Showing 33001 words to 36000 words out of 278032 words

Chapter 12 - JAMI'AR TSARO COMPLET by MRS SARAKIES.doc

23 Oct 2025

1027

Hana uncle yamin aurannan wlh mutuwa xanyi nace banason lateef,ya Tahir yace naji Amma saikin daina kukan tukunna, Amma Ina ta Kasa dainawa ji take kamar ta kashe kanta,idan ta tuna kalaman Alhaji sunusi,ya Tahir ya rasa ya xai mata kukan ta kawai take yay shiru yana jinta Saida ta Dan sassauta sannan ya rarrasheta yace ta daina kukan babu Mai aura mata lateef da ALKawarin xai shigo Kaduna gove, sannan tai shiru ta fara sauke numfashin salama Jin xaixo gove,....


Bayan ya gama rarrashin ta sukai sallama ,ta kira anty mufeeda ta fada mata anty mufeeda ta kwantar mata da hankali tace itama in Sha Allah xataxo gobe ko Kuma cikin satin ,haka sukai sallama Dan yau kosu mimie batace abawa ba,bayan tafiyar Ruky daki ,hanaf wucewarsa daki yay shima sbd bakin ciki yaso mamah ta barshi yay wa mutumin nan Rashin mutunci Amma ai akwai lokaci badai yace nanda sati biyu ba,Allah ya kaimu xaiga ta yadda ya isa ya aurawa Ruky lateef zaiga isar tasa da takamar dayake da ita akansu,da ai Bai nuna isar akan su ba,na kulawa dasu sai Yanxu dayake biyan bukatar Dansa ce,....


Mamah gabadaya ranta ya gama baci taga alama Saita bitowa Alhaji sunusi,a ainahinta tukunna, wannan isar dayake nuna mata,ta Isa haka, daki tashige tana isa taji wayanta Dake kan mirror Yana ringing tana dubawa taga mufeeda ce,kamar baxata daga ba saikuma tai picking sbd ranta a bace yake,tai sallama mufeeda ta ansa mata tareda gaisheta mamah ta daure ta Shanye damuwan da take ciki,Dan kada mufeeda ta Gane, mufeeda tace mamah wlh Yanxu Auta ta kirani akan wai yanxu uncle sunusi ya bar gidan nan Sannan wai zai aura mata lateef,bayan tace Bata Sansa ,waidama ba'a bar wannan maganar bane,nan dai ta kwashe yadda sukai da ruky ta fada mata, mamah ta Sauke numfashi tace mufeeda Aina fada Mata ta kwantar da hankalinta babu Mai mata auran dole, shima Alhaji sunusi,fada yake ,svd haka ki kwantar da hankalinki,bana San ku ta-da hanakalinku , mufeeda tace shikenan mamah Allah yasa, mamah tace Ameen daga haka sukai sallama,...



_________?&

*ZARI'A*

Malam xuwa nai yaudai ka barni naje na duba AMEENAH, shekaran jiya da Nana taje akwance ta tadda ta Bata da lpy,sbd haka kabarni naje na duba ta ummah ta fada tana kallan malam Auwalu dayake shan koko ga dumame a gefensa cikin wata silver, saida ya sauke ludayin Daya kai bakinsa sannan ya duveta dan itace da girki,yace maimuna ita Nana ce dataje gidan ta tarar da Ameenah Bata da lpy, ummah tace kwarai kuwa malam Kuma kasan dai Nana baxatai karya ba, shiyasa ranar na cemaka jikina yana bani Ameenah ba kalau take ba Amma kuka min musu kaida matar ka,to kaga yanxu tunda an gano min da GSK ne saika Barbi naje ai,....


Malam Auwalu ya sauke numfashi yace,ba kinyarda nai da keba maimuna kawai Gani nai Bai dace ba,Kuma Kinga ya ran nan Yana iya kokarinsa akan Ameenah,sannan yanxu Kuma da ace batada lpy da yanxu ya rannan ya kirani ya fadamin, ummah cikin takaici tace yanxu ai ya kiraka ya fada Maka koh,malam Auwalu yace abashshima Batada lpyn ,kila jinyar Bata kai wacce xai kira ya fadamana bane shiyasa kika sani ko bayaso ya ta-da mana da hankali ne, ummah tace nifa malam babu abinda yamin xafi da Kiran ya fada ko karya fada ,xuwa xanyi kawai Nagano halin da 'Yata take ciki, Nana fa tace tsallake ta yayi yay tafiyar sa sai makociyar ta ce ta kaita chemist,nifa malam dama basan wannan kaddararran auran nake ba, Kaine ka dage,kafi karfina Dan kaga ka fini iko da ita,


Ga Wanda yaxo Neman AURENTA mutumin kirki amma Ka 'ke kashe kasa kace sai Kabiru,wlh danasan hakane wlh da sai inda karfina ya qare wajen ganin aurannan baiyuba, ta karasa fada cikin bacin Rai,malam Auwalu Daya saki Baki Yana Jin ummah Dan baitaba ganin bacin ranta Irin wannan ba, lallai Mai hkr idan aka kureshi bashida kyau Kuma muddun ya bari taje wajen Ameenah kila baxata kwana agidan Kabiru ba xata dawo da ita gida Amma Kuma yasan maganinta,ya sauke numfashi yace oh ta haka kika bullo kenan aidama Nasha ganin dama bakyasan Kabiru bansan me yarannan yay miki ba,da kika tsaneshi haka,sbd haka maganar karshe itace baxa kije ba ummah ta mike ta fito tana kokarin barin dakin tace wlh wannan Karan saidai kai komai xakayi malam Amma nagaji saidai kai hkr Amma gidan Ameenah saina je daga haka ta fito daga dakin inda malam Auwalu ya biyo bayan ta Yana mata magana,Hakan da yay shiya janyo da hankalin baba asabe Dake cikin uwar dakinta tana lissafin kudi, Amma jin hayaniyar mowa da mijin ta???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? yasata tai bacali da kudin ta fito da sauri har xanin ta nekan kadata Amma ta mike,...


Jin malam Auwalu na cewa idan ta fita daga gidan nan xuwa gidan Ameenah Bada yawunsa ba ita Kuma ummah tana maimaita masa Saita je,tana Kuma fadar Rashin kirkin Kabiru,baba asabe tace haba maimuna batun rannan aka kashe wannan maganar ba,malam Auwalu cikin fushi yace Nana ce taje ta Gano wai Bata da lpy shine ita Kuma tabi duk ta tada Hankalinta,baba asabe Jin ta samu abinda takeso yasata,gyara tsayuwarta tace ,hmm maimuna kina bani mamaki kinada kulafucin 'Ya'ya Nima inada 'ya'yan nan bawai bani dasu ba Amma kintaba Ganin muna dayan biyun akansu nida malam , Ke garake ma ba nisa tai dakeba nikuwa kinsan bama anan kusa damu suke ba,Kuma ni sai insamu malam ince duk abinda ya samesu saina je,Kuma wlh saikisa ma mijinta yaga kamar ya gazane,yanxu Kabiru yadda yake kokari akan yarinyar nan ai wlh baxakice baya kula da itaba,kina fa ganin yadda tai tafiyar ta,sama da wata Daya Bata dawoba, Amma data dawo haka malam yay Kiransa akan yay hkr ya tafi da ita,...


Ko musu yarannan baiyiba haka ya tafi da ita yanxu idan Banda Allah yasa Yana qaunarta wlh da baxai yadda ta koma masa gida ba,kodan aidama ke ba kaunar sa kike ba bare kiso auran naga alamar ma kamar so kawai kike ki kashewa yarinyar nan aure,malam Auwalu yace sosai ma to wlh ba'a gidannan ba,babu Kuma inda xakije, ummah data fito daga dakin ta da hijab dinta,da hawaye Yagama wanke mata fuskarta,ta kalli baba asabe kallan takai ci,tace asabe idan Ina magana da malam kidaina sakamin Baki,nasha fada miki Amma bakyaji ko,Kuma dakike xancen bana San auran banason Kabiru, barima Kiji na Maimaita miki tunda ke muna fukace,eh banasan auran Kuma baxan tava San wannan AURAN ba,idan har da GSK kikesan ke Kabirun Kuma ya iya rike aure ki aura masa yarki mana,nikuma xansa ya sakomin yata ,ke Kuma zanga idan har San gsky kike wa Ameenah akan ta xauna dashi saiki aura masa zaliha shine karshen abinda zakiyi na yadda da cewa eh lallai Kabiru ya iya rikon AURE,baba asabe fa sai bakinta ya mutu Jin ance ta aurawa zaliha Kabiru, ...

Tab itako hauka take ba xata yadda ta aurawa zaliha Kabiru ba,yaran Dan smoking Dan ta adda, ita da take cin buri akan zaliha Dan me kudi taso ta aura,Tai murmushi domin ita kadai ce tasan wanene Kabiru, xancen xucin da takene ya katse lokacin da taji malam Auwalu Yana waya da yayan ummah Kuma yace ya Bata wayar, ganin taki karbar yasa ta a handsfree yadda xataji shi,inda yace cikin kakkausar murya karta kuskura ta bar gidan mijinta ta tafi gidan 'yarta shima gashinan xaixo gidan,Jin muryar Yayanta yasa ta komawa daki tana kuka Mai cin Rai baba asabe koh kiris ya rage ta saki guda sbd farin ciki bataso plan dinta ya wargaje akan umma da Ameenah, daga haka ta koma dakinta ta tattare kudin ta ta cigaba da lissafi ranta fes ,malam Auwalu Kuma ya xauna a tsakar gidan Yana jiran xuwan yayan ummah,....

Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DC2ekqRnajZAQQvErdaWfD


*_____JAMI'AR TSARO_____*


*____THE WOMEN POLICE ____*


*NA*


*____NAJA'ATU UMAR FAROOQ ____*


*____(MRS SARAKIES)____*


*QUEEN OF WRITERS ASSOCIATION QUWA) =?1?*



*Bismillahirrahmanirrahim*


____season one ep 1?? 6??


_______?&

Washe gari ya Tahir ya shigo Kaduna tun daga Lagos,Vai kira mamah ya fada mata xaixo ba iya hanaf kawai ya fadawa inda hanaf yace karya xo gidan sai sunje sun samu Alhaji sunusi tukunna xasuxo gidan Dan kadama mamah ta hanasu xuwa su tunkareshi,wurin 11:00am jirginsu ya sauka ,Yana sauka babu Bata lokaci ya kira hanaf,haka hanaf ya shirya shaf shaf ya fito yay wa mamah sallama akan xaifita yaje ya dawo,...

Dan yasan Alhaji sunusi yau weekend ba lallai ya fitaba idanma xai fita may be Saida yamma,haka ko akayi bayan ya Tahir ya sauka a jirgi haka kira hanaf akan Yana airport, Yana xuwa ya Mai barka da xuwa idan ka gansu kamar twins suna kama sosai , daga airport direct gidan Alhaji sunusi suka nufa Dake GRA ,suna xuwa unguwar securities ne sosai tundaga farkon layin har kofar gidan Alhaji sunusi,inda Saida suka Sha tambayoyi kafin su isa bakin gate din gidan nasa,Amma da sukaxo I'd card kawai suka nuna sbd an canxa security din da suka sani na da,da suna xuwa gidan su gaidashi sbd mamah ce take sasu yin Hakan ,Koda ko Basuyi Niya ba,Amma badan haka ba wlh babu abinda zaisa su xuwa gidansa,aka wangale musu gate din suka shiga,bayan sun shiga akwai Wani gate dinma Dan gate biyu ne shima kuma Duka akwai security din,shidai hanaf gabadaya furkarsa murtuke take ko fara'a babu ,Amma shi Tahir fuskarsa babu yabo babu fallasa, ..


Bayan sunyi parking kafin su fito Tahir ya dubi hanaf yace please hanaf idan munshiga Dan Allah karkai wannan behavior din da kakeyiwa uncle please ka saki fuskar ka kaga sulhu mukaxo dole saimun kaskantar da kanmu tunda ai ba Sa'an mu bane,hanaf ya kalleshi yace Taya ya muda mukaxo Yi masa worning ,nifa wlh badan kace na rakokaba da wlh baxan taba takowa kafata naxo gidannan ba, Amma ya Tahir shine zaka kira worning da sulhu, Tahir yay murmushi yace hanaf baxa ka gane ba dole Irin wadannan mutanan sai ana binsu da lallabawa duk da mune Wanda ake tilastawa,ni sbd Auta nake yin haka, badan hakaba wlh ko kallan gidan uncle sunusi baxanyiva,hanaf ya sauke numfashi yace muje,...

Haka suka fito directly babban apartment din suka nufa Dan gidane na manya manyan Yan siyasa wanda bama kuduna ba Nigeria ma gabadaya keji Dasu ,domin Alhaji sunusi
Dan majalisar tarayyane meci ayanxu,yanxu haka neman kujerar senator yake axabe ne me xuwa, bayan ya rike mukamai da yawa ,suna xuwa babban falon gidan suka Tarar da yan aiki sai safa da marwa suke,inda sukai sallama yan aikin suka hada baki wurin ansa musu,shidai hanaf ya samu wuri ya xauna, Tahir ma ya xauna Daya daga cikin Yan aikince ta karaso garesu tai musu sannu da xuwa,Tahir ne kawai ya ansa,shiko hanaf danna wayarsa kawai yake, Tahir ne yace umm Hajiya SA'A xaki mana sallama da ita,babu musu tace masa to haka ta haura sama , tana xuwa tai knocking kofar ta,ba jimawa ta leko Indo ta tsugunna agabanta tareda sunkuyar da kanta kasa tace Hajiya kinyi bakine shine sukace ai musu sallama Dake, Hajiya SA'A ta Dan yatsuna fuska tace Baki Kuma suwaye Maza ko mata ,inda ta qara yin kasa da kanta tace maxane,tace ni banyi da kowa zaizo da safennan ba, harxata ce ace musu sai anjima saikuma tace kice musu Ina xuwa,cikin girmamawa indo ta ansa mata kafin Hajiya SA'A ta rufe kofar,ita Kuma ta mike taje ta fadawa Tahir cewa gatanan xuwa, Tahir ya ansa mata ta koma Inda take aikin ta,hanaf sai tsaki yake qasa qasa Yana kunkuni, shidai tahir tausar sa yake Yi,Dan kada ya hasala,wajen mintuna 20 saiga Hajiya SA'A ta sauko cikin shiga ta Alfarma bata ganesuba Saida ta karaso cikin falon sannan taga Tahir daya dago Jin Karan takalmin ta,ganin sune yasata sakin murmushi tace a'a Tahir kune agidan,ta samu wuri ta xauna,Tahir shima ya Maida mata murmushin yace wlh mune Hajiya, Hajiya SA'A tace sannun da xuwa haka suka gaisa da Tahir ganin haka shima hanaf ya gaisheta Batare daya kalleta ba,ta ansa masa tana murmushi tace a'a hanaf ,Ina Hajiya Halima ya Tahir yace mata tana lpy,ganin ba'a kawo musu komai ba yasata kwalawa indo kira inda ta karaso wurinta jiki na rawa,ta xube,cikin rawar jiki tace Hajiya Gani,batareda ta kalleta ba tace me kuke jira da baku kawowa bakinnan ruwaba,cikin rawar jiki tace kiyi hkr Hajiya aikin da kika sani nakeyi ,tace to Kuma ke kadai ce Ina su kaltime,tace suna sashen yaya lateef suna gyarawa,tace maxa ki kawo musu ruwa yanxu Yanxu,haka ta mike cikin rawar jiki tai hanyar kitchen, shidai hanaf ya bita da kallan gefan ido ganin yadda wannan yar aikin jikinta ke rawa kamar wacce mutuwa taxo dauka,


kafin kace me Indo ta cika musu gabansu da kayan ciye ciye kala kala Hajiya SA'A tace Ina sirikartawa hanaf yay mata Wani kallo Tahir yay murmushi yace tana gida,ganin ya tahir baiyi maganar abinda ya kawo suba saima Wani jansa da hira da Hajiya SA'A keyi yasa hanaf cewa emm Hajiya munxo wajen Alhaji ne Yana nan, Hajiya SA'A tace eh Yana nan,bari ai muku iso ixuwa wajensa haka ta mike tai partdinsa,babu dadewa ta dawo,tace yace kuje haka suka mike suka bi bayanta, Alhaji sunusi Yana xaune a parlonsa Dan Bai Dade da tashi daga barci ba,waya ma yake yi da abokinsa honorable babajo Ali,akan meeting din da xasuyi da president ranar Monday,, Yana ganinsu ya sauke wayar har suka karaso suka zauna,suka gaidashi atare danshi hanaf gasuwarma ciki ciki yayi ta, Hajiya SA'A ma ta zauna kusa da shi....

Alhaji sunusi ya ansa musu babu yabo babu fallasa,Yana kare musu kallo,Tahir yay Dan murmushi yace amm dama uncle akan maganar auran lateef ne da Rukayya, Alhaji sunusi yace to ya akayi ,Tahir yace dama nace uncle tunda Rukayya naga Bata shiryawa auran yanxu ba,naji kace nan da Wata Daya kadawo Kuma kace nan da sati biyu,me xai hana ayi hkr ,tunda Bata shirya ba Sannan Kuma kaga babu wata shakuwa tsakaninsu,idan aka daga ko nan da 6 months ne kaga kafin lokacin sun samu fahimtar juna, Alhaji sunusi ya dinga yiwa Tahir Wani kallo,shima Kuma hanaf kallansa yake with expression, Alhaji sunusi yace , waidama wannan maganar ce ta kawoku kome,ni ai nariga Dana gama magana tun lokacin Danaje gidan,ko ita Hajiya Halimar Bata fada Maka ba,koshi wannan marar kunyar bai fada Maka ba tunda aishi a gabansa akayi ya fada Yana kallan hanaf da ya Wani make Yana latsa wayar hannunsa, Alhaji sunusi yace Tahir Ina ganin mutuncinka baxan iya barin farin cikin Dana ba sbd kawai abinda Bai kai ya kawoba,zancen Kuma fahimtar juna sau goma xasu fahimci junan ,ni bansan Wani Irin lokaci kuke nufi ba daga ku har mahaifiyar taku,kana nufin navar farin cikin Dana svd kanwarku kome ,


xancen gsky shine kuyi hkr aurannan kawai abari ayishi tunda shi lateef Yana Santa xanxen Kuma fahimtar juna idan Ku aganin ku,Basu fahimci juna ba to idan akai auran xasu fahimta tunda shi namijene itakuma macece jawo ra'ayinta baxai wahalaba,da ace namijinne ma bayaso to da sai a bari din Amma tunda itace ,Ina ganin abarshi kawai tunda idan akai auran xasu fahimci junan nasu,idan ma sanshi ne batayi zai koya mata , tsakanin mace da miji sai Allah sbd haka Abar xancennan kawai,hanaf da tunda ya fara magana yake masa Wani kallo me kama da harara,ya Tahir xaiyi magana Alhaji sunusi ya daga masa hannu haka ya saki baki Yana kallansa,hanaf Daya gama xuwa wuya cikin bacin Rai ya mike ya Kalli Alhaji sunusi da shima yake kallansa ganin ya mike yace kaga ba Alfarma mukaxo NEMA wajen kaba ba roko mukaxo wajenkaba bare Neman taimako,Kuma zanga ta yadda Zaka aurawa Rukayya kaxamin danka,tunda kai baka duba ya abin xaije ya dawo kai kawai ta danka kakeyi ,sankan ya Maka yawa sbd San xuciyarka afili kake nunawa ,ni Kuma wlh indai Ina numfashi xanga ta yadda xaka aurawa Rukayya aure da danka ya kalli ya Tahir Daya kasa magana yana kallansa da tun lokacin da ya fara magana yace ya Tahir ka taso mutafi saida na fada Maka kada muxo Amma kace dole saina rakoka ka dauka zai saurareka ne,...

Alhaji sunusi ya mike yace kai hanaf nikake fadawa Irin wadannan magan ganun,kodan baxan Yi mamaki ba,tunda awajen uwarka ka Gani,da ace Bata faffadamin magan ganu ranar da naje gidan Kuba,da baka Samu damar fadamin wannan maganar sanranka ba,da ace tunfarko ta nuna muku mahimmanci na agunku,da baxa kaxo gabana kana fadamin magana ba, Amma babu komai xanyi maganinka yanxu nan , security haka ya mike ya fara kwalawa security kira,ya Tahir ya mike yaxo gabansa yace Dan Allah uncle kayi hkr, Hajiya SA'A ma ta taso ta kamo hannunsa tace Dan Allah kayi hkr wannan abun aina gidane sai kasa mutuncinka ya xube dan Allah kayi hkr,ya fusge hannunsa yace wlh saina koyawa yarannan hankali,harni xaixo Yana fadawa magana har gida,SHikan hanaf ko ajikinsa,ya Tahir yace Dan Allah uncle kayi hkr ya Kalli hanaf Dake tsaye kikan kamar Wanda babu abinda ya aikata yace ka bashi hkr,hanaf yay shiru Bai maganaba,itama Hajiya SA'A haka ta dinga tausarsa da kyar ya hakura ,ya koma ya xauna tuni hanaf harya shiga mota,ya Tahir ya sake bawa Alhaji sunusi hkr Sannan ya fice,ya tarar da hanaf harya ta-da mota Yana shiga ya jata da mugun gudu suka fice daga gidan,ya Tahir sai fadan abinda ya aikata yake masa,...


Ya dubi ya Tahir Yana driving yace ya Tahir mutumin nan bashida mutunci idan muka kyaleshi xaidinga abinda yaga dama ne akanmu ,sbd yaga ana raga masa , ya Tahir yace Amma ai Koba komai shidin kanin mahaifin mune ya girmi wulakanci agunmu yanxu idan mamah taji abinda ka aikata wlh kasan sai Rai ranka ya Baci, yanxu da ace ya kaika station dinfa,da ya xakai dole sai mamah tasan halin da ake ciki, Hanaf yay Wani miskilin murmushi yace kasan Wani Abu wlh na masa


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login