Showing 273001 words to 276000 words out of 278032 words

Chapter 92 - JAMI'AR TSARO COMPLET by MRS SARAKIES.doc

23 Oct 2025

1105

doc ya k'araso Yana kallansu yace.

"ta sauka?" sukace yes sir"

yace."Ina yallab'an?.

Sukace "yanzu ya shiga
Ya Jin Jina kai Kafin yace.

"Alright kuje",suka tafi shima ya koma office d'insa.

AA Arab Yana shiga ya tadda ruky tana bacci,ya duk'a dai dai fuskarta ya kai mata sunba a goshinta kafin ya d'ago ya shafo fuskarta wacce take bacci cikin gajiya, ganin lafiyar ta lau kawai bacci take na Gajiya yasa ya saki murmushi cikin farin ciki afili ya furta.

" Alhamdulillah ya Allah!, Allah Nagode Maka bisa ga wannan kyauta da kamin daka sauki matata lafiya da ita da abinda ke cikin ta duk suna cikin k'oshin lafiya" ya zauna kan kujerar Dake gaban gadon ya zubawa yarinyar ido wacce ke mutsu mutsu tana k'ok'arin Saka hannunta a Bakinta sai a lokacin yasamu damar Ganin babyn.masha Allah haka ya furta a saman lab'b'ansa Yana kallan yarinyar da ko ba'a fad'a ba Yasan tana kama dashi tunda ga kamannin su zuhrah a fuskar ta fara ce K'al kamar 'yar larabawa, fuskarta doguwar ce ga hanci daya Mik'e ziyat ga maganai Irin na uwarta duk da shima ba baya bane wajen maganan Amma kuma wannan dai idon ruky ne da ita ga gashin kanta Wanda yake Bayki wuluk dashi Daya cika mata kanta ,kai yarinyar dai Masha Allah Dan kamar 'Yar Larabawa haka take ya kai mata Sumba a goshinta da Kuma Kuma tunta,taya Mutsa fuska zatai kuka,yay murmushi Ya dinga binta da Kallo kafin ya dauk'i waya ya k'ira ummi ya fad'a mata , ummi tayi farin ciki sosai tace gasu nan zuwa asibitin bayan ya fad'a musu wanne asibitin ne , sannan ya k'ira anty mufeeda ya fad'a mata akan ta k'ira mamah ta fad'a Musu anty Ameenah taji Dad'i sosai kamar me bayan taji wannan albishir d'in Babu Bat'a lokaci koh ta k'ira mamah ta fad'a Maka mamah tace zata turo baba hasiya tazo ta .bayan ya gama wayar ya juya yaga yadda Ruky ta k'ura masa ido tana kallansa Ashe ta farka tun lokacin Daya fara wayar take ya sakar mata murmushi Yana mik'ewa tsaye ya ajiye babyn a D'aya kan gadon Dake kusa Da Wanda ruky take kai ya k'arasa kusa da gadon da Ruky take ya danna Wani D'an Abu take gadon yad'an d'aga dai dai yadda Ruky zataji dad'in kishin gid'a a jikin gadon,ya d'auki babyn ya dawo kusa da ita ya zauna Yana kallan ta yace.

"Sannu Noor!kin tashi".ya fad'a da tausayawa.

Ta gyad'a masa kai, yace.

"Akwai inda yake miki ciwo yanzu?".

Tace cikin sanyin murya
" a'a Babu ko Ina".

AA Arab ya Mik'a mata babyn yace.

"Noor Sunan da yake K'iran ta dashi kenan yanzu,Kinga kyautar da Allah yay mana koh?,ya cigaba yace."thank you very hugely Noor,kinsani farin ciki Marar misaltuwa,Allah yay miki albarka ya raya mana abinda muka haifa".ya fad'a Yana rungumota jikinsa, ruky tai murmushi tana zubawa babyn ido sai yanzu ta k'are mata kallo Masha Allah kawai ta Ambata a Zuciyarta AA ya kalleta yace .

"Kinga babyn mu me kyau ko?"ya fad'a Yana murmushi.ruky ta gyad'a masa kai kafin tace cikin yanayin muryarta.

"Kuma shine ta iyo kamar kaba nida Nasha wahalar Bata iyo kama taba sai kai?". ta fad'a cikin shagwab'a.

Yay murmushi yace."jealous".tace babu Wani jealous ai gaskiya na fad'a yace.

" Ai kuman Irin idonkine da ita ko Baki ganiba?".,ta harareshi yay murmushi yace.

"Oh! Baki yarda daba kenan".ta tura Baki gaba tace.

" Amma ai ta kwashe komai naka"ta fad'a cikin shagwab'a.ya lakuci hancinta kafin ya kalli babyn Dake mutsu mutsu yace.

"Kinga fa shan hannu take ki Bata Tasha?". ruky ta harareshi tace.

"Gaskiya kunya nakeji".

Yace."common please ki Bata mana Kinga fa kartai kuka". ya fad'a Yana k'ok'arin kawo hannu k'irjinta.

Ruky tai saurin ture Hannunsa tana tura Baki gaba tace.

"sai anjima gaskiya"zaiyi magana wayarsa tai ringing Yana dubawa yaga ummi ce ya Kalli Ruky yace .

"ummi ce Inaga sunzo".

Ruky tace.


"ok! to kaje ka taho Dasu mana"
Yace.

" idan sukazo baza su barni na sake ba let me kiss you before I leave", Bai jira cewar taba ya had'e bakinsa da nata for almost a minute sannan ya saketa Yana murmushi tare da cewa Allah yay miki albarka.ruky tai murmushi tana kallan sa tace .


"Ameen thumma Ameen Deee!".yace.

" bari naje na taho Dasu" daga haka yay gaba ruky ta bishi da kallo kafin tai murmushi ta ajiye babyn a gefenta ta kwanta itama Dan baza taso ace sunzo sun sameta da babyn a hannun taba....


Haka aka sallame ruky wajen k'arfe goma na safe tunda daga ita har babyn suna cikin k'oshin lafiya,da suka koma gida bayan su ummi sun K'ara mata barka suka koma gida aka bar Ameerah zatana Yi mata wasu abubuwan sai baba hasiya da zatana kula da ita.mamah ta k'ira ta tai mata barka da dasu ya Tahir harda matarsa anty mufeeda kan ai tak'irata yafi a k'irga,a ranar itama Hanan tazo da D'anta irfan Mai kama da ubansa sak ,ya hanaf d'in NEMA ya kawo su yay wa AA Arab barka Wanda bakinsa ya kasa rufuwa saboda farin ciki.hakanan Hanan ta wunar mata sai dare ta tafi, washe gari aka Dunga zuwa barka har ya kasance saura kwana biyu suna,inda anty mufeeda tazo ita da 'ya'yanta,AA Arab yayiwa Mai jego da 'yarta kayayyakin suna kamar me Dan tun kafin ai haihuwar yay tai musu siyayya Yanzu ko da yasan mace aka haifa masa Baki ga uban kayan Daya dinga lodo musu ba kamar za'a Bude Wani k'aramin boutiques,ya Siyo hakikar suna sa guda d'aya sai raguna guda biyu Tirk'a Tirk'a Daya siyo za'a yanKa na suna hidima babu kalar wacce Bai yiba musu ba ,ana gobe suna matar governor her Excellency ta Aikowa da ruky kaya kusan cikin mota tace na bar kar tane ,duk da tazo Kwana biyu da akai haihuwar taiwa ruky barka.governor shima ba'a barshi a Baya ba shima yayi musu Shatara na arzik'i haka sukai ta godiya mutane sukai ta mamaki....


Ranar suna kuwa ya Allah! wato Hajiya zo kiga Taron Rad'in suna da akayi manya manyan Bak'i akayi a wannan Rad'in suna,yarinya taci sunan ummi Fatima za'a na K'iran ta da Rauda ,can na hango angon K'arni wato AA Arab Yana ta baza Babbar riga yasha kyau harya gaji,Mai jefo kuwa sai shiga take tana fita cikin tsadaddun suturu kala kala,anci ansha Dan abincinma caterer's aka d'auko sukai aikin babu Irin abincin da ba aiba Kuma serve your self,duk Wanda kikeso shi zaki d'iba Mai jego tayi kyau harta gaji su anty mufeeda Hanan da matar ya Tahir khadija suma sunsha sutura sai kai da kawowa suke Yi ,su ukhty ma duk sunzo sunan ga baba lami da shafa suma sunzo Kuma sun kawowa baby abun arzik'i daidai k'arfinta ga shafa itama an fara zama 'yanmata jikinta yayi kyau sosai har baba lami itama gabad'aya suun sauya sun zama abin kallo,gida dai yayi people Masha Allah,ga Mai jego da babyn ta Babu Wanda Bai Basu gift na tundaga kan Abba ummi,su ukhty,agidansu ruky ma kowa ya Basu gifts JAMI'AR TSARO fans suma sun kawo gifts d'insu na musamman sunci sunsha sun godewa Allah a sunan Rauda.kai yarinya dai tayi goshi saidai muce Allah ya raya.haka akai Taron suna aka watse,haka ruky da AA Arab suka cigaba da Kuka da babynsu wacce suke bala'in sonta da ji da ita baya ma AA Arab idan ba wajen aiki ba kullum zakiga Rauda tana hannunsa Yana mata wasa da haka har sukai arba'in ahaka AA Arab ya samu k'ira daga Abuja akan za'a k'addamar dashi akan muk'amin da aka bashi Ma'ana za'a Yi bikin rantsar dashi nanfa su ruky suka fara shiri dama Bata fara fita aiki ba gashi Kuma dole a Abuja zasu zauna Amma saisun fara zuwa anyi bikin sannan zasu dawo shima AA Arab yaje ya kai takaddarsa headquarter sannan yayiwa Ruky transfer zuwa Abuja kusa dashi.

Bayan kwana biyu suka shirya Wanda washe gari za'a yi Taron, jirginsu ya sauka a birnin Tarayya Abuja,wannan karon gida aka bawa AA Arab Wanda zai sauka da iyalansa k'aton gida kamar me ,murna wajen anty mufeeda kamar me ganin itama yanzu ta samu 'yar'uwa a kusa da ita , washe gari jirginsu su Hanan ya sauka a Abuja Dan Suma sunzo tayasu murna tunda biki za'ayi ,mamah Bata zoba tace sai daga baya zatazo ta tayasu murna Amma ta turo musu baba hasiya, Abba da ummi dasu zuhrah duk sunzo Suma Amma su agidan Abba Dake Abuja suka sauka,dayake Taron k'arfe goma da Rabi ne na safe tuni wurin ya cika mak'il da da dandazon manya manyan mutane,ga tsaro da aka zuba a wajen ba'a magana yo shugaban k'asa zaizo ai dole,su Hanan har sunzo sun samu wuri sun zauna Wanda aka ware musu na musamman can na hango wata Prado tai parking gaban Wani waje na musamman Wanda yasha decorations na hango Wani police yay saurin Bud'e motar tare da k'amewa a inda yake tsayen Yana Kuma Sara wa AA Arab Wanda naga ya fito daga cikin motar cikin shigar sa ta uniform as police sak ya tsaya Yana duba wayarsa,aka Bud'e D'aya site d'in ruky ta fito itama tayi bala'in kyau harta gaji tana rungume da 'yarta a kafad'arta wacce take cikin shigar doguwar rigar 'yan kanti Wanda idan kikaji kud'insu saikinyi mamaki saboda tsadar su, Rauda ta Saka Hannunta a cikin bakinta tana tsotsa,ga kanta ammata parking d'in dogon gashin ta Irin 3 babyn nan yarinya kamar 'Yar Larabawa Dan kowa agunnan kallo saiya koma kansu idan kiga yarinyar kamar ki d'auketa ki gudu saboda kyau,haka ta wuce wajensu Hanan dasu anty mufeeda shikuma AA Arab ya wuce wurin zamansu,babu dad'ewa president yazo aka Mik'e tsaye cikin girmamawa ana masa Barka da zuwa aka rakoshi har wurin zamansa Kafin afara National anthem ,bayan angama president yay jawabi Sosai tareda da manya manyan mutane masu muk'ami suma Sukai, president ya Mik'e tsaye aka Mika masa Wani Abu ,AA Arab ya k'arasa gunsa ya sarawa president kafin suyi musabaha , president ya d'aurawa AA Arab Wani k'arfe me kamar star da Kuma wasu igiyoyi aka fad'arsa,aka k'ira ruky ta mak'ala masa wata ster d'in bayan ta gama ta Sara masa take yay murmushi Shima ya Sara mata ya Mik'a mata hannu saukai musubaha Nan fa aka dinga d'aukar hotunansu da iho da tafi ,ta koma ta Zauna kafin Kuma rantsar dashi sukai picture da president kafin wasu manya manyan mutane sannan sai 'yan uwansa yayi da kowa harsu anty mufeeda sai Kuma sukai da Rukayya Wadda Rauda ke hannun ta sannu ya karb'i Rauda akai musu tana d'auke a hannun sa sai Kuma ya Mik'awa zuhrah Rauda ya rungumi ruky ajikinsa akai musu su biyu zo kiga kallo ya Allah sunyi bala'in kyau kamar me,daga k'arshe nanma ta rataya masa rough d'in flowers ya Sara mata kafin ya kamo hannunta ya sumbata ya furta I love you.haka dai aka gama taro aka watse,da suka koma masauki nanma da daddare anhad'a wata k'warya k'waryar party Wanda iya su yasu 'Yan uwa aka Yi ,haka aka gama taro ,washe gari Kuma jirgin su ya d'ago zuwa Kaduna,bayan Kwanaki hud'u ya gama duk Wani processing harda transfer fa d'in Ruky dayake ba yanzu zai koma Bakin Aiki ba sai nan da sati uku Hakan yasa ya yanke shawarar zasu tafi saudiya suyi umar ta one week su Mik'a godiyar su ga Allah Daga can kuma su wuce Maldives suyi two weeks acan , Aiko haka akayi Saida suka gama komai sukai sallama da iyayen su da kowa da kowa Dan Babu abinda suka d'auka daga su sai kayan jikinsu tunda akwai komai na buk'atar ruyuwa acan gidan nasu na Abuja Dan babu Abinda AA Arab Bai sa musu ba kwanan su biyu a Abuja Jirginsu ya D'aga zuwa a Saudiya shima satin su D'aya acan suka tafi Maldives inda suka D'an huta acan tareda more rayuwar su da soyayyar Kamar me tareda baby Rauda sun yawata guri duk Wani wurin da masoya suke zuwa babu inda basu jeba sunyi wata Irin soyayya Mai tsayawa Arai ya Allah! Dan mutanan nan jinsu suke tamkar su kad'ai ne a cikin duniyar masoya haka suke jin kansu ga baby Rauda yadda suke Bata kuluwa ta musamman da nuna mata soyayya da k'auna haka suka gama sati biyunsu suka dawo gida Nigeria.


__________?&


Acan Zaria kuwa Nana ta gama school of nursing tana aiki anan asibitin koyarwarwa na ABU ZARI'A inda anan aka d'auke ta aiki dama da offer su suke fitowa salisu dai ya dawo wa Nana akan Yana Santa da kamar baza ta Bashi had'in kaiba sai Kuma ta bashi ganin yadda yake yawan zarya agidansu kullum Yana yawan zuwa ahaka har suka dai dai ta ya turo magabatansa nan Bada dad'ewa ba za'a Yi biki .yanzu ummah Bata da fargabar komai Dan duk Wani buri da take dashi akan 'ya'yan ta Allah ya cika matashi Dan babu Abinda ta NEMA ta rasa na b'angaren Jin Dad'in rayuwa ,Dan kud'i dai Bata rasawa ke komai dai da kika sani na Jin Dad'in rayuwa ummah tana dashi 'ya'yan ta suna mata ga sirikinta mutumin kirki Babu abinda baya musu kayan abinci kud'i kayan sawa babu abinda Bai d'auke musu sai yanzu malam Auwalu yagane me ummah take nufi Dan shima kansa ya sauya Dan lokacin D'aya canji dai yazo musu..


Ameenah ta haihu ta haifi d'anta namiji kyakkyawa dashi baba asabe dayaji Saida ta girgiza ta k'ara Jin tsoron Allah ya K'ara mamaye mata zuciya nam tasa aka k'ira mata ummah da Malam Auwalu akan zata fad'a musu duk Irin abinda ta aikata musu.


Malam Auwalu yace.

"Muna jinki".

Baba asabe ta share hawayen dayak'i tsaya mata tana kallan ummah tace da bakinta Wanda yake akarkace tace .

" Dan Allah maimuna ki yafemin duk abinda zan fad'a muku, tabbas ada na zalinceku Nima na zalinci kaina duk abinda zan fad'a muku karku tuna Irin Abinda na aikatawa muku ku yafemin dan Allah ta fad'a tana zubar da hawayen nadama,nan ta shiga Basu labarin duk irin abinda ta aikata daga kan asirin datai har aka fasa auran Ameenah da barrister Babu har aurawa Ameenah Kabiru da akayi nan mamaki ya gama kashe ummah da malam Auwalu daga k'arshe Baba asabe tace.

"Ni dama nasan duk alhakin kune yasa nake ta ganin masifa kala kala akaina da Kuma ya'yana Dan Allah ku yafemin" ta fad'a tana rushewa da gunjin kuka.ummah tana kuka tace .

"Ni kan na yafe miki asabe Dan wannana iznace Allah ya yafe mana Baki D'aya"shiko Malam Auwalu tashi ma Yay bar falon yanajin zuciyar sa Kamar zata fashe saboda Bak'in ciki Yana Mai yin nadamar auranta da yay Dan baba asabe ba k'aramin cutar dashi tai ba ta Kuma cuci 'ya'yansa shiko Taya ma zai yafe mata ,su Mardiya duk sunaji Dan suna k'ofar falon daga waje suka shigo suman sukace cikin Kuka yanzu dama duk wannan halin da muke ciki ke kika jefamu sannan Kuma da aka sakomu kika dinga hantararmu Ashe kece kika aikata wa baba maimuna da 'ya'yanta wannan zalincin gashi zaliha itama tai cikin shege harta haihu to ai gashi Wanda kika cuta d'in sune agaban ki ba kowa ba kinaji kina kallo ai wallahi kad'an ma kika gani Kuma sai Allah ya Saka mana nan sukai mata tas har sai da ummah ta hanasu sannan sukai shiru suka fice daga d'akin suna nadamar kasancewar baba asabe uwa garesu haka zaliha itama kukan tai tayi kamar ranta zai fita tana nadamar biyewa baba asabe da tai ...


Bayan sati biyu mijin lawisa yazo ya Basu hak'uri ya Maida lawisa d'akin ta itako mardiya saidai ta sake Wani auran,ita da zaliha idan ta yaye suwaiba.baba asabe tana nan kwance Babu abinda take iya yiwa kanta komai sai dai amata bakinta ya karkace Yana dalalar da yawu kullum tana Cikin Kuka kamar me tana ta addu'ar Allah ya yafe mata zunubanta...



*Abuja Nigeria*


Su ruky dai sundawo daga Maldives,a kaduna suka sauka bayan sun huta suka je gidansu bayan sun huta kuma suka je har gida suka gaida iyayensu alokacin ne aka kawo kud'in auran su Ameerah nan da two months biki da ita da ita zuhrah a saudiya za'a bada ita Wani D'an uwansu Abba ne ita Kuma Ameerah anan Kaduna zata zauna Dan gidan Wani D'an majalisa zata aura kwanan su biyu suka koma Abuja Dan AA Arab zai fara fita aiki haka itama ruky wanda ita nan federal headquarters zata cigaba da aikinta ,sun fara zuwa wajen aiki cikin kwanciyar hankali na nutsuwa gefe D'aya Kuma suna soyayyarsu Mai ratsa zuciya suna tattalin junansu da nuna kulawa kamar me ga yadda suke bala'in son baby Rauda da ji da ita kamar me yarinya kullum kyanta K'ara fitowa yake tayi kyau tayi b'ulb'ul abinda kamae ki sace ta ki gudu haka take Dan kyau duk Wanda ya kalleta saiya tanka saboda Wani Irin sassanyen kyaune kawai yarinyar take Dashi adole Ruky ta tafi da jikar baba hasiya Mai suna adama wacce zata dinga kula mata da Rauda.....



*Bayan wata biyu*


Lokacin bikin su Ameerah,anyi biki ankai Amare gidanjesu an watse sai dai muyi fatan zaman lafiya.matar ya Tahir ta haihu ta haifi mace ansa mata sunan mamah Halima ana ce mata Diyam


*Bayan shekaru uku*


Lokacin komai ya sauya daga yadda muka sani a Baya dan kuwa harda girman Rauda Dan lokacin tana shekara Uku da wata Tara a duniya,ga ciki ajikin ruky tsoho haihuwa ko yau ko gobe,Hanan itama ta K'ara haihuwa ta haifi mace itama sunan mama aka Saka mata Halima,sai anty mufeeda itama ta K'ara haihuwa ta haifo twins duka Maza abun dai abun ban sha'awa, cikin dare Nak'uda ta tasowa Ruky babu Bat'a lokaci AA Arab ya fito zai d'auki mota ya kaita asibiti police din Dake kula da gidan suka Hanashi sunce ai baza su bari yaja mota ba tunda ai yanzu yafi k'arfin haka,babu yadda ya iya ya kinkimo ruky aka Bud'e masa motar yashiga back seat Yana rumgume da ita suka wuce asibitin da comboi na police.


Rauda ta tashi bayan tafiyar su tana Neman mummy da Dady nan adama ta


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login