Showing 30001 words to 33000 words out of 388021 words

Chapter 11 - Tarko Book Complete Book by Zainab Makawa.doc

24 Sep 2025

8234

store din suka kwasa zuwa inda suka Parker motar su,
Sun fara tafiya ba,a dadeba taji muryan shi yana cewa,
Sannu da kokari miss salawatu, na gajiyar dake da yawa ko ?
Nagode kwarai,
Cikn jin dadi da rausaya kai, tace ma shi,,
You are welcome,,
Murmushi yayi alamar maganar ta ya gamsheshi har zuciya,
Yace godiya nake,
Yar siririyar dariya ta sake tace Sir, kamar wanda nai wani abu wanan godiyan haka,?
Saida ya sake murmushi ya furzar da iskar bakin shi yace mata,
Lokacin ki fa kika bani salawati,
Aikin ga dole na gode maki ko ?
Da kwatance ya isa gidan su Salawa din inda ya fahinci bawasu masu karfi bane gidan su,
Rufin asirine kawai irin na Allah, ke tare da ita,
Kayan da ya siya mata ya bude but din motar takwashe ya kara mata godiya ya sa kai zuwa nashi gidan da kayan tsaraban yan hutu niki,niki,

***** ****** *****
Jin yau cikin ikon Allah, ciwon baiyi mata tsanani irin yadda ya saba yi mata ba,
Tadan rarafo zuwa falo inda ta samu dogon kujera ta kwanta,
Sai,dai daga kwanciyar zaka gane cewa tana cikin wani irin yanayi gaskiya,
Da sallama kamar kullun yadda ya saba shiga gidan nashi ya shigo,
Duk da yasan ba lalaine ya samu ansawan sallamar tashi ba,
Tun daga kofa ya hango ta daga yanayin kwanciyar ta yasa shi gane cewa ba lafiya,
Sai bai kula da yan kan,nenshi dake zaune falon ba cikin yanayin damuwa,
Da wata irin murya ya kira sunan ta cikin nuna kulawa,
Ba tare da ta dago ba ta, ansa mai kiran nashi da naam,
Tsungunawa yayi daidai kanta yana mata magana kasa kasa ta yadda ba dole ba ne wani yaji may yake cewa,,
Hannu ya kai daidai wuyan ta yana taba jikin nata don jin lafiyan ta,
Muryan Aisha ne ya katse mai tabe taben da yakeyi a jikin matar na shi,
Yaya dazun mun ji tsoro sosai irin halin da mukaga anty sadiya ta shiga ,
Sai da Allah ya bamu ikon yi mata addua, da kuma tofi irin yadda malam tsoho ya gwada muna akan ciwon mara,
Daidai lokacin da yake dagowa tsaye da ga duken da yake ne yace mata Ok,
Daga haka yasa kai abinshi ya wuce zuwa ciki,
Gaba dayan su kallon mamaki suka bishi dashi a lokacin irin yadda yai masu,
Kallon kallo suka bi junan su dashi don dai irin yadda ya basar da su,
Sosai abin ya bata masu rai saidai babu halin su nuna tunda yayan su ne,
Kuma kadan daga cikin irin rayuwan shi ke nan, don mai ba hagon hali suke jin iyayyen su na ce mai,
A dakin su inda suke zaune suna ta kus,kus, kowan su a gajiye yake da ya koma gida,
Tun dai manyan su irin su Aisha da murja masu samari
Gashi sun bar,su can ba hira,,nan kuma tunda su,kazo babu inda suka taba zuwa ,

***** ****** *****
Baba Buhari ne tafe cikin wanan ranan da aka famtsama yau, rigar shi uk ta jike da zufa da alamar da k?fa yai yawo cikin wanan ranan,
Daidai zai shigo sashen nashi ne yaji muryan mama Ladi tana cewa,
Su wa yan nan yan jakar uban basu da ranan dawo wa tunda sunji dadi sun samu gidan ci da sha, mai galmi,,
Kai Allah dai ya sau,waka da wanan irin rayuwan na rashin sanin ciwon kai,
Zagi haka har kowa naji suwa kika samu haka ne wai ladi?
Wa yan nan yan jakar uban yara mana da suka tafi gulma,
Wani irin mugun bacin rai Baba Buhari yaji alokacin
Don har sai da gaban shi ya fadi gudun kada iyayyen yaran su ji,
Wani irin kunya ya lulubeshi a lokacin da ya hango matar kanin shi gufa ta lungun su tana kada kai,
Mama taci gaba da cewa wanan yaron ai wahala ta samay shi tunda ya nuna yana dashi,
Haka kawai a dinga yiwa mutum iko inga tausayi ai bai kamata atura mai su dukkan, su ba
Ke Ladi cikin wani irin daka tsawa baba ya kira sunan ta yace ahir din ki wallahi,
Naga abin naki tabin hankaline,
Shin ke ka dai keda yaron gane wai shin?
To wallahi ki iya kan ki akan wanan zancen don zan bata maki rai fiye da tsanmanin ki,
Ganin irin yadda rayuwan shi ya baci yasa mama tai shiru don tasan irin zuciyan baba yanzu zai iya mata abinda yace din,

***** ****** *****
Dukkan sune a falon inda yasa Samira da Murja suka kasa kayan gida biyar,
Baki yabasu akan kowa ta zaba daga cikin, sanin cewa sune manya gare ta,
Tana zaune gurin da take har suka gama zaben su,
Komai itace ta karshen dauka daga cikin abinda aka saya masu din,
Sai murna da farin ciki sukeyi don ganin irin wanan tsaraban mai tarin yawa da tsada da akasaya masu,
Cak tamike har zuwa bakin hannun kujeran da yake zaune akai tadan dafa,
Cikin girmamawa tace yaya mungode Allah ya kara bude ya kara rufa asiri,
Kai ya kada mata alamar bakomai, dama tasan cewa ba lailaine ya ansa mata ba,
Ganin hakane ne suma tan uwan daga gurin da suke suke tacewa yaya mungode mungode,
Sauran kayan da zasu kaiwa sauran mutanen gidana kuma nan ya shiga dan yi masu bayani sama sama,
Kiran Salawatu ne ya shigo a lokacin don haka bai karasa zamcen shi ba yadauki wayan,
Cikin murmushi a fuskan shi yake magana da ita,
Rankashi dade ka isa gida lafiya ko ?
Ya madam ya bakin ka ko ince bakin mu,
Don nima ai sun zama yan uwana yanzu,
Sai tai shiru taji yaya zaiyi re,action,
Duk lafiya suke suna gasheki sun kuma yaba da sakon ki sosai,
Kai, Sir har fa naji dadin wanan zancen da na ji


ZEEE MAKAWA YELWA,,,,
[7/5, 9:52 PM] MAKAWA: =?x?=?x?=?x?TARKO=?x?=?x?=?x?
=?x?=?x?=?x?=?x?=?x?=?x?
1? 4?
ZAINAB IDRIS MAKAWA,

ALLAH_AL-MALIK,,,,

BANZAN MANTA DA KAUNAR KU GARENI BA,,,

SAFIYA ABDULLAHI HUGUMA
MARIYA SB
HAFSAT YUSUF
NAFISAT HARZAMI,
MAMAN FARIDA
SAFENAT MAHMUD MAIDUGURI (ABUJA)
PRECIOUS HINDU KB
MAIJIDDA HARZAMI,
FATIMA YAHAYA NASAWA,
FATIMA GARBA LUV,
MAMA WALID DA WALIDA,,,
DAMA DUK WANCE BANKAI GURIN SUNAN TA BA, NAGODE MAKU KWARAI DA GASKE GA TAIMAKON DA KUKE BANI A KULLUN,,,,



Duk yadda suka so tafiya a karshen mako hakan bai samu ba don ciwon da Sadiya take fama dashi,
Dole tafiyan nasu ya dage zuwa wani lokaci don tana jin jiki,
Ga Samira fafir taki zama agurin su itama tashirya dawowa gida, gurin yan uwan ta,
Gado a,kabawa Sadiya don haka su Aisha da murja da suke manyan su,
Su ke zauna da ita a sibiti
Ganin irin yadda take wahala yasa yaran hankalin su tashi, sosai,
Suna tsaye a kanta har zuwa lokacin da abin yadan lafa mata,
Yayan su ya umurce su da su zauna da ita i je yadauko masu abin bukata a gida,
Barci Sadiyan takeyi i,yanzu don haka suma suka samu kujera su ka dan za,zauna a gefen ta,
A gida su Samira ne ke faman kokatin girka abinci kafin su dawo asibiti,
Kwatsan sai ga yayan su yashigo yanayin ba dadin gani don fuskan shi babu annuri ko kadan,
Hakan ya tayarwa yaran da hankali do sun matsu suji wani irin hali matar yayan nasu take cikine ?
Ba wani sakin fuska kamar kulkun fuskan shi a,daure, tam,
Kai tsaye yace masu ku sa min ruwan zafi a flasks, da kuma yan kayan da ake bukata a,asibiti,
Wanan dalilin yasa su gane cewa, an kwantar da ita a,asibitin ke nan,
Daga haka ya wuce, direct zuwa dakin kwanan shi,
Ido suka bishi dashi cikin jin takaicin irin halin yayan nasu,
Meenat dake daga cikin kitchen tana jin duk yadda suka yi tare da yan uwan ta,
Sai ga Samira tafado kitchen din tana cewa Meena kinji wanan matar wai gado aka bata, ashe,?
Ni wanan abin wallahi haushi yake bani,sai da mutane suka shirya zuwa gida, sanan zata wani kakalo ciwo ta narke a gado,,,
Sai ta karasa da jan guntun tsuki tana kokarin duba flask din dake gefe a jiye,
*** *** ***
Duk wani abinda ya umurce su da su hada mai don tafiya asibitin da su,
Sun hada mai a cikin wani basket da ke cikin kitchen din,
Yadda ya shiga fuska babu walwala hakan ya fito masu,
Yana kokarin sa bottom din hannun rigar shi fuskan shi a kan kayan da suka hada,
Inda Samira take zaune ya dan kalla yana cewa naga kayan da yawa mana , yaya haka, ?
Cikin dan girmamawa tace dama har da abincine muka hadawa su, Aisha,
Bai tankawa kowa ba sai kokarin da yakeyi na daukan basket din,
Samirace tace yaya dama wai muna son mu, bi ka zuwa asibitin ne,
Kamar bai ji may take fada ba ya sakai fuuu ya wuce abinshi,
Samira wace ta kai iyakan sai cewa tayi a fili, mugunta, har kan shi ya ke yi wa,,,
Nafisa wace ke zaune a cikin shirin bin yayan nasu zuwa asibitin da suka sa rai tace,
Ni tun farko ban so kisa musa ran mu ga zuwa ba wallahi don na san yaya bazai ko saurare mu ba, don dai kawai ina son ganin gari ne,
Hon din motar shi ne suke ji daga waje cikin karfi ya ke masu,
Samira wace ta san halin shi da sauri tace ashe, miskilin bai wuce ba mu yake jira a waje fa,
Meenat wace tana zaune har yanzu batai wani alamar motsawa ba yasa Samira cikin sauri tace mata taso mana Meena don kin san fa ba jiran mu zaiyi ba yana iya wucewa,
Kai ta gyada mata tare da kokarin shafa addu,a a fuskan ta sanan tace,
Anty Samira idan nace in biku wa zai zauna gida yayi muna girkin dare,
Baki Samira ta tabe gami da fisgan gyalen ta da sauri taja hannun Nafisa suka fita,
Su biyu Abubakar ya hango tun,daga nesa sun tunkaro gurin da yake,
Mamaki yayi na rashin ganin diyar Baba Samaila a tare da su,
Kamar zai masu maganar ta sai dai kuma ya share su kawai suka bude mota suka tafi,

***** ****** *****
Fitan su babu dadewa Meenat tafito tsakar falon gidan da nan tafara inda ta gyara shi tas takawo kamshi ta fesa,
Girkn dare ta dora sai kuma ta fara gyaran dakun gidan tun daga nasu har zuwa na matar gidan da na yayan su Abubakar din,
Ba, ita tasamu kanta ba sai zuwa gab da magrib a lokacin duk ta hada komai,
Kiran sallahbda akeyi a ko ina ina ya sanar da ita cewa,lokacin sallah yayi ,
Don haka babu bata lokaci Meena ta fada dakin su ta dauro alwala don tai sallah,
Falon gidan ta dawo can wani dan angul ta tsaya don,tai sallah, saboda yau gidan yai mata girma,
A gurin da take zaune ne taji sallaman shi yadawo,
Tun daga kofa Abubakar ya gane cewa gidan yasha gyara yau,
Kamshi biyu ne suka daki hanncin shi, a lokaci guda, gana air fresh ga na girki,
Ganin tana sallah yasa shi shigewa dakin shi direct,
Tsowon lokaci ya dauka da shigan shi dakin nashi,
Don ganin irin yadda dan lokaci guda dakin shi ya sauya kama, dakin ya bi da kallo ko ina tsab,
Ko bai tambaya ba yasan cewa meena ce tai wanan aikin haka,
Ita ko Meena tana zaune tana karatun Alkur,ani maigirma izu, biyu,
Jin muryan shi tayi kamar daga sama yana cewa ina, ina abincin da za,a kai asibintin, ?
Da sauri Meena ta dago daga duken da take tana karatu, don ta bashi ansa,
Voil ce a jikin shi mai ruwan madara, ya,na ta kyalli,
Mamakin wanan irin kwalliyan da ya sauya takeyi,
Don dai ita, tun zuwan su gidan shi, bata ga yana sa manyan kaya irin haka ba,
Kan ta, ta marya kasa da sauri cike da kunya da ladibi,
Sai kuma nauyin da ta dan jin don wani daure fuska da yayi da yaga irin kallon da taimai,
Don shi azaton shi yarinyar miskilace ta karshe ,
Mikewa ta yi inda kai tsaye ta wuce gurin da basket din abincin yake,
Cikin mamaki yake kallon irin yadda yar yarinya kamar meena ta iya wanan aikin haka, ?
Unlike matar shi Sadiya wace ko wankin toilet aikine a gurin ta balle daki,
Ya dauka har ya kai kofa ba tare da ya juyo ba yake cewa i hope baki sa masu plates da yawa ba don akwai na dazun a can,
Kan ta dake kasa ta girgiza alamar a,a tare da dn cewa a,a a asanyaye,
Daga haka yabar falo ya na dauke da basket din abincin,
Inda dama Meena a matse take don gani take duk a takure take dan tsayin da yayi a gaban ta,

***** ****** *****
Shiga na gani na fada, tayi cikin wasu tsaddadun material masu daukan ido,
Dinkin dogon riga ne sai shara, sharan hannun da akai, ma,su,, sai kuma saukan da rigan yi har kasa,
Ga jakar su, da takalman shigen kalar kayan, da ta sa, sai kayan su kai mata wani irin kyau, ajikin ta,
Ita da kawarta aminiyar ta watau lubuna, suke tafe don zuwa duba mara lafiyan,
Kayan fruits ne,suka tsaya a hanya suka siya don kaiwa mara lafiyan,
Basu wani sha, wuya ba sosai gurin gane dakin da Sadiyan take kwance aciki,
Saboda tambayan noban dakin da ta,ke kwance aciki,
Gaba daya yan mata suna cikin dakin sun barbaje sai kwasan girkin da kaunar su ta tsaya gida ta girko ma su,su keyi abin su da kuma shan "ya"yan fruits , wanda yayan su, ya siyo wa mara lafiya,
Tun kafin su shigo dakin kamshin turaren su ya sanarwa duk wanda ke a cikin dakin a lokacin zuwan su gurin,
Gaba daya hankalin na cikin dakin ya koma gurin masu shigowan dakin a lokacin,
Saboda kamshi da kuma sautin, takon takalman su,,
Da sallama suka shigo dakin a lokacin, Sadiya wace ke kwance tana facing din kofan dakin,
Mata ne yan gayu, su biyu da ganin su gogagun Abuja ne basai an fada maka ba,
Sun yi wankan mai sunyi wani irin fari wanda har ya fara canza masu kalar fatan jikin su,
Aisha ce tafa yi masu sannun da zuwa inda murja tafara mikewa saman kujeran da take zaune akai, ta basu,
Samira ce saman dayan kujeran, don haka ta tsaya wani dan shan kamshi kafin ta tashi sama, ta mika masu,,,
Fuskan su gurin Sadiya wace ke kwance saman gado wani kimdin da ita kanta wanda ba kitso ba kuma gyara yai wani chushewa guri guda,
Ya ya jiki ?
Inji Salawatu wace ke wani kallon mutane uku saura,
Da sauki inji Sadiya inda ta juya kan,ta don bazata jure irin kallon da suke mata ba na kurullah,
Dakin yai wani tsit a lokacin kamar ba kowa acikin shi,
Ko wacen su da abinda take, sakawa a zuciyar ta don zaman kallon kallon akeyi,
Yaya Abubakar nr ya shigo dakin a lokacin shima sai kamshi ke tashi a jikin shi,
Hannun shi dauke da ledan maganin da ganin shi kasan daga gurin sayo magani yake,
Abin mamaki sai ga yaya Abubakar yana yar murmusawa don ganin wa yan nan matan, da yayi,
Cikin mamaki sisters din nashi suke mai wani irin satan kallo,
Muryan shi sukaji yana cewa sannu ku da zuwa ashe har kun kara so, ne, ?
Da hausan su na yan Abuja suke cewa eh amma dai bamu wani dade da zuwa ba ai,
Ashe yan hutu basu samu tafiya ba ?
Eh ciwon madam ne,ya hana su tafiya wallahi,amma yan,zu ta samu sauki zuwa wanan lokacin, sosai,
Allah ya sauwaka suka ce tare da kokarin mikewa inda Lubuna take kokarin tura ledan da suka shigo dashi a gaban su,
Salawatu wace tasa hannu a cikin jakarta ta debo kudi yan dubu guda guda,,
Samira wace ke kusa da ita tsaye tun bayan mika mata kujeran da tayi ta miko ma kudin,
Karba tayi cikin rashin wani nuna zumudi kamar yadda Salawatu ke tsan manin zasu nuna kwadayin kudi


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login