Showing 111001 words to 114000 words out of 278032 words

Chapter 38 - JAMI'AR TSARO COMPLET by MRS SARAKIES.doc

23 Oct 2025

1045

kai ,Dan tambayar da aka masa tayi masa nauyi sosai,Amma idan Bai fada ba yasan AA Arab bazai tava kyaleshi ba,yace suna can dajin iyaka Kaduna da Abuja,AA Arab ya jinjina kai ,sai Kuma ya juyo yace yanxu idan munje kana tunanin xamu samesu, acan , zailani yace eh yallabai, AA Arab yace ka tabbatar karkasa muje kuma mu tadda sabanin haka, zailani yace wlh yallabai baxan Maka karya ba,AA Arab yace bayan nanfa akwai inda kuke xuwa, zailani yace nan ne maboyarmu,AA Arab yace shima gogan duka tare kuke dashi,idan munje xamu sameshi, kullum anan yake , zailani yace eh xaku sameshi,.,AA Arab yace duk harin da ake kaiwar nan qauyukan kuduna kune kukeyi, zailani ya qara sunkuyar da kansa, afusace AA Arab yace answer me, zailani ya ansa masa da kai,AA Arab yace da Baki xaka ansa min , zailani yace mune,AA Arab ya jinjina kai,sai Kuma yace,Ina kuke kai yaran idan kun daukesun, zailani yace amotoci ake daukarsu idan antara yadda suke bukata,sai a fitarsu daga kasar gabaki Daya, Amma wlh yallabai nidai bandani ake kaisu inda ake kaisun,AA Arab yace yanxu Ina yaran da Kuka dauka shekaran jiya, zailani yace ankaisu inda muke tarasu ,AA Arab yace xuwa yaushe kake ganin xa'a kai su inda ake kaisun,I mean suna kaiwa yaushe awurin kafin a kaisu inda ake kaisun, zailani yace suna iya kaiwa kwana biyar ko sati Daya,yadan ganta da yawansu idan sunkai yadda akeso bama sa kaiwa haka,AA Arab ya jinjina kai sai Kuma yace kunkai shekara nawa Kuna wannan ta'addancin, zailani yace ni banfi shekara biyu ba,su Kuma a yadda naji suna fada sun kai shekara goma Sha biyar,....



AA Arab ya jinjina kai sai Kuma ya mike yace shikenan,ku kunceshi ku maidashi inda yake ,daga haka ya fice daga wurin,Bayan fitar AA Arab, direct office dinsa ya koma ya dauki wayarsa ya kira DCP akan yaxo office dinsa yanasan ganin sa,cikin girmamawa DCP ya ansa masa da girmamawa,DCP Yana xaune bayan ya gama sauraran AA Arab,Dan AA Arab DCP kawai ya fadawa komai Dan shi yanxu ya dawo daga rakiyar CP tunda har Hanan ta fada masa yadda ya tauye gsky ya Dora masa ayar tambaya akansa tunda haka yake,shi yanxu ma yaso ya fahimci Wani Abu akan CP,Kuma shima xai saka masa ido sosai a kan duk Wani motsinsa, wayasanima kila yasan inda Alhaji sunusi ya kai su Rukayya tunda bakinsu Daya,hardashi xa'a hada baki ayi cin hanci da rashawa,Yana matsayin CP ,DCP ya fishi Amana, DCP ya gamsu da bayanin da AA Arab yay Masa ,sun Kuma yanke hukuncin ayau ba sai gobeba xasu fara bibiyar Alhaji sunusi, bayan sun gama tattaunawar da xasuyi suka mike suka fita daga office din, direct sashen bincike suka nufa ,bayan sun shiga ciki kowa ya hau kan computer Dan kowa da akwai abinda xaiyi,shi AA Arab da kansa ya fara tracking number Alhaji sunusi,babu Wani bata lokaci,bayan Hanan ta tura masa number Alhaji sunusi itama data karbo awayar mamah Batareda ta saniba ba,,suka sa number kan computer AA Arab ya fara tracking inda Alhaji sunusi yake,.....



CP ne tsaye acikin toilet din office dinsa ya jike sharkaf da xufa, kai kace gudun tsere yayi,waya yake da Alhaji sunusi,Wanda ke Bada oder yadda xa'a kashe masa zailani,Dan kada ya tona musu asiri,bayan ya gama sauraransa CP yace wlh yallabai,baya bari kowa ya shiga Dan dai kawai Nima Ina matsayin CP ne shiyasa na Shiga gunnan,daga shi sai wasu police biyu Wanda ya yarda dasu,da su suke kula da zailani, Alhaji sunusi cikin bacin Rai yace to kosu kasa mana suyi Maka aikin,CP ya xaro ido waje yace wlh yallabai baxai Yiwu ba,Sako Wani police Kuma na heardquater acikin wannan aikin da kasani , kasan ganganci ne asirin xai iya tonuwa aKoda yaushe,bare Kuma su masu kula dashi ,Dan bana tunanin xasuyi haka sbd sunsan halinsa, baya wasa,gashi da basira yadda baka tunani, Yana gane me laifi ko ya yake ,Alhaji yay tsaki yace nasan shi sarai tun lokacin su yallabai taju,aisaidai na bawa wasu lvr,CP yace to ka Gani,gara kawai ni xanyi da kaina ,ka barni ni nasan Tayaya xan shiga wurin, anjima xan fito sai mu hadu na karbi sakon,....



Alhaji sunusi yace nifa nafison a kashe shi ayau dinnan ma, duk da naji babban yarona yace baisan mu yake yiwa aiki ba, Amma hankal????































!
"
#
$
%
&
'
(
)
*
+
,
-
.
/
0
1
2
3
4
5
6
7
8
9
:
;
<
=
>
?
@
A
B
C
D
E
F
G
H
I
J
K
L
M
N
O
P
Q
R
S
T
U
V
W
X
Y
Z
[
\
]
^
_
`
a
b
c
d
e
f
g
h
i
j
k
l
m
n
o
p
q
r
s
t
u
v
w
x
y
z
{
|
}
~

?
i na Bai kwanta ba,CP yace karka damu xa'a Yi Hakan , Alhaji sunusi yace allura zan baka ko Kuma gubar, CP yace duka zaka Bada, gabadaya idan Daya bazai Yiwu ba,Daya xai iya yiwuwa, Alhaji sunusi ya sauke ajiyar xuciyar salama yace shikenan daga haka sukai sallama,CP ya dafe kansa, kirjinsa na bugawa duk wannan maganar da yake da Alhaji sunusi, daurewa kawai yakeyi, Amma kamar ya fashe da Kuka haka yakeji,baisan Wani tsautsayin bane yasa ya karbi tayin Alhaji sunusi ba,baisan su suke sawa ake ta wannan ta addancin ba, tsawan wannan lokacin,da Koda gangan baxai tava amincewa ba,Saida Alhaji sunusi ya kirasa suka hadu awani gidan sirrinsa Wanda Babu Wanda xaisan da maganar, bayan Alhaji sunusi ya gama fada masa komai, Wanda Babu Wanda ya taba fadawa,Saida yay shock Bai taba tunanin su Alhaji sunusi ne suke sawa ake wannan ta'addancin ba,farko Saida ya nuna Mai bazai iya ba, Amma Alhaji sunusi yay Masa barazanar kisa, tunda yaji sirrinsa Bai isa bijirewa umarnin sava,wlh badan Alhaji sunusi yace zai kashe Shiba idan Bai karbi tayin Saba ko Kuma ya tona masa asiri ba,wlh da baxai karbi wannan aikin ba,Dan masifar da zaishiga idan aka gano yasan komai ko Kuma asirinsa ya tonu , gara Alhaji sunusi ya kashe shin,haka dai ya fito daga toilet din jikinsa a Sanyaye,ga xufa ta gama wanke masa uniform dinsa ya kure AC ya xauna kan kujera dafe da kansa,.SHikan Yana tsaka Mai wuya....






07066508376________
'?Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DC2ekqRnajZAQQvErdaWfD?mode=ac_t






*_____JAMI'AR TSARO _____*




*____THE WOMEN POLICE ____*



*NA*




*_____NAJA'ATU UMAR FAROOQ _____*




*_____(MRS SARAKIES)_____*




*=?1?QUEEN OF WRITERS ASSOCIATION (QOWA) =?1?*



*Bismillahirrahmanirrahim*



________season one ep 4?? 8??



___________?&


Lateef alokacin dayaji batanda Rukayya tai baisan alokacin meya shige Shiba,bakin ciki zaiyi ko farin ciki, ma'anar farin cikin sa shine ZA'A banxatar da Shari'ar, xa'a dakata da Shari'a,bakin cikin sa Kuma andauke Rukayya matar auransa wacce yake muradin yin rayuwar aure da ita na har abada, Allah ya Gani Yana masifar San Rukayya tsakani da Allah,ko wannan qarar tashi da tai maimakon yaji tsanarta saima Wani sabon sannata dayaji ya qara mamaye masa xuciya,baisan Alhaji sunusi shiyasa adauke Rukayya ba ,domin agabansa Alhaji sunusi shima ya nuna alhini da damuwar sa na sacetan da akayi, Hajiya SA'A itama Batasan Alhaji sunusi shiya sace ruky ba har yau, Dan Koda wasa Bai fada musu ba, Amma Kuma taji dadi da taji ansace Rukayya koba komai ai ta Raba lateef da ita da yake masifar Santa, Dan tunda tai qarar lateef ta qara Jin tsanarta aranta,Alhaji sunusi nuna musu yay shi bashiya sace Rukayya ba, lateef kuwa bore yahauyi akan wlh saiya Nemo duk inda Rukayya take matar da xai Aura nan da Yan kwanaki ita xa'a sace masa ita ,wlh baxai yadda ba, saiya nemota da kansa,Hajiya SA'A tayi kan lateef da fada tana waya sanima ko saurayi tabi, yarinyar da idonta abude yake kai lateef me xakayi da ita,da har xakabi ka samu kanka Dan ta bata,duk Yan mata garin Kaduna ,da Wanda a nake kokarin hadaka dasu yayan kawayena Bandama masu kawo kansu suce suna sanka,Amma Dan Rashin sanin ciwonkai ka nacewa mace daya, macenma wacce idanta yake abude,duk San kan lateef yace ya fasa auran ruky yaji tsanarta aransa yasa ta fadi haka,....



Lateef kuwa nunawa yay cewa ruky bazatai haka ba, Dan yasan wacce ita yarinya ce Mai tarbiya,da kamun kai baxa taba aikata haka ba, Hajiya SA'A tai tai lateef ya fahimci abinda takesan fahimtar dashi Amma ya nuna shi Sam Rukayya yakeso har gobe, domin akanta ya fara so Kuma akanta xai kare,Kuma wlh saiya fita Nemanta duk inda take da kansa,Koda ko Hakan na nufin xai rasa ransa ne,Alhaji sunusi ganin lateef ya birkice Musa,bai shirya rasa lateef ba ,Hakan yasa yace da Hajiya SA'A ta kyaleshi,shi xai nemowa lateef Rukayya da kansa ya kwantar da hankalinsa,da Kyar ya samu ya lallashi lateef,ya hkr , Hajiya SA'A Dan bakin ciki tashi tai ta fita daga falon,fuuuu, lateef Shima ya bar falon kamar xai tashi sama,Alhaji sunusi shima mikewa yay shige dakinsa ya sauke ajiyar xuciya , sai Kuma ya fara xagaye dakin lateef ne kadai matsalarsa, Amma shima yasan ta yadda xai bullo masa,....



Ya fesar da numfashi,sai Kuma ya daga kansa sama alamar tunani,yanxu badan Allah yasa yay wannan dabarar ta dauke Rukayya da yay ba,aida tuni lateef ankusa kaishi gidan yari,koma ankaishin, badan barrister Salman ya fada masa cewa lateef shiya fada masa da bakinsa cewa shi ya ketawa yarinyar da ake tuhumarsa akan ya keta mata haddiba ,aida baxai taba saniba,da tuni Yana ganin lateef bamai laifi bane Saidai yaji an yanke masa hukuncin xaman gidan yari,ko Kuma daurin Rai da Rai Allah ya Gani Yana matukar masifar San lateef,baxai taba barin Wani Abu na cutarwa ya sameshiba matukar Yana raye,.....



Bayan yaje yaywa Hajiya Halima Jaje shine yasa suje suyiwa mamah jaje Dan kada ta xargi Wani Abu, Hajiya SA'A Basu Samu damar xuwa ba sai da akai kwana uku da batan Rukayya,da ita da lateef sukaje sai driver,mamah Bata nuna musu komai ba,ta tarbesu kamar yadda take karbar kowa, Hajiya SA'A ta danjima agidan sannan ta tafi,bayan ta fita harabar gidan,ta samu lateef xaune kan kujerar aharabar gidan ya Wani takure waje Daya,Dan tunda ya shigo ya gaida su mamah dayi mata Jaje ya fita compound din gidan , Hajiya SA'A data fito ta ganshi yayi Wani tagumi kamar wacce wata uwarsa aka sace, yasa ta saki tsaki qasa qasa ,bayan ta isa gunsa Hajiya SA'A tace tashi mutafi kaxo ka wani takure kamar Wani marayan da bashida gata,ta fada tana Maka masa harara,lateef baice komai ba,ya mike fuskarsa a murtuke yay hanyar gate suka fita daga gidan gabadaya, Hajiya SA'A takaici ya cikata kamar ta makeshi,.....




?& Agidan su ruky kuwa,yau kwana hudu da batan Rukayya,mijin anty mufeeda yaxo daxu da safe ,daga Abuja dan jiya ya sauka a qasar cikin dare,mamah duk ta rame tayi Baki,yanxu haka ma kwance take Batada lpy, ya hanaf ya kira doc Khalid abokinsa ,Dan yazo ya duba ta,yanxu haka mamah tana dakinta Dake upstairs,akan gado akwance ta lulluba da duvet anty mufeeda ce agefenta , fuskarta da damuwa sosai itama duk ta fada kwana biyun nan,sai maman Shareef,anty mufeeda tai kasa da murya cikin tausayin halin da mamah take ciki wacce idanta ke lumshe tace mamah ki tashi ko tea ne Kisha kafin doc ya shigo Kinga fa tun jiya Bakici komai ba,maman Shareef tace cikin kwantar da murya Halima ki tashi Kisha Kinga ko doc yaxo dole saikinci Wani abun sannan xaiyi treatment dinki,kafin mamah tayi magana doc Khalid yaxo Wanda abokin Yaya hanaf ne Dan kamar Dan gida yake,shima yaji Batan da ruky tai har gida yaxo yayiwa mamah jaje, ....



Doc Khalid ya tsaya abakin kofa da sallama abakinsa,aka Basu ixnin shigowa,bayan ya hanaf ya masa jagora ,duk suka ansa sallamarsa tareda Yi masa barka da xuwa,ya risina ya gaida maman Shareef da anty mufeeda da tambayar su Mai Jiki,suka ansa masa da kulawa,yay wa mamah sannu da Jiki, sannan ya fara treatment dinta,bayan yay mata Komai ya gwada bp ta yaga ya hau sosai,Dan haka ya cire air peace din yace mamah sannu da Jiki, Allah ya qara lpy,Amma jininki ya hau sosai yadda ba'a so,mamah saikin Dan rage damuwar sosai tukunna, jininki zai sauka,yace zan rubuta miki magun guna in Sha Allah idan kinasha Kuma kina cire Damuwa aranki kova duka ba xakiji sauki da yardar Allah,ya Kalli anty mufeeda yace taci abinci kuwa xan Saka mata kanula ne, jikin ta naga akwai zazzabi atare da ita,maman Shareef tace a'a bataci ba bari a Bata ,doc Khalid yace shikenan bari ya jirata a falor daga haka ya fita daga dakin,....



Da kyar mamah ta iya Shan shayin nan Dan gabadaya Batada apartite a Bakinta, Dan yanxu hakama Wani mugun xaxxabine ajikinta,bayan ta Tasha Wanda zata iya Sha tace ya isheta, suka kyaleta haka, mufeeda ta mike Dan kiran doc Khalid,bayan doc Khalid ya shigo,ya sawa mamah kanula sannan ya bawa anty mufeeda tai mata allurarorin da xatai mata , sannan ta cire mata ruwan idan ya qare Dan itama nurse ce,babu musu anty mufeeda tace xatai mata in Sha Allah,haka doc Khalid yay musu sallama ya Fita,bayan yaywa mamah addu'ar samun lpy,bayan fitar doc Khalid anty mufeeda taiwa mamah allurarorin da xa'a mata, babu dadewa Kuma bacci Mai nauyi yay awan gaba da ita Wanda xai dauketa awowi tanayi,Dan samun ta huta daga tunanin da take Yi,Dan hadda Rashin baccin ma ya qara sawa jinin nata ya hau bayan damuwar da take ciki,Dan dama tunda wannan abun ya faru Bata rintsa ba,har yau kwana hudu, kullum tana kan sallaya tana Mika kukunta xuwa ga Allah,..



Ganin ta samu bacci yasa maman Shareef tace bari ta fita Dan barinta ta huta,ta fita daga dakin,anty mufeeda ta gyarawa maman kwanciyar ta ,Dan kada ta goce kanula sannan itama ta fita daga dakin Dan barin maman ta huta,mimie da moha suna wajen dadynsu Dan tunda yaxo suka makale masa ,bayan ta sauka qasa ta tarar da Yan jaje sunxo maman Shareef na tare dasu ,idan sun tambayi mamah tace bacci takeyi,baba asabe baiwar Allah itama duk ta rame Dan wlh Allah ya Gani Rukayya kamar yar cikinta haka ta dauketa,kamar yadda itama Ruky ta dauketa tamkar babarta, mamah ko kamar kanwarta haka ta dauki baba hasiya,kamar yadda itama baba hasiya ta dauki mamah tamkar yayarta wacce suka fito ciki Daya,.......



___________?&


Da yamma saiga Alhaji sunusi Dan Rashin kunya yaxo gidan wai yiwa mamah jaje,Dan kawai kada su xargi Wani Abun, saidai Vai samu mamah ba sai maman Shareef da anty mufeeda, baba hasiya tana kitchen,bayan ya shigo da sallama, suka ansa masa ,ya samu waje kan kujera ya xauna,ya gaida maman Shareef,maman Shareef ta ansa masa cikin sakin fuska,anty mufeeda ta gaidashi ya ansa mata harda Dan mata wasa ,anty mufeeda murmushi kawai tai, Amma batace komai ba,Alhaji sunusi yace cikin alhini, Hajiya Maryam ( maman Shareef kenan)har yanxu shiru ko babu labarin ta,maman Shareef tace wlh haryanxu shiru ko lvr babu,Alhaji sunusi yace cikin alhini wlh Nima ta bangarena inayin iya bakin kokarina Amma shiru banji komai ba,.Kuma nasa ayi bincike sosai..



Maman Shareef tace to ya ZA'Ayi,mu damuwar Rashin sanin inda take,da munyi tunanin ko masu garkuwa da mutanene suka dauke ta,muke ta xuba idan muga sun kira,mundauka xasu kira awaya su bukaci kudi,ko Wani Abun,Amma shiru shiyasa muka cire Rai dasu din,Amma babu komai Allah Yana tareda mu, kullum muna kan sallaya muna addu'a Allah ya tona asirin Wanda suka dauke tan, Allah karya Basu damar cutar da ita, aduk inda take muna addu'ar Allah ya kubutar da ita,Alhaji sunusi yace Ameen dai muma addu'ar nan kullum muna yinta,har kudi na bawa Wani malamin almajirai akan ya Taya mu da addu'ar Allah yasa aganta,anty mufeeda suka ansa da Ameen,yace bari naje duk yadda ake ciki Dan Allah adinga sanar min ,idan Hajiya Halima ta farka kuce naxo ,maman Shareef tace in Sha Allah,ya ajiye musu damun kudi, yace ga wannan babu yawa Allah ya bayyana ta,maman Shareef tai masa godiya,Yana kokarin mikewa su moha suka shigo falon da gudu suka fada kan anty mufeeda, suna kyalkyala dariya,anty mufeeda ta Dan musu tsawa tace meya Hakan,kuka shigo da gudu babu sallama ban hanakuba,moha sarkin kuka take ya Bata Rai ya saki Kukan baci, Alhaji sunusi yay murmushi yace ko jikokin namu ne mufeeda,, anty mufeeda tai murmushi tace sune uncle,yace yaku kuxo na ganku,moha ya makale kafada yaki xuwa,mimie ce kawai taje ,Alhaji sunusi ya kama hannun ta yace nasamu mata kinga shikenan saina tafi Dake koh, mimie ta kwace hannunta to koma wajen mamanta , Alhaji sunusi yay murmushi yace bakya so na kenan Kona miki tsufa aishikenan,ya xaro kudi ya Basu Basu karba ba , ya ajiyewa anty mufeeda a gabanta yay musu sallama ya fita,......



Abangaren su AA Arab kuwa aranar sun samu location din inda Alhaji sunusi yake, Amma saidai Yana cikin garin Kaduna Yana ma gidansa,Dan haka atake AA Arab ya sanar da jami'an daya sa su dinga bibiyar Alhaji sunusi, location din,yace su fara bibiyar sa Daga yanxu, suka,ansa masa cikin girmamawa,bayan sun fito kowa ya shige office dinsa,AA Arab Yana komawa office dinsa yasa wayar Rukayya a charging,Dan Yana so ya dinga ganinta a kunne ko akwai Wani Abu Wanda xai haska musu bincikensu,ko xa'a iya Kiranta,....



Ya Jima Yana mamakin Alhaji sunusi,har hotunansa yasa aturo masa,Saida ya ganshi ya ganeshi,oh aiyasan shi lokacin su yallabai taju,ai yaron su yallabai taju ne, lallai ya yarda xai aikata fiye da hakama tunda rainon su yallabai taju ne da baxai taba mantusa, yayi mamaki kwarai dayaji qanin AIG umar MaiTama ne,Dan baisan Baban Rukayya bane Saida ya karanta sunan,akan wannan case din daya faru na sacetan nan da akayi,AIG umar MaiTama mutumin kirki ne sosai,gashi jajirtaccen jami'i ne,Wanda baya wasa da aikinsa,lokaci Daya yaji rasuwarsa, rasuwarsa ta bigeshi sosai Dan alokacin boss din sune Allah dai ya jikan Maza,in Sha Allah baxai taba barin xuri'arsa suyi kuka ba in Sha Allah sai qara tsayawa tsayin daka wajen ganin ansaki inda Rukayya take, akwai Wani abun kyauta tawa Daya masa Wanda bazai tava mantawa ba,daga haka ya sauke numfashi ya cigaba aikin Daya rage masa,.....





07066508476________
'?Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DC2ekqRnajZAQQvErdaWfD?mode=ac_t





*____JAMI'AR TSARO____*



*____THE WOMEN POLICE ____*



*NA*




*____NAJA'ATU UMAR FAROOQ ____*



*____(MRS SARAKIES)____*




*=?1?QUEEN OF WRITERS ASSOCIATION (QOWA) =?1?*



*Bismillahirrahmanirrahim*



_______season one ep 4?? 9??



____________?&



_______*ZAR'IA*_______


Agidansu Ameenah kuwa tun ranar da malam Auwalu ya hana ummah xuwa gidan Ameenah, bayan haka Bai tsaya nanba ya hadata da yayanta har yaxo ya disgata gahan kishiyarta,bata qara sakar masa fuska ba, bayan kwana biyu dai ta aika Nana gidan danta gano mata Ameenah,da kayan abinci da Dan kayan makulashe,Kuma malam Auwalu


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login