Showing 192001 words to 195000 words out of 278032 words

Chapter 65 - JAMI'AR TSARO COMPLET by MRS SARAKIES.doc

23 Oct 2025

1062

WRITER'S ASSOCIATION ('*



*TEAM 4 THE GOLDEN STAR (' WRITER'S*



*Bismillahirrahmanirrahim*



_____season two ep 7?? 7??



____________?&


*ZARI'A*


Yau satin Ameenah D'aya da dawowa gida , Amma abun mamaki har yau Baba asabe uwar 'yan San jin gulma da shiga abinda ba'a sa da itaba, Bata tab'a bud'ar bakinta tambayi "meyasa Ameenah ta dawo gida ba, ko Kuma ta tambaya taji dalilin dawowar Ameenah gidan , Amma a yadda ta fahimta kamar Kabiru ya saki Ameenah duba da yadda ummah take cikin nishadi da walwala tunda Ameenah ta dawo gidan, ,Amma Batai magana ba,ta zuba ido kawai tana kallan su ,Wanda zata tambaya ma Malam Auwalu ne to Kuma yanxu haushinsa takeji tunda ya banzatar da zancen da taje masa dashi na sakin da ta ce masa anyiwa lawisa bataga ya Wani damu ba ,tun daga nan take Jin haushinsa,Dan ko magana Ba ta masa,ga babban ta kai cinta a yanxu shine adda taga Ameenah agida Kabiru baixo ba,baxa ta tab'a yadda ace wai Ameenah ta bar Hannun Kabiru ba a yanxu,baxa taso ace yanxu komai yaxo karshe ba, zataso ace bakin cikin auran Ameenah da Kabiru da ummah take zataso ace shine ajalin ta,Amma tasan yadda xatai bari dai tasan mai yasa Ameenahn ta dawo gidan.ita yanxu abinda yake damun Tama ya isheta,na sakin da akayi wa 'ya'yan ta,ga basu da Wani extra d'aki da zasu zauna aciki ga ko Wacce ta kama ta d'ebo 'ya'yan ta tazo dasu ,daga falor dai sai uwar d'akin ta, ita da zaliha suke kwana acikin d'akin, mardiya Kuma da lawisa su ???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?kwanta a falor suda 'ya'yan su,gabadaya ba'a sake take ba sbd yadda 'ya'yan su mardiya suke Hana ta bacci da Kukansu na cikin dare Kamar me, Dan D'an gidan mardiya karamin nan bala'in kuka ne dashi kamar hauka ga Dan iskanci baya tashi kukan sa sai tsakar dare lokacin suna cikin bacci idan ya dinga kuka kamar zai kashe musu dodon kunne haka Baba asabe take ji,ga bala'in ci acikinsu kamar gara ,abincin siyarwar ma idan tayi su suke cinyewa suda 'ya'yansu gashi yanxu malam Auwalu ya Raba musu kayan abinci na wata D'aya idan kika cinye kafin wata D'aya to baxai tab'a Baki ba sai Watan ya cika,Dan mugunta,Kuma tasan badan kowa Yay ba saidan ita da 'ya'yanta ,gashi ko ganin su mardiya da yay sun dawo gida ayya Kara masu abincin kan yadda yake Basu a da ,Amma shine Bai qara musu ba yadda yake Basu anbinci daga ita sai zaliha,haka yanxu ma ya cigaba da Basu, Da tai magana sai ya ce "aiba shi ya ce "suk'i zaman aure ba ko Kuma ya ce a saki su mardiya ba,gashi abincin harya k'are ko Rabin wata baiyi musu ba 'ya'yan su mardiya sun cinye sbd bala'in cin su ,yanxu kuma sun koma kan abincin siyarwar ta dole sai shi suke ci......



Zaliha kan liyafa taci gaba Dan sai Wani qara kyau take kamar me,ga ko Ina na jikinta sun qara cikowa Masha Allah, baba asabe har yau Bata tab'a kawo komai akanta ba, illah cikar budurci ne kawai zaliha takeyi, yanxuma tana bakin murhu duk tayi butu butu da ita ,su lawisa da mardiya suna can a falor suna xaune suna hira kamar Babu abinda yake damunsu ,saidai ta girka ta Basu suci Amma babu Mai fitowa ya Taya ta girki bare Kuma aikin gidan,ta k'walawa zaliha kira, zaliha ta fito cikin kwalliya, ta ce "Gani babarmu yanxu nake shirin fitowa,kin gama ne? Ta fad'a tana kallan baba asabe.baba asabe ta ce "eh nagama ki fito lokaci sai k'urewa yakeyi" zaliha tana gyara zaman mayafinta ta ce "nagama ai babarmu,Ali ko ya xo" kafin ta rufe Baki Ali me napep ya shigo zai fara d'iban kulolin abincin Yana fita dasu daga gidan ,saiga mardiya ta fito daga d'akin baba asabe da roba a hannun ta ,ga d'anta tasi'u a hannun ta sun fito gadan gadan kawai wajen kular abincin ta nufa zata dibar ma tasi'u ta kalli Ali Dake k'ok'arin daukar kukar jollof din shinkafa ta ce"tsaya karka d'auka bari na d'ibar wa tasi'u tun jiya ya dameni da kuka Ni na San yunwa yakeji" ta fad'a tana k'ok'arin Bud'e kular abincin, baba asabe ta Daka mata tsawa ta taso afusace ta rik'e kular tana kallan mardiya wacce ke kallanta da mamaki ta ce " karki kuskura ki d'ibar min abinci na fad'a miki? Mardiya ta tsuke fuska ta ce "haba Babar mu,kina fa Ganin tun d'azu tasi'u yake min kuka Kona ce tun jiya cikin dare Kuma wlh nasan yunwa yakeji abincin safe ma wlh ba Wani koshi yay ba, sbd koni kaina wlh banci ya kai loma biyu ba" Baba asabe ta Maka mata wata muguwar harara ta ce "Ina ruwana da yaci da karyaci ,ki siya masa mana ko Kuma ki Maida shi gidan ubansa mana idan ke Baza ki iya ciyar dashi ba,ko hakk'i nane na ciyar dashi? mardiya ta saki Baki tana kallan baba asabe da mamaki Jin abinda ta fad'a,wai tasiya masa abincin ta ce "yanxu babarmu abincin ma saina siya masa bayan gashi nan kin girka har za'a fita a siyar dashi to meye anfanin Sana'ar da kike idan baxa ki ciyar damu ba mu 'ya'yan ki " baba asabe tai mata Wani kallo kafin ta ce"ke har kina da bakin magan ma, da ace kina tausayina ne saina Baki ko Dan wannan ma, Amma Dan Bakuda mutunci keda lawisa Kuna kallo na xan fito na D'ora girkin abincin nan tun sassafe Kuna can Kuna zaune Babu Mai fitowa ya tayani,idan Kuma girkawa nai Kun iya kufito kuce zaku d'iba ko Kuma ku dibar wa 'ya'yan ku sbd Baki da kunya ki matsa ki bani wuri tun kafin na Wanka miki Mari"......



Mardiya ta turo Baki gaba ta ce "yanzu babarmu ni kike fad'awa haka akan xaki bamu abincin? Baba asabe ta ce "an fad'a mikin,idan ubankine ya bani jarin basai ki k'wata na gani ba, iya abincin da ubanku ya bani na Baku ya kare, wannan Danake siyarwa nake rufawa kaina asiri shi zan dinga d'auka ina Baku _kuda 'ya'yan ku kenan koh?idan Kinga baxa ki iya ba ki Maida su mana gidan ubansu mana ko dole akace sai kin zauna tare dasu, Koda su aka kaiki gidan uban nasu da zaki debo 'ya'ya ki taho Dasu" mardiya hawaye ya xubo mata ta dubi d'anta Dake tsala Mata kuka ta Daka masa tsawa ta ce "kamin shiru tasi'u" ai kamar zuga shi tai ya Kara wangale Baki Yana kuka , lawisa da ta fito daga d'akin tun dazu tana kallan su tana Jin duka conversation dinsu ta dubi baba asabe ta ce "Haba babarmu Dan Allah ki bawa 'ya'yan nan abincin wlh yunwa yakeji , bama iya tasi'u ba harda sauran ma" baba asabe ta ce "tafi ki bani wari tun kafin kema nai miki abinda bakiyi zato ba,da zaki fito kice na bashi abincin tunda na fito ina girkin Nan akwai Wanda ya yaxo acikin ku ya ce xai tayani , Kuma shine Dan Bakuda kunya kema xaki fito kice na bashi abincin,to idan Kin Isa ki kwatar masa, Kuma idan har saina bawa 'ya'yan ku abinci ne,to kuwa wlh 'ya'yan naku sai dai yunwar ta kashe su Amma babu D'an da zanbawa abincina idan Kuna da kud'i Kuma kisiya musu"lawisa ta ce "yanzu babarmu abincin gashi muna kallo xaki bayar asiyar Amma kice sai mun siya? baba asabe ta Kalli Ali ta ce " Ali d'auki kular nan ka fita da ita "Babu musu Ali ya dauki kular ya fita da ita waje ,mardiya taja tsaki ta kama hannun d'anta suka koma dak'i, itama lawisa tab'e Baki tai ta bi bayan mardiya ta shige falon tana Allah ya sawake .Mai napep har ya gama kwashe kulolin abincin , zaliha ta tab'e Baki itama tana kallon baba asabe ta ce "Babar mu na tafi" Baba asabe ta ce "sai kin dawo"daga zaliha ta tafi , baba asabe tai kwafa itama ta fara kwashe sauran abincin data ajiye zata ci.......



Duk wannan abin da suke ummah da Ameenah Dake xaune cikin falonsu suna jinsu ,Nana Bata nan ta samu admission a school of nursing Dake cikin garin ZARI'A,ta fara xuwa tun ranar Monday, Ameenah tana zaune tana karatun Al_Qur'ani ta kalli ummah ta ce "Waini ummah su Mardiya kuwa xuwa sukai ganin gida ko Yaya? Ummah ta tab'e Baki ta ce "yadda kika gansu Nima haka na gansu bansan meya kawo suba"Ameenah tai shiru batace komai ba ta cigaba da karatun ta, lokacin sallan Azhar yay ta tashi ta shiga toilet Dan dauro alwala tai sallah , ummah itama mikewa tai tana jiran Ameenah ta gama itama tayi......



Ai yanxu zaliha sai ma abinda ya K'aru tsakanin ta Alhaji tanko,Dan yanxu idan taje Tasha juye ma yake mata sbd ya riga da ya Bud'e mata ido, Alhaji tanko kullum saiya je yayi mata juyan abincin ya ce "ta xubawa Kowa yadda zai koshi, mutanen tashar nan kuwa suyi ta Mai ihu suna ce masa saiya fi haka,ya ce "Kuma Kona nawa ne ta fad'a masa zai biya,idan zaliha ta fad'a masa kud'in kuwa take awajen yake biyan kud'in nan gabadaya, sannan ya d'auketa ya kaita wani gida su sheke ayarsu acan, da daddare ma ya koma ya qara kwasar wata Gani mar, Baba asabe Dad'i take ji saidai kawai taga kud'inta wani lokacin ma harda qari Amma Bata taba tambayar zaliha Ina take samun kud'in ba sbd San kud'i ya gama mamaye mata zuciya,itadai ummah ta fara tunanin Wani Abu aranta Amma Bata furtawa kowa ba tana dai addu'ar Allah ya Ganar da baba asabe tun kafin ranar ladama tayi......


___________?&


Yau gabadaya ruky agajiye take tunda ta shigo tun safe office din nan take ta aiki kamar Babu gobe,Kuma ahakan ma bawai gamawa tai ba ganin lokacin sallahn Azhar yayi yasa ta ajiye aikin Dan ta huta kafin taci gaba.AA Arab ne ya shigo office din bayan ya dawo daga masallaci,tana ganin sa ta juyar da fuskar ta gefe sau d'aya ya kalleta ya shige office dinsa,Babu jimawa ya fito da wasu File ya dire mata agabanta , ruky ta juyo Jin an ajiye mata abu kan table ta Wani kalleshi sannan ta kalli file din , AA Arab ya Wani hade Rai ya ce " gashi wannan file d'in kishi garmin dasu cikin laptop din ki,saiki tura min ta email Dina,ruky kamar ta saki Kuka haka taji "cikin sanyin murya da gajiyawa da wannan Saka ta aikin da yake ta ce "wlh Nima inada da wasu aikin gashi banma gama ba" AA Arab ya ce "shiyasa dana shigo na ganki kina aikin koh? Ya fada rainin hankali,Ruky ta ce "wlh da GSK nake hutawa nake shiyasa,Dan Allah kayi hakuri "AA Arab ya ce "sorry for ur self, Amma saikinyi aikinnan koda ko sai kin gama naki aikin ne" ruky ta qara Marai raicewa ta ce "Dan Allah kayi hakuri" AA Arab ya ce"kima daina bani hakuri Dan sai kinyi" rukya ta ce "Dan Allah meyasa kake son kaga ka takuramin ne,badama kaga Ina hutawa dole sai ka k'irk'i romin da Wani aiki kace nai Maka?" AA Arab ya ce "ai tunda harni kike gulma da cewa baza ki qara abinda nake saki ba, nikuma nake so na nuna miki nine gaba Dake,Kuma dole kiyi ,yanxun ma gashi nan idan Kinga dama karkiyi kamar yadda kika fad'a".....



Ruky ta shagwab'e fuska ta fara matsar kwalla ta ce "wlh nidai sai Allah ya Saka min ya xa'ayi kaita axabtar Dani kana ta sani aiki kawai Dan na Fad'i GSKY"AA Arab ya saki Baki Yana kallanta cikin mamakin xancen ta,ya ce "wato bakinki baxai mutu ba koh?Kuma nine mugun koh? Wato yanxun ma Dan raini kika qara fada ko? Ruky ta juyar da kanta gefe, tana kuka qasa qasa,ya ce on a serious note "dan Allah karkiyi kiga abinda xan miki , daga haka ya wuce office dinsa, ruky kifa kanta tai da table din gabanta ta fashe da Kukan tausayin kanta, ta fi 20 minutes tana wannan kukan taji wayarta na ringing tajawo ta duba taga number ne,kamar bazatai picking ba harta katse aka qara K'ira ,Saida ta kusan tsinkewa sannan tai picking takai kunne,tai shiru tana sauraran me kiran, wata murya ce taji anyi mata sallama da ita ,ta ansa da shakakkiyar murya,daga D'aya bangaren ya ce "barkan ki da wannan lokacin zinariya ta"ruky tai sakare tana jinsa ,tana mamakin waye kuma wannan ta qara duba wayar taga dai number ce, Kuma Batasan me number ba,ta Maida kunne ta ce" please who is on the line" ya qara lumshe idonsa Yana Jin yadda muryar ta ke qara rura masa wutar sonta axuciyarsa.....



Ganin anyi shiru yasa ta ce a fusace "I'll hang the called idan baxa ayi magana ba" yay saurin cewa am sorry my heart beat,but am begging u ko kinji waye Dan Allah karki kashe min waya "ruky ta ce "ban Maka wannan ALKawarin ba I said who are u "yay murmushi ya ce "Ameer by name ,ruky tace i didn't know u" yay murmushi ya ce "Wanda kuka je gidanmu ranar keda k'awarki Hanan"take ruky ta gano shi ,batai mamakin Ina ya samu contact din taba domin tasan hanan ce tai mata wannan aikin ,ya ce "nasan zakiyi mamakin Kiran ki danai koh? Ruky tai shiru ya cigaba ya ce "wlh na kasa jure wane tun ranar Dana fara ganin ki naji gabadaya na rasa nutsuwata, please Rukayya Dan Allah ki bani dama wlh I felt in love with you please ki tai makamin" ruky had'e Rai kamar Yana gabanta ta ce "Dan Allah malam kayi hkr ni inada mijin AURE" ya ce banyarda ba da kyawarki xata fad'a min, Dan Allah kiyi hkr ki bani dama koya take" ruky ta ce "please Nima kayi hakuri sai anjima" daga haka ta kashe wayar, Tana Jin yau saitayiwa Hanan wulakanci wato data ce kar ta bashi contact din ta Saida ta bashi koh,tai k'wafa" AA Arab da ya fito Dan xuwa masallaci Dan tana cikin wayar ya fito xai tafi masallaci yaji Wani Abu cikin wayar da takeyi Amma ba duka ba ya kalli file din Daya ajiye mata ,yaga ko tab'awa batai ba,Yana gyara hannun rigarsa farar top din yace" wato bakiyi abinda na sakaki ba koh?kika kama soyayya koh, soyayyar ma a office d'ina Dan kin Raina ni koh?......


Ruky ta kalleshi ta ce "ni ba soyayya nake ba ,idan Kuma haka kaji to",AA Arab ya ce"kici gaba da abinda kike tunda ke bakida kunya Ina fad'ar magana kina Maida min zanje masallaci na dawo Dan Allah in dawo In tarar Baki fara min aikina ba,kiga yadda xanyi Dake,ya ce "silly gurl" daga haka yay hanyar kofar fita,ruky ta bishi da Harara tana K'un K'uni qasa qasa......





07066508376________
'?Follow the Mrs Sarakies=؋? =?1? HAUSA Novel Channel channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VbBRj1D35fLuSHibdq1Y







*___JAMI'AR TSARO ___*



*___THE WOMEN POLICE ___*



*NA*



*____NAJA'ATU UMAR FAROOQ ____*



*___(MRS SARAKIES =؋?)=?1?___*




*('TAURARI WRITER'S ASSOCIATION ('*



*TEAM THE 4 GOLDEN STAR (' WRITER'S*



*Bismillahirrahmanirrahim*



____season two ep 7?? 8??



___________?&


Kwance tashi babu wuya awurin Allah,hardai yau ya kasance saura kwana biyu a koma shari'ar su Alhaji sunusi da babajo Ali,suna can a prison idan kuka Kallesu sai sun Baku tausayi sbd yadda suka fita a hayyacinsu gabadaya, ko a gidan prison d'in ma sun Had'u da Wanda suka tab'a xalinta shekaru kusan uku kenen ,Kuma ga ya fisu Rashin mutunci,Dan tsabar taqadirancinsa acikin prison din ma shine sarkin gidan, tun da yaga ankawo su Alhaji sunusi gidan ya Bud'e musu wuta ya ke zalintar su da zaginsu da hanta rar su,Kuma ba komai ne ya jawo hakan ba,sai asanadin siyasar su Alhaji sunusi aka kawo shi gidan prison d'in nan,gashi har yau yana shekara ta uku acikin prison d'in Amma Bai fitaba Babu Kuma Wanda yaxo yay belin dinsa acikin su,ya d'auka ma tunda asanadin siyasar su Alhaji sunusi aka kamashi ya d'auka ma zasu sa afito dashi,tunda akan Siyasar su yay kisan kai , alokacin da suke bangar siyasar su Alhaji sunusi su ne ' Yan dabar su da suke sawa suke sace akwatin zab'e sannan su tar watsa taro shi sarkin gida kisan kai yay ya sari Wani agent na warin zab'en da suka tar watsa, shine police suka kama shi aka kawo shi prison d'in nan, dayake su Alhaji sunusi manya ne nunawa sukai basu ma sanshi ba ,ya d'auka zasuzo daga baya su sa fito dashi Amma yaji shiru har yau , wannan Abu da suka masa yayi matuk'ar B'ata masa Rai,Amma duk da haka Bai sare ba dan gani yake baza su tab'a watsar dashi ba zasuzo su fitar dashi , duba da asanadin siyasar su aka kamashi Kuma ai su suka sakashi ba wasu ba,tun Yana Saka ran yau gobe harya fidda ran su Alhaji sunusi xasuxo su sa a fitar dashi.Kuma da ma ya k'ullacesu Dan yasa a ransa duk ranar Daya fito daga gidan yarin nan ya ce "wlh sai yayi a jalin su Alhaji sunusi, sai gashi Yana xaman xamansa ankawo Mai su har Inda yake zaune,gashi Kuma b'angangaren su aka kawo Alhaji sunusi shida babajo Ali,to shine fa tun daga nan ya sakosu agaba da sakasu aiki,shine ya ce suyi masa tausa ,gyaran gado shara ,ko Kuma yace suyi masa wanki,ga ya tulo musu har Mayan prisoner's yace su zasu wanke ,ko Kuma yace baxa suyi bacci ba gugar kayan su prisoners din Nan zasu kwana sunayi,gashi fa yaro ne Amma sai iskanci fal ciki,kowa tsoronsa yake agidan har su kansu gandoro bobin baya k'yalesu idan suka masa ,farko Alhaji sunusi nunawa yay Yama Raina masa hankali ya ce "zai sa shi aiki ,Kuma Gani yake zai fita daga prison d'in nan tunda akwai abokanan su 'yan siyasa Wanda suke mutunci dasu Yana sakaran xasuxo su fitar dashi, shiyasa farko da sarkin gida ya fara sashi aiki ya nuna Mai Bai isa ba ,aiko sai yaran sarkin gida sukai kansa suna duka


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login