajefa baki da cewa ga shi kuma ta girmi shi Abubakar din,
SUBBAHANALLAH inji malam tsoho shi Abubakar din ke kuma son ta a hakan ?
Kwarai kuwa don da muka tafi ya nuna muna jin dadin shi kwarai da gaske a lokacin,
Shiru malam tsoho yayi batare da ya iya cewa ufan ba saboda atake zuciyar shi ta baci
Baba Buhari wanda tun,fara magana bai iya cewa komai ba sai kai yake kadawa kawai a lokacin
Can ya ce watau shi mai sunan malam sabon al,amari yake son kawo muna kuma ke nan?
Gaskiya hakan ba zai yuyu ba sam dole ne idan har aure yake son karawa ya dawo gida ya zaba a cikin dangi ko yan wanan yankin,
Ido kawai malam tsoho ya kura masu baki dayan su yana nazarin abubawa daga zancen kowan su,
Baba Hamza yace aiko a nan gida muna da yara sai ya zaba daga sashen shaibu ko yahaya da hamza,
Sam bai kawo sunan Baba Samaila ba wanda ke da yar matashiyar diya guda acikin su,,
Shima din sam bai damu ba don dama ba wai wanan karon bane suka fara numai haka ba,
Komai a yasu,yasun su suke abin su sai, dai su ware shi shi kadai koda yar uwar shi
Mikewa yayi don jin inda zancen ya juta akala yana mai ce masu to jama,a mukwana lafiya fa,
Dag haka ya shige abin shi cikin gida zuwa gurin iyalin shi,
Ido malam tsoho wanda ke daga kishigide yabi dan nashi dashi kawai don yasan halun samaila sai shi,
Samaila mutum ne mai murdaden halin wanda ba ruwan shi da shiga shirgin wani arayuwan shi,,,

****** ******** ******
Tafiya take yi a hankali kasancewa rana yau yai zafi,
Wanda hakan yasa masu abin hawa sukai karanci a saman titin a lokacin,
Tafe take da irin takon ta tankar tana tausayin kasa, ne
Wata bakar mota lafiyyaya ta zo ta harba a saman titin,
Can kuma Meena ta hango motar na yowa baya baya
Har zuwa daidai inda take batare da ta waiga ba don ganin gurin da motar take
Sai ji tayi mai motar na dan dana mata hon din motar,
A hankali ya sauke glass din motan inda yake cewa, Beauty daga ina kike haka a cikin wanan ranan ?
Sai a lokacin Meena tajuyo don ta ga waye ke mata magana,
Ta tsura masa manyan idanuwan nan na ta , wanda ke rikita duk mai kallon ta,
Ali,Abbas ne taga yana sakar mata irin shu,umin murmushin nan nashi,na ranan,
Bakin shi na yar kyarma cikin rawan murya da ganin fuskan ta ya ce kizo in rage maki hanya pls,
Ranan nan yai yawa kada ya illanta mun ke pls,
Meenatu wace ta kada idon ta wai ita harara ta dan rausaya kanta gefe guda cikin yar yatsune fuska, tace,
Kayi hakkuri malam don ni bana shiga mota da namiji dagani sai shi,,
Daga haka ta juya abinta taci gaba da tafiyan ta,.
Murmushi Ali, Abbas yayi, don yasan abinda ta fadi har cikin ranta haka zancen yake,
Don haka sai bai matsa mata ba yasa kai abin shi zuwa gurin da ya nufa,

Meena wacce tasha tafiya donbdaga karshe hakkura tayi da ta sara da kafa kawai tun da har takawo nan babu yar vespa,
Da kyat taga gida don haka ido rufe ta iso, sai dai gidan na tsit a lokacin,
Batai mamaki ba don tasan yaran gidan suna makarantan islamiya a wanan lokacin ,
Gurin Fridge ta nufa don ta sha ruwa ta duka ta dauko goran ruwa masu sanyi ta kafa kai da niyar sha,
Har tasha takai rabin yar, goran, sai taji an rungumo ta ta baya,
Wa, iyazu billah,,,
Cikin sauri Meena ta furzar da ruwan da ke a bakin ta lokacin,
Ta juyo a fusace, don ganin ko waye mai wanan dabiar banzan
Ali,Abba's ne ya na sakar mata wani irin shu,umin murmushi a fuskan shi,
Idon ta dan rutse inda tadaga hannu da niyar kai mashi mari,
Cikin sauri ya gwauce, sai bata samay shi ba ta samu iska,
A lokacin wasu irin hawaye masu zafi suka ziyar ci fuskan Meena,
A cikin masifa ta nunashi da dan yatsan ta tace,
Cikin daga murya tace daga yau daga rana mai kamar ta yau kada ka kara shiga tsabagata ko ka nuna ka san ni
Kasa ni cewa ni ba yar iska bace irin ka wanda ya tashi cikin rashin tarbiya,
Kuma ina neman tsarin Allah daga duk wani sheri daga ire, iren ku shedanun mutane,
Daga haka taja wani irin dogon tsaki gami da hararan shi ta watsar gefe guda,
Sai a lokacin hawayen idon ta suka fara yawa a fuskan ta,
Wani kallo ta watsa mai , mai tatare da tsana da kiyayya,
Baki bude Ali,Abbas, ya tsaya yana kallon yadda yar yarinya, karama ke gaya mashi, magana son ranta,
A fusace Meenatu tabi ta gaban shi ta wuce zuwa cikin gida, rai bace,

Direct dakin Anty amarya ta nufa da shiga ta zauna a,bakin gado idon ta na mai zubar da hawaye kawai,
Anty tana fitowa daga bathroom taga Meena acikin wanan halin,
Take hankalin ta ya tashi da sauri ta karaso gurin da Meenat take zaune ta na tambayar ta cikin tashin hankali,
Amma Meenat ta kasa bude baki tayi magana don bakin ciki, da ya mamaye mata rai,
Da tambayar yai mata yawa ne ta kwanta ga kafadar uwar dakin nata cikin kuka take fada mata abinda ya faru,
Rayuwan amarya ya baci sosai nan ta shiga bawa Meena hakkuri har ta samu ta dan sasauta kukan nata,
Shiko Ali,Abbas shigar Meenat ciki yasa shi sauke yar ajiyan zuciya cikin takaici,
A lokacin ne yasan cewa ya tabka babban kuskure don nan kasar hausane ba wai turai ba,
Gashi kuma ko banza Meenat still karamar yarinya ce tukun ba wani girma tayi ba
Gashi Allah yasa mai son wanan yarinyar a rayuwan shitun ranan da ya ganta,
Sam ba zai iya jure rashin taba a halin yanzu don haka dole ne ya jure duk wani cin fuska da zai gani a gurin ta,
Cikin yanayi na rashin kuzari da kyat ya ja kafan shi da yaje jin sunyi masa nauyi,
Tankar bazasu dauke shi ba, ya nufi hanyar fita wajen gidan ran shi a bace,,,,,

****** ******** ******
A cikin gidan malam tsoho ko wani sashe sai kokarin ganin ance yar su za ai wa Abubakar kamay,
Daga sashen Baba Hamza' da Baba Shaibu har da Baba yahaya,
Sai kuma bangaren gidajen gwagwan,nin su suma suna son wanan hadin,
Duk wanan wainar yan gidan Baba Samaila basu da labari sam,
Ko ma suna da a yanzu yar shi bata cikin jerin manyan yan matan gidan, tukun na don duk sun girmay mata sosai,

Malam tsoho wanda yau da kan shi yasa aka kira mai wayan jikan shi na fari Abubakar,
Bayan sallama da gaisawa ne, malam tsoho ke cewa jikan nashi
Kana magana ne da Abubakar manya mai almajirai,
Murmushi Abubakar yayi a bangaren shi sai da malam din yaji tankar yana agaban shi ne,
Abubakar magana nake son yi ta fahinta da kai don mu fahinci junar mu,
Abubakar wanda a lokacin yana zaune yana cin abincin dare, ne ,
Yadan dago kai ya kalli gurin da Sadiya take zaune tana kallon wani shiri a African, magic,
Malam din ya soma da cewa akan zancen auren da kake da burin karawa ne mai suna,
Banji dadin yadda iyayen ka suka dawo suna fada min irin zurian da kake son mu hada iri da su,
Shin mai suna ina tarbiyan ka da sanin ya kamatan ka suka shige da har zaka kwaso wa kan ka irin wanan macen,
Tun a wanan ??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????ookacin rayuwar Abubakar ta baci yaji wani iri a zuciyar shi,
Muryan malam din ce ya dan dakatar dashi daga tunanen shi,
Malam yace kazo gida cikin dangin ka da


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login