Showing 36001 words to 39000 words out of 278032 words

Chapter 13 - JAMI'AR TSARO COMPLET by MRS SARAKIES.doc

23 Oct 2025

1095

uxuri shiya dauka xanji tsoro Dan Yana Kiran security akan su tafi Dani,wai na bashi hkr ya isa nabashi hkr,ya Tahir yace Dan dai kawai mun bashi hkr ne Amma wlh yadda ya harxuka dinnan da saiya kai station,ya hanaf yay murmushi yace wai na bashi hkr wlh Bai isaba, hanaf yace da kasan Irin wulakancin da yaxo har gida yayiwa mamah akan auran lateef da Rukayya,da kai kanka wlh saika wulakanta shi,shima kansa lateef din bakaga Irin Rashin mutuncin dayaxo har gida yay wa mamah da Auta ba, kawai Dan ubansa Yana daure masa gindi shikenan sai su dinga abinda sukaga dama suna Maida mutane kamar wadannan Basu San mahimmancin suba,....


Ya Tahir yace duk da haka hanaf batasu ZA'A dakaba ,idan shiya ja , mu saimu saki kasan Mamah ita Batasan tashin hankali, shiyasa take kyaleshi yake duk abinda yakeso akanmu,hanaf yace to wlh itama yanxu mamah ta fara gajiya da halinsa ,ta fara maida masa da martani tunda shi baisan xuru ba, Kuma wlh indai Ina da rai ko kai baxaka sa Baki ba wlh baxan taba bari ya aurawa auta lateef ba tunda ba sanshi take ba,wlh koma tana sanshi baxan tava bari mu hada xuri'a dasuba,ya Tahir yace hmm hanaf kenan ka dauki abin da xafi aishikenan,daga haka yaja bakinsa yayi shiru Yana kallan titi,....


Suna xuwa gida bayan sunyi parking hanaf direct part dinsa ya wuce baima shiga gidanba domin Alhaji sunusi ya Bata masa Rai,sai ya Tahir ne ya shiga main falon gidan Yana shiga yay sallama,babu kowa a falon ,ya qara yin sallama baba lami Dake kitchen ce ta leko ganin shine washe Bakinta tace a'a mutanan Lagos ne agidan ,lale sannu da xuwa,ya Tahir Dake murmushi yace yauwa tareda da gaidata,haka ta ansa tana bari na kawo Maka ruwa yace a'a baba kije ki cigava da aikinki ,bari naje dakin Mamah,tace toh ,haka ta koma ta cigava da aikinta shikuma ya haura sama,...

Yana xuwa yay knocking kofar dakin Mamah,ta ansa da ashigo haka ya tura kofar ya shiga,inda ya Tarar ta kan darduma,tana Laxumi,haka ya karasa ciki, ganin sa yasa mamah kasa boye mamakinta tace a'a Tahir Kaine yau Kuma a garin ,babu sanar wa,ya qarasa shiga ciki ya xauna kusa da ita ya shafa kansa yace mamah Ina kwana mamah tace lpy lau Tahir kaxo lpy ,yace lpy lau alhamdulillah yace naxo ne kawai na duba ku gove in Sha Allah xan wuce mamah tai murmushi tace mungode sosai sannu da xuwa yace yauwa,haka suka fara hira , Batare da sun Sako zancen auran ruky ba,hardai lokacin sallah yay ya fice yace zaije yay sallah ya dawo, mamah ta ansa masa,haka ya fice itama ta miki ta shiga toilet,.....


A bangaren Alhaji sunusi suna barin gidan ya dinga sakin huci Yana xage xage yace SA'A da kunbarni nanuwa yarannan ni basa'ansa bane ,yaron bansan lokacin Daya Raina niba nida ake tsoro ake bawa girma Amma kwata kwata yarannan Banga alamar haka a tattare dashiba,wlh sbd Tahir kawai na kyaleshi badan hakaba wlh da sai ankai minshi cell nasa an faffasa masa jiki an sauya masa kamanninsa,yayi laushi ya koyi iya magana a gavan Manya yadda ko sashi akai yamin rashin kunya baxai yiba, tukunna xansa asakeshi, Hajiya SA'A tace Dan Allah yallabai kayi hkr aiba wannan xaka duba ba alakar Dake tsakani da Kuma siyasarka xaka duba ,...


Yanxu kasan abin yadawa a social media ba wahalane dashiba musanman ma kai da kake Neman takara a yanxu,Yay tsaki yace wacce Irin Alaka babu ruwana da wata Alaka wlh sbd Tahir da ke kawai na hkr ,da Kuma siyasar tawa da kika fada Amma babu komai akwai gaba matukar bai gyara harsanshiba,haka Hajiya SA'A ta dinga tausarsa kafin daga bisani ta baro sashen nasa Dan barshi ya shirya,Dan fita xaiyi sukaxo suka tsaida shi da maganar da Bata da muhimmanci karshe ma aka Bata masa Rai..


_________?&

Kabiru ne ya dawo wujiga wujiga jikinsa duk raunika, kafafuwansa duk kasa kamar Wanda sukai wasan kokawa,haka yaxo ya haye kangado ya kwanta,yana sauke numfashi,can wayarsa ta fara ringing ya lalumota ya daga ya Kara a kunnansa,daga Daya bangaren abokinsa xailani yace ya Maza,ka karasa Gida kuwa, Kabiru Yana daga kwance yace ,ka ganni yanxu na dawo Allah ya taimakeni na kwace a hannun kulawannan ,xailani yace wlh Nima dakyar na dawo gida,Ina kwacewa ahannun su Kaine kawai ja fadomun duk da nasan baxaka tava kamuwa ba,Amma sbd Amana nace bari nakira naji lafiyarka, Kabiru ya e wlh zailani ka ganni sai godiya,ka kira su osi Muji, Allah yasa Suma sun kwace,zailani yace no yawa oga kb bari nai plashing nasu,daga Haka ya katse wayar ,yay cilli da wayar geban gadon ,yay rufda ciki ya kwalawa Ameenah kira,...

Ameenah Dake tsakar gida tunda ya shigo ta bishi da kallo tana mamakin Hali Irin na Kabiru ta shigo dakin Jin Yana Kiranta,bayan ta shigo tace gani, batareda ya kalleta ba,yace doramin ruwan zafi,ta ansa masa ta fita,bayan ta Dora masa ta cigaba da aikin ta,saida ruwan yay xafi sannan ya fito daga dakin Yana dingishi ya debi ruwan ya sirka sannan ya wuce toilet danyin wanka Ameenah ta bishi da kallan takaici
da mamaki,....


_______?&ZARI'A

Yayan ummah malam sabi'u bayan yaxo yay wa ummah tas akan ta dauke idanta akan Ameenah dole saitana kau da kai itama,aidama rayuwar aure yar hkr ce yau Dadi gobe babu Dadi,ba kullum ake kwana a gadoba,svd haka ta daure ta daina sa damuwa aranta akan Ameenah da auranta itadai ummah badan ta yarda ba ko taji,haka ta dinga karfin halin ansa masa da ka,baba asabe tace wlh Yaya sabi'u kullum haka nake fadawa maimuna ta dinga kauda kai,gashi Kuma wannan yaran Kabiru yadda yake kaunar Ameenah Wlh Allah Yaya sabi'u saika Gani tukunna,Amma gabadaya NEMA take ta kashe mata auran nata,malam sabi'u yace kijifa wannan Rashin hankali Dan Allah,to yanxu idan Kikasa ta kaso auran waxaki aura mata,ko sata zaki agaba kuzauna agidan kina kallan ta,duk Wanda yay aure ya dawo gida ya xauna wlh rayuwarsa baxata tava xama daidai da kafin auran ba,tunda ya riga Daya girmi xaman gidan, ummah cikin takaici tace yaya sabi'u yanxu saika yarda da abinda munafukar matarnan tace Maka, ..


Ta nuna baba asabe tace asave ki tashi ki bar gunnun tunda sharrin naki da kike bina dashi ya bar kan malam ya Dawo kan yayana , yanxu Kuma zaki hadani da yayana, asave tace kaji malam ke maimuna yanxu gyara kayanka saiya xamto sauke muraba, ummah tace bansaniba munafuka ,malam sabi'u ya dakawa ummah tsawa yace ba gsky take fada miki ba, ai maisanka shizai fada Maka gsky maimuna Amma ke kwata kwata bakya ganewa, ummah ta cika tai fam malam sabi'u sai fada yake mata,yace wa baba asabe idan ummah ta qara Sa baki acikin sha'anin Auran Ameenah ta fada masa ko ita ko malam Auwalu,cikin farin ciki baba ta asabe tace masa to ta shige daki ta dinga taka rawa ganin komai na tafiya mata yadda ya kamata,malam sabi'u Yay taiwa ummah fada kafin ya qara musu nasiha itada malam Auwalu sannan ya fita, baba asabe tafito daga dakinta Dan gulma tace mungode Yaya sabi'u yace a'a asabe babu komai , Allah ya qara xaman lpy,baba asabe ta ansa da Ameen,tana yiwa ummah murmushi da Kuma Wani kallo Wanda itakadai tasan MA'Anarsa,haka ummah tashige daki ta dinga kuka kasa kasa,yanxu ya xa'ayi yarinyar nan Tana cikin wannan halin Amma ace bazataje ta duba tava,Amma tasan hanyar da zatabi,haka ta dinga sake sake aranta,itako me zatai wa asave akan ta daina shiga harkarta,ta daina sa mata Baki cikin sha'anin yayanta da Kuma itama kanta,itako me taiwa asabe da kullum takesan ganin ta muxan tata,ta Bata mata Rai,...




07066508376_______
'?
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DC2ekqRnajZAQQvErdaWfD

*____JAMI'AR TSARO____*


*____THE WOMEN POLICE ____*


*NA*


*_____NAJA'ATU UMAR FAROOQ _____*


*_____(MRS SARAKIES)_____*


*QUEEN OF WRITERS ASSOCIATION (IN QUWA)*=?1?


*Bismillahirrahmanirrahim*


____season one ep 1?? 7??


________?&

Ranar Monday DCP da kansa ya kira Ruky office dinsa akan idan ta gama abinda take ta shirya suje asibitin yaje yaga halin da shafa take ciki,haka ko akayi bayan ta gama aikinta ta taka taxo har office din DCP, inda shima ya rage nasa aikin ,haka suka fito ita dashi sai wani police shima ASP ne, sunan sa anas suka tafi a motar DCP, ASP anas shine ke tukawa sai DCP a gefensa sai ruky Kuma a kujerar baya,da ace ba akan case din nan bane da baxata tava yadda tafiya ta hadasuva daga shi sai ita ba, danma Allah ya tai maketa a kwai wannan ASP da Batasan ya xatai ba,haka suka kama hanyar asibitin, DCP da ASP anas ne kawai ke hirarsu Amma ita ruky kallan gefen hanya kawai take,....


Babu dadewa suka karaso asibitin inda DSP tun daga bakin gate din asibitin yake jinjinawa ruky sbd yasan asibitin na kwararrune sosai, Kuma gashi private ya tavva ta kashe kudi sosai bayan securityn gate din sun Bude musu gate din suka shiga, sukayi parking motar su a parking lot din Dake asibitin Dan komai nasu daban yake , ASP anas ne ya fara fitowa yay maxa yaje ya budewa DCP muktar motar ya matsa baya cikin girmamawa ya Sara masa yay murmushi ya daga masa hannu Yana Mai fitowa daga cikin motar,sai itama ruky ta fito ,cikin shigarta as usual na uniform dinta sai after data Saka Asaman uniform din sai talhat Kuma light blue Wanda ya qara fito da ainihin fatar ta,Dan ba karamin kyau shigar take mata ba, DCP ya Kalli anas yace ASP anas bari mu shiga mofito ASP anas yace yes sir a fito lpy,ya koma cikin motar ya xauna DCP ya Tako har gaban ruky Dake tsaye daga gefe tana kallan kasa,yay murmushi yay qasa da murya yace my let go ta dago da dara daran idanuwanta ka kallashi sai Kuma ta janye su ta mayarsu kan hanyar da zasuvi cikin cool voice din ta tace yes sir ,haka suka jera suna tafiya DCP yace but incharge asibitin Yana nan ne ya kamata na fara xuwa mu ganshi tukunna,ruky tace may be yana nan yace ok muje haka suka cigava ta tafiya duk inda suka ratsa gaisuwa ake musu cikin girmamawa svd sunga jami'an tsaro,haka Suma idan sunga patient ko patient relatives suna musu ya Jiki da Kuma masu jiki,Dan shima DCP akwai shi da tausayi,...

Bayan sunje office din incharge din asibitin,ya tarbesu cikin girmamawa Dan yasan DCP muktar tunda jami'in tsaro ne sananne Wanda ya Dade akan aikinsa,Kuma aiki ma ya tava hadasu haka ya tarbesu cikin girmamawa,inda ya Basu wurin xama bayan sun xauna ya kawo musu ruwa da lemo acikin fridge din office din bayan sun sake gaisawa,DCP muktar ya Danyi gyaran murya yace muna da patient ne asibitin nan naku shiyasa ka ganmu,Doc bala yace awani department take DCP ya fada masa ,Doc bala yace ok nagane patient din doc Fatima ta fadamin case din ta harma an Bada scanning din da xa'a mata a Lagos ko ,is she d one ,ruky ta jinjina kai yace ok,dama patient dinkuce,doc Fatima ta fadamin komai akanta harma file din nata ta kawomin na gani,tace min wata women police ce ke kan case din itace ma ta kawota , DCP muktar ya jinjina kai, doc bala yace ai abin yayi worst dayawa,DCP muktar yace Yanxu haka xuwan da nai naxone naga yarinyar, doc bala yace ok sir , badamuwa muje idan ka shirya, haka suka mike gabadaya suka fita xuwa dakin da aka kwantar da shafa,....


Suna xuwa suka tadda baba lami ce rike da shafa sunfito daga toilet data mata tai wanka ,tana takawa ahankali dai dai tana xaunar ta bakin gadon sukuma suka qaraso cikin dakin bakinsu dauke da sallama,baba lami ta juyo tana ansa musu,ganin Ruky yasata Kara fadada murmushin ta,ta gaidasu cikin girmamawa, suka ansa mata da Kulawa,doc bala ya nuna musu wurin xama suka zauna,Ruky ta Kalli DCP muktar tace sir wannan itace mahaifiyar shafa ga Kuma shafa axaune, DCP muktar ya jinjina kai yace sannu baba , yana kallansu Sosai Dan baba lami ta canxa sosai tayi kyau ta qara gogewa itama kanta shafa fatarta ta murje Dan dai kawai tana fama da jinya ne,Kuma tana Shan magani babu laifi sauki Yana xuwa da kadan kadan, baba lami ta sauke kanta qasa tace sannu yallabai,ruky tace baba wannan shine mataimakin commissioner na jihar Kaduna,shima ya naimu zai tsaya muku bayan munje mun shaida masa Halin da shafa ke ciki,shima yace in Sha Allah xaiyi iya bakin kokarinsa wurin tsanan ta bincike,....

Baba lami ta dago ta kalli DCP tace ranka ya Dade mungode sosai Allah ya Saka da Alkhairi,yace karki damu baba in Sha Allah xamuyi iya bakin kokarinmu wajen ganin Wanda yay laifin nan,duk Wani abinda xamu bukata na bincike nagani cikin statement din da aka dauka, ASP Rukayya ma ta qaramin bayani sosai Kuma na gamsu,inma da Wani Karin bayanin zaki iya yimana ko Kuma wani qarin hsk wurin binciken mu,ya Kalli shafa wacce ke kwance akan gado , ta lullube jikinta,yace sorry kinji Allah ya Baki lpy,ya Kalli Ruky yace , ASP Rukayya xamuyi iya bakin kokarinmu in Sha Allah, ya kalli baba lami,yace baba mu xamu tafi dama xuwa nai na ganku ku saki jikinku in Sha Allah komai xai dadaita itama xata samu lpy,.....


Baba lami ta fara matsar kwalla tace nagode sosai ranka ya Dade, nagode nagode Allah ya Saka da Alkhairi, Allah ya Baku iko,ta kalli ruky wacce ke kallanta tace jami'a babu abinda xance Dake saidai nace Allah ya biya miki bukatunki na Alkhairi, Allah ya faran ta miki kamar yadda kike faranta mana,ruky ta matso kusa da ita tai qasa da murya tace baba Ameen thumma Ameen nagode da addu'ar da kikemin,Dan Allah baba kidaina kukan nan haka,banaso naga kina Kuka ai hakkin mune amatsayin mu na jami'an tsaron damu tsaya muku tunda har mundauki ALKawari, DCP muktar yace kwarai kuwa,baba karki damu Dan Allah kidaina kukan nan,yaciro kudi masu yawa ya ajiye musu Bakin gadon yace to baba Allah ya qara mata lpy mu xamu tafi sai munsake dawowa,.....


Baba lami ta tsaida Kukanta,tace yallabai farin ciki ne yasani haka nagode nagode muku, Allah ya Saka da Alkhairi suka ansa da Ameen suka tafi,ruky ta tsaya taxo kusa da baba lami Ganin sun fita tace baba Khalil ko yaxo,baba lami tace yaxo daxu Ruky ta sauke numfashi tace nayi ta Kiran sane bansameshiba Amma tunda yaxo shikenan,baba bari muje ki tayamu da addu'a in Sha Allah tunda DCP ya shiga case dinnan muna sa Ran nasara aciki,baba lami tace jami'a addu'a kullum munayi Kuma in Sha Allah xamu cigava dayi , Allah yay muku albarka, ruky ta ansa da Ameen taiwa baba lami sallama ganin DCP na Kiranta a waya,ruky tana fita ta tadda DCP suna sallama da doc bala,tana xuwa suka qarasa sallama,sannan suka nufi mota,....


ASP anas Yana ganin sun qaraso yay sauri ya budewa DCP muktar motar tareda da Sara masa ya budewa ruky ma sbd DCP,da Yi musu barka da dawowa, DCP yay Masa godiya tareda da ansa masa,suna shiga mota gabadaya bayan ruky itama ta shiga, ASP anas ya ta-da motar bayan sun fita daga asibitin DCP muktar ya bawa ASP anas address din inda akai raping din shafa,Dake hayin rigasa, babu musu ya karba ,babu dadewa suka qarasa cikin unguwar inda Sundan xagaye wurin suna monitoring sosai kafin su qaraso har bakin gate din gidan suna ganin sawun mota alamar idan akaxo direct shiga ake da motar ciki,gashi Kuma anqara gyara gidan ,daga ciki alamun aDan kwanakin nan da ruky batazoba aka qara gyara gidan,Dan iya kofar gidanne kawai ba'a gyara ba,Dan nesa da gidan sukayi parking suna qarewa wurin kallo ,suna na zartar ko Ina, sun Dan xauna awurin sbd suga ko akwai Wanda xai shiga gidan koya fito daga gidan Amma shiru,svd gidan arufe yake da key sunyi xama na kusan one awaya Amma babu Wanda ya shiga koya fito daga cikin gidan ,wayar DCP ce kira ya shigo ,ya duba screen yaga CP ne ke Kiransa,cikin girmamawa yay picking,bayan sun gaisa yace idan ba damuwa yana San ganinsa anjima akwai maganar da xasu tattuna,cikin girmamawa DCP yace ok sir Allah ya kaimu,daga haka sukai sallama bayan ya sauke wayar ya Kalli anas yace mu wuje hayin rigasa division Muji suwa aka kaiwa case din tun farko Basu dauki case din da muhimmanci ba, yace wa ruky xai turo police unguwar nan sudinga wuni,idan ma ta kama su kwana saisu kwana sbd su dinga ganin shiga da fitar koma waye Mai gidan tunda ai ana xuwa gidan
Ruky ta ansa masa da toh tana masa godiya ,daga haka suka wuce hayin rigasa division,.....


________?&

Lateef gabadaya Abin duniya ya isheshi ya Shiga damuwa sosai sbd tun ranar Sunday yake Kiran layin ruky Amma taki shiga ,layin busy ma take sa masa alamar dai tayi blocking dinsa, gashi Allah ubangiji ya jarabceshi da qaunar ruky kamar me,wlh bayajin xai iya rayuwa babu ruky kwata kwata,Dan a yadda yakeji wlh ko ransa xai iya badawa akanta ,Amma Kuma sanda yake mata baya hanashi yay mata rashin mutunci koya sata Kuka,shi kansa baisan Mai yasa baya iya controlling kansa ba akan Ruky bayaso yaje gidansu,sbd hanaf Kuma yasan ko karan haukane ya cijeshi baxaima Jeba , Dan Babu Laifi ya Maru a wurin Hanaf Dan Saida yatsunsa biyar suka kwanta a both kuncinsa,.....


Yanxu ma haka kwance yake Daya daga cikin dakunan dake gidan haydar ,ya baje akan gado Dan yanxu ya gama samun nutsuwa da wata Daya kawo gidan ,bayan sun samu nutsuwa ita Kuma ta shiga toilet danta gyara jikinta,harta fito Bai saniba,tace Beb wlh ka gjiyr Dani , gabadaya jikina ciwo yakeyi Yi tayi managar tana nufar gaban mirror dan tsane jikinta da towel Dan daga ita sai towel ma,ta Kuma shafa Mai ,haka taita surutu Bai kula taba Saida ta gama shafa manta ta shirya sannan ta qara Yi masa magana cikin daga murya Dan yafi jinta sosai,...


Yay firgigit yace hava aneee wannan Kiran fa ta matso kusa dashi tana shafa kirjinsa Dake Bude duk gashi tace Ina ta Maka magana ka kyaleni tunanin me kake


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login