Showing 42001 words to 45000 words out of 278032 words

Chapter 15 - JAMI'AR TSARO COMPLET by MRS SARAKIES.doc

23 Oct 2025

1108

bidirinsa ai dama na fada masa gsky shine dai Bai dauki abinda GSK ba sbd haka ki bar maganar nan,idan har saina dinga kula shine ko Kuma wani bashi lokaci na,wlh saidai ya bar case din na karbi kayana ai dama banyi niyyar Sako kowa ciki ba kece kika dage da saina sashi,sbd haka idan bazai iyaba xan iya handling kayana,....


Hanan ta sauke numfashi tace ni ba haka nake nufi ba,Ina nufin xaifi daukar abinda muhimmanci, ruky tace Kinga Hanan nifa ba sanshi nake ba, why not ke baxa ki bashi kulawar Dani ban bashiba,itafa soyayya ba'a dole, please & please na rokeki Dan Allah kidaina sakomin maganar Wani DCP,Hanan tace Kinga tunda kindauki abinda da xafi shikenan,Abar xancen ,ruky tace dayafi ,Hanan tai murmushi ganin yadda Ruky ta dauki maganar ta da xafi ,sai kumu tace Niko Ina lateef two days bakyamin xancensa koya daina takura miki yanxun ya hkr,ruky ta tabe Baki tace Kinga Dan Allah kidaina kawomin Irin wannan xancen bana so, Hanan tace sorry amaryar lateef ai Babu shiri ruky ta yanke Kiran tana Jin xuciyarta na tafasa,tunowa da lateef da Kuma abinda ubansa ya fada take taji xuciyarta kamar ta faso kirjinta ta fito svd fargar abinda xai biyo baya kuma,Dan shaf ta manta da maganar svd su ya hanaf sun kwantar mata da hankali , Saida Hanan ta fargar da ita sannan ta tuno ashefa akwai wata damuwar a gaba,tana tsoron Allah tana Kuma tana tsoron Alhaji sunusi sbd shi mutum ne kaifi daya babu Wanda yake sashi ko hanashi sai lateef,duk abinda yakeso shi yake masa,ga Kuma ya hanaf Daya Tahir sunce ta kwantar da hankalinta babu Mai aura mata lateef,ita yanxu maganar wa xata dauka acikinsu,take hawaye suka fara rige rigen xubo mata nan dai ta fara anbaton sunan Allah, ta fara juyi agadon nan ganin Daya Saura na dare da Kyar bacci barawo ya saceta.....




07066508376________
'?Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DC2ekqRnajZAQQvErdaWfD



*____JAMI'AR TSARO____*


*____THE WOMEN POLICE ____*


*NA*


*____NAJA'ATU UMAR FAROOQ____*


*____(MRS SARAKIES)____*


*QUEEN OF WRITERS ASSOCIATION (QUWA) =?1?*


*Bismillahirrahmanirrahim*


____season one ep 1?? 9??


_______?&

Alhaji sunusi ne tsaye a haraban gidan hutswarsa,Dake ca bayan gari cikin Dan jaje kadan, idansa ya kada yay jajur saikace Wanda aka aikowa da sakon mutuwa, mutuwar ma saikace lateef ne ya mutu,sai masifa yakewa Wanda yake tsaye gefensa, Wanda kallo Daya xaka masa kasan cewa rekyakken Dan dabane,bayan Alhaji sunusi ya kai kashen xancensa,goga cikin muryar riqaqqun Yan dava,ya karkace bakinsa Iran dai na Yan Shaye shaye yace haba yallabai,Bafa laifinmu bane ba ,motarce aka tareta tsakanin iyaka Nigeria da Libya ,Kuma munyi iya bakin kokarinmu Amma saida Kulawannan suka tare motarnan , ka godewa Allah ma daba'a kama Daya daga cikin muba,...

Alhaji sunusi yay tsaki yace ai dole na damu ,ya xa'ayi Saida muka karbi kudin yaran Sannan Kuma ace babu yaran,yanxu yaushe ZA'A sake Tara wasu har amaye gurbinsu dasu,haba ya xa'ayi kuyi ta mana asara ,yanxu akwai wasu a kasa ko babu,goga yace Babu wasu domin gabadaya mun tattarasu,munbada a tafi dasu,svd jami'an tsaron nan sun fara Gano inda muke,sun fara takura mana, Alhaji sunusi yace yanxu kana nufin kace duka motocin biyu aka rike mana,goga yace eh da yanayin muryarsa,...

Alhaji sunusi ya cire hular kansa sankonsa ya fito sosai ya fara fifita ta hular yace goga Kun ja mana asara ba kadan ba wlh , meyasa baku San yadda kukai kukafi karfinsu ba , kuka kashesu ,bayan ga mamakamai nan mun muku order su masu yawan GSK meyasa ku idan Baku mana asara ba bakwa Jin dadi ne,goga yace cikin yanayin muryarsa haba yallabai,yanxu idan baka gode mana ba,ai baxaka tsine mana ba,yanxu duk kokarin da muke Amma Dan ansamu mistake Sau biyu shikenan zaka rufe ido kanemi ci mana mutunci to tunda baka Gani Irin kokarin da muke ni xan aje aikin saika samu Wani kadora akan aikin tunda ni ka Raina kokarinmu,daga haka ya fara kokarin barin gidan , Alhaji sunusi yay maxa yace haba goga Ina Kuma xaka wlh Rainane ya Baci shiyasa bawai raina kokarinku nai ba,kawai kudin da muka karba wajen mutanan nan ne kawai ya dameni,Kuma ai nasan Kuna kokari Amma Dan Allah ku qara Wani akai , yanxu abinda nake so da kai shine xan Basu hkr nace hanya ce bamu samu va Amma nan da sati Daya in Sha Allah xa'a kawo musu ,...

Abinda nakeso da kai dan Allah ku Dage nan da sati Dayan mucika musu ALKawarin su, atara yarannan kafin sati Dayan,goga ya dago yace nidai wlh idan har ka sake Raina kokarin mu a gsky xan bar harkar nan in yaso ko kai da kanka kayi ko Kuma kasa danka yay Maka yadda kakeso din,ko Kuma ka samu Wanda kaga hankalinka yafi kwanciya dashi, Alhaji sunusi yace, a'a goga,ni ba Raina kokarin ka naiba,aini bani da Wanda yafika abinda nakeso da kai shine Dan Allah a daina sakaci ,gashi yanxu munyi asara,goga yace sai Wani Mai MaiTa kunyi asara kake wato mu mutsaya
Akamamu indai har dukiyarka xata tsira koh,svd mu ba iyayene suka haife muba,sune suka San darajarmu,da Dadinmu ,Amma ku kawai anfaninmu shine mu muku aiki ku biya mu,idan kuma bukata ta biya shikenan mungama anfani,Kuma yanxu da ankama mu aida baxaka tava ta-da hankalinka ba,sbd ba Yayanka bane , Alhaji sunusi yace haba goga meya kawo wannan maganar ni ba haka nake nufi ba,Abar xancen kawai ,.....


Ni yanxu ka amince nan da sati Dayan xa'a samu wasu yaran , Wanda xa'a maye gurbinsu da wadannan da aka kubutar,goga yace eh, alhaji sunusi yace shikenan goga ,ya dauko wasu kudi acikin yar qaramar Jaka yace ga wannan Dan Allah akula,goga ya Wani hade Rai ya jawo jakar ya Bude yaga abinda ke ciki Sannan ya mike ya fice daga gidan bayan ya rufe fuskarsa, Alhaji sunusi Yay tsaki bayan ya tabbatar da fitar goga daga gidan sannan ya dauki waya ya Latso wata number sannan yay kira,babu Bata lokaci aka daga,daga Daya bangaren mutumin yace , Allah ya taimaki honorable,Kuma senator nan Bada dadewa ba, Alhaji sunusi yay tsaki yace kasan ankama motocinmu guda biyu, mutumin yace what, Alhaji sunusi ya kada kai yace yanxu Sha Shan yarannan ya bar gidan nan bayan ya fadamin, mutumin yace Ina dai fatan ba'a kama suba, Alhaji sunusi ,yace babu Wanda aka kama motar kawai aka kama da yaran ke ciki,...

Babajo Ali yace ,nidama damuwata kar akama yarannan suji matsa su fadi suwa suke yiwa aiki Amma tunda har sun tsira abin yaxo da sauki,yanxu , ya xamuyi Da mutanan nan,alhaji sunusi yace wlh abinda nake ta tunani kenan nace bari na kiraka mu tattauna ya xamuyi ,babajo Ali yace,kawai aka Basu lokaci kadan su sake Tara yaran in yaso mu sai mubasu hkr muce matsala ce ta Dan faru Amma nan da lokaci kadan kayan su xasu iso, Alhaji sunusi yace nima tunanin da nai kenan ,haka Kuma nace suyi ,nan ya kwashe duk yadda sukai da goga ya fadawa babajo Ali,babajo Ali yace shikenan wannan ma Yayi ,karka damu xan kirasu. Nai musu bayani, Alhaji sunusi yace shikenan babajo nagode,babajo yace ai muna tare daga haka sukai sallama, Alhaji sunusi ya koma cikin falon gidan ,....


_______?&


Ummah ce xaune abakin kofar falonta tana xaune tana Jin radio,misalin karfe takwas da Rabi na dare , Nana Kuma tana cikin falon tana karatun exam din da xasu fara nan da few weeks, baba asabe itama tana kofar falonta a xaune tana lissafin kudi,tana ware Wanda xasuyi siyayya na abincin siyarwar da suke,zaliha Kuma ta fita dandali,baba shima Yana kokarin fitowa daga dakinsa rike da carvi a hannunsa xai fita waje yasha iska,sallamar da akayice yasa su gabadaya dagowa suna kallan maisallamar ummah ce ta ansa, baba asabe Kuma ta karve da cewa yaron Daya shigo meyafaru,yaron yace wai ana sallama da Nana, ummah tace waye, yaron yace Wani ne awaje, ummah tace kace Nana Bata isa fita xance ba,yay hakuri saita gama makaranta,....

Baba asabe dakewa ummah Wani kallo, ganin malam Auwalu yasa tace haba Maimuna ya xa'ayi,ace ana sallama da danka Amma kice wai Bata isa xance ba , Ina Nana sa'ar zaliha ce, Nana Dake shekara goma Sha uku ta shigo ta Sha hudu Amma kice wai Bata isa xance ba makaranta take wacce Irin makaranta Kuma, makarantar da nidai banga anfanin da take mukuba daga ke har ita Nanan,tunda ba Wani kudi take Baku ba, saima bakin talauci da kuke ciki,yanxu wlh na tabbata daxa'a duba dakinki wlh sisi baxa a samu ba,Amma kindaukawa kanki Buri na wai sai Nana tayi Boko, Bokon Banxa Bokon wofi,wlh ki kama Sana'a kiga idan Baki xama kamar niba,nida zaliha Bata Bokon aibanga dame kuka fimuba, saima talauci kawai da Kuka fimu,...


Ummah da take hararar asabe tace asave wlh na miki uxuri tunda ke bakisan bariba,duk gargadin da nake miki bakya dauka na kidaina shiga sabgata nida Yayana kinki koh,tunda ke jahilace ai baxaki tava sanin Dadin Bokon ba,ai ita Boko ba Saida wata manufa ko buri xakayinta ba,kodan cigaban kanka ,da cigaban da xamanin yaxo dashi kayi Boko,ke kinfiso yayana su xauna karsuyi Boko Susan ciwon kansu ,kamar yadda kema bakiyi ba ,ba Kuma kibar yayanki suyiba,kinfiso yadda kuke cikin bakin jahilci keda yayanki babu arabin babu Bokon Nima yayana su xauna koh,to wlh ni baxanyi wannan jahilcinba,kedai da kikaga xaki iya kije kiyi Kuma wlh Boko saikinga anfanin ta agidannan in Sha Allah indai kina da tsawan Rai agidannan,....


Zakiga anfanin Boko,Kuma xancen yata baxata fitaba,kedai da Kika koyawa taki yar take fita Kuma kike ganin ta Isa zaki iya Kiranta taje,tunda abinda yay Nana shi yay zaliha,daga haka ummah taja tsakinta ta tsuke,baba asabe datai shiru tana sauraran ummah, tace ahayye nanaye a Bokon xanga wani anfani lallai kan ayidai mugani idan tusa xata hura wuta muna nan muna jira indai har ranmu ya kai,lallai iska na wahamar da me kayan Kara,su Boko manya ,da zakice zaliha taje Kuma ai ba ita akace ana sallama ba,da ace da ita ake aida kinsan Tuni ta fifa tunda ke ba Aurar da yar taki zakiyi ba,sauki sata agaba ki ta kallo,Boko yay muku abinda xai muku, ummah tace hmmm asabe kenan jahilci baiyi ba, inda ace kina da ko ilimin Arabi ne wlh baxa ki sawa kanki wannan aqidar ba,....



baba asave xatai magana malam Auwalu cikin kakkausar murya yace asabe,waini bana hanaki Shiva sabgar maimuna agidan nan ba,baba asabe tace malam kanajifa jahila take cemin sai kace ita Bokon tai ko Kuma arabin,ai wlh idan ni jahila ce nida ita aiduk samma Kaine, malam Auwalu ya daka mata tsawa yace ya isa haka,ya Kalli ummah yace maimuna Nana ta fito taje tunda Kiranta ake, ummah ta juyo tai masa Wani kallo tace wlh Allah wanna Karan babu Wanda ya isa yay wa Yata auran wuri,kundai Yi akan Ameenah na kyaleku kaida matar ka Amma wlh wannan Karan babu Wanda ya isa ya takurawa Ra yuwar yata,ni yata Bata isa fita xance ba bare Wani aure,.....


Malam Auwalu yace to idan ba'ayi mata aure ba me xa'a mata, so kike musata agaba muna kallo,itama kanta zaliha fita xance take Kuma ai sa'ar Nana ce,fikon su da Nana aiba babu dadewa,duk da zaliha ta bawa Nana wata uku , ummah ta kalli malam Auwalu sheke tace ashedai ta fitan nifa wlh ko rana Daya aka haifesu wlh Ina kan bakata ,kai wlh ko Yan biyu ne kaga dai sune dai karewar sa'anni koh,wlh Nana baxatai xance yanxu ba,...

Baba asabe tace hmm lallai kan mage ya waye yanxu maimuna kece yau kike Maidawa malam magana Yana fada kina fada,kike musu da malam,hakafa akai akan Ameenah kika dage Sauya gama makaranta Kuma saida ta gama din,Sanna Kika aurara da ita yanxu ma haka xaki akan Nana, lallai wlh Malam duk kaine kake sakar mata take duk abinda taga dama yanxu da ace nice nake Maka abinda maimuna take Maka da tuni Ina gidanmu,ummah tace Badake nake magana ba ungulu da miji nah nake magana,Kuma kema waya hanaki kiyi sai kiyi ai,baba asabe mamaki ya kasheta ganin yadda malam Auwalu ko magana ya kasa yi,can Kuma saiya dubi yaron da aka Aiko Daya gama Jin duk conversation dinsu yace yaro waye yake sallama da Nana,yaran yace salisu ne,Dan gidan Alhaji hamza Mai taki,...

Baba asabe ta xaro ido waje Jin Wanda me sallamar ya fadi sunan Wanda ke sallama da Nana, salisu dai wannan yaron Dan gayu ,Dan Boko waye Bai San ubansa ba , kaf ZARI'A,bare su da suke unguwa Daya dasu sbd kudin da ubansayake dashi ,kai yaranma ance Yana da kudi, itafa shi takewa zaliha sha'awar ta aura Amma shine wai yake sallama da Nana, lallai Bata ga ta xama ba,ai gara ma da ummah tace Nana baxataba, Dan wlh koda ta amince din data fita ,wlh da baxata tava barin ayi aurannan ba , saita shiga ta fita kamar yadda tai a auran Ameenah an fasa aurannan,Jin ummah batai magana yasata yin shiru,tana kallan ummah taji Mai xatace,....


Ga mamakinta da malam Auwalu yace kinji maimuna Dan gidan Alhaji hamza ne Mai taki aisaiki bari taje koh tunda shidai wannan ba talaka bane, ummah ta juyo tace ai malam babu ruwana da Dan gidan uban waye da kudinsa da Rashin kudinsa,kai ba Dan gidan Alhaji hamza Mai taki ba,ko Dan gidan Mai kashin awakine,wlh Babu inda Nana xata Ina nan akan bakata, kune kudi ke gabanku Amma Banda maimuna,....


Mal Auwalu yama rasa Mai xaice svd mamakin maimuna,Kuma a gsky bayasan su qara samun wata matsala Dan yanxu so yake su shirya,tunda tun ranar da yayanta yaxo gidannan ya tafi ya kasa Gane kan ummah,kwata kwata ta daina shiga harkarsa,zadai tai girki idan ranar girkintane,ta Kuma kai masa, abincin dakinsa, kai babu dai abinda ta rage na abinda take masa indai ranar girkinta yay Amma Kuma sakin fuskar da bata masa da Kuma magana yasashi cikin damuwa,Dan haka ya dubi yaron yace ,kaje kace masa Bata isa xanceva saita gama makaranta tukunna,yaro ko ya juya ya tafi ya isar da sakon da aka umar ceshi,...


Malam Auwalu ya koma dakinsa, Baba asabe ta saki Baki ganin malam ya biyewa maimuna ya hana Nana fita xance,Amma Kuma ta Wani fannin taji ranta fes Jin ummah Bata dauki xancen da sauki ba,Dan haka ita wlh ummah kamar ita taiwa Dan haka yanxu xata fara shiri Dan salisu yadawo yace zaliha yake so,yanxu xatasa zaliha ta Dinga daukar wanka tana wucewa ta kofar gidansu ,haka ta cigaba da lissafin kudinta, ummah koh ta kure volume din radio da takeji,Dan wlh wannan Karan babu Wanda ya isa ya mata karfa karfa kan Nana sunyi akan Ameenah Amma wlh Nana dai Basu isaba,...



_________?&

Kabiru Dan Allah Mai nai maka da baka taba sauke hakkina Daya rataya awiyankaba, Kabiru saika tafi kai kwana da kwanaki baka nan sannan baka barmin abinda xanciba, Kabiru karka mantafa mutum ka ajiye agidan ba Dabba ba,wlh ko Dabba ce tunda tana da Rai Kuma kai ka ajiyeta hakkin Kane daka Bata ci da Sha , Amma Kabiru babu abudaya daka tabamin,idan har kaga baxaka iyaba Dan Allah ka Kaini gida da kanka ka samu baba kace kai baxa ka iya rikeniva,ka sakeni na fada Ina hade hannayena alamar rukon Kabiru,Dan wlh na gaji da Irin rayuwar Danake agidan Kabiru,da sai kace a firixun ai wlh ga rama firixun ana basu abinci ko saudayane Amma nifa Kabiru ko chokalin shinkafa xan iya Lissa saunawa ya Ya taba ciyar Dani tunda naxo gidannan,.....


Duk wannan maganar da nake cikin dauriya nake yiwa Kabiru domin wlh mugun tsoransa nake ji,sbd Irin dukan dayake min,yanxuma bana tunanin idan na gama maganar da Danake masa ya rufeni da duka Dan kadan daga cikin aikinsa ne,Dan dazu ma ganinai Yana waya,gashi yanxu Kuma Yana hada kaya cikin wata yar qaramar Jaka,alamun dai tafiya zai Kuma da dukan alamu xai Dade,wani dai xance suke Wanda bangane me suke fada ba awayar , Yana cewa wai kulawa sun kusa kamasu ,ba Dan Allah yasa sunsha da kyar ba,Kuma abin ya tsayemin sosai,araina, Babban damuwa Tama nida Bansan Sana'ar da Kabiru yake ba,Dan haka xanga ya shigo gida Wani lokacin da gudu Kuma kiga jikinsa duk jini Wani lokacin ma duk raunika haka xakiga jikinsa,wannan abun Yana matukar damuna,....


Maganar dayake min ce ta dawo Dani daga duniyar tunanin Dana tafi Inda ya dago daga daure takalminsa da yake me igiya ,ya fara magana da,kinsan Allah baxan tava sakin kiba,domin kina min anfani ta Wani fannin,idan Kuma kikai yunkurin tafiya gida kinsan halin tsohonki,kamar yasa na dawo Dake ne,duk abinda na fada masa dashi xaiyi anfani , sbd haka idan kina San kanki da arxiki to kixauna,xancen ciyarwa Kuma,bazan iya ba,tunda bani nace da tsohon ki dole saikin dawo ba, sbd haka banida dashi, Ameenah da hawaye ya gama Bata mata fuskarta tana kallan Kabiru tace Dan Allah kataimakamin Kabiru Niko gidama ka Kaini in yaso idan xaka dawo saikabiya ka daukoni,ya wurga mata Wani kallo,ya mike Yana saba jakarsa a kafada,yace ni ban hanaki tafiya gidan Kuba ga hanya nan ,Amma idan Kikasa tsohon ki ya kirani akan naje na daukoki wlh idan muka dawo gida saina miki dukan mutuwa ,daga haka yay gaba abinsa,Saida yaje bakin kofar dakin sannan ya juyo ganin tana a yadda ya barta ga hawaye sai xuba yake yasa shi Ciro dubu biyu a aljihun gaban rigarsa ya jefa mata yay gava abinsa,....




07066508376________
'?Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DC2ekqRnajZAQQvErdaWfD



*____JAMI'AR TSARO____*


*____THE WOMEN POLICE ____*


*NA*


*____NAJAATU UMAR FAROOQ____*


*____(MRS SARAKIES)____*


*QUEEN OF WRITERS ASSOCIATION (QUWA) =?1?*


*Bismillahirrahmanirrahim*


____season one ep 2?? 0??


_______?&


Mamah ce xaune tana kallan labaran karfe takwas da Rabi na safe ,baba hasiya kuma tana gefenta daga Daya site din ,Mai Maici ma Ake Dan jiya da wuri tai bacci sbd svd ta fita unguwa,agidan TV na GADANGA,Wanda yawan sace mutane da ake da Kuma kashesu da ake Batare da hakkin suva,kai hukumar ma itama Kanta yan ta addar Basu kyale suba,yanxu gabadaya hanyar Kaduna da Kewayanta,harma da qauyukanta Basa cikin kwanciyar hankali,yanxu ko tafiya xakiyi kina far gava ne,shin xaka dawo ne ko baxaka dawo ba, mutane dayawa, suna San tafiya Amma gabadaya sun hkr sbd masifar da suke ciki,.....


Mai labaran


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login