Showing 12001 words to 15000 words out of 278032 words

Chapter 5 - JAMI'AR TSARO COMPLET by MRS SARAKIES.doc

23 Oct 2025

1076

kira tace baba bari mutafi Allah ya qara lpy,....

Baba lami ta kalli wannan uban kaya da ruky ta Siyo musu ga abinci shima Wanda Bata tava Ganin irinsu ba Dan abincin restaurant ne Irin me Rai da lpyr nan ga pure water shima Leda Leda,haka ta hau Yuma ruky godiya tareda Yi mata addu'ar gamawa da duniya lpy,harma da iyayenta, harda hawayenta, inda ruky tace baba Dan Allah kedena yimin godiya,babu godiya tsakanin mu,ta kalli shafa wacce take bacci ,harta Dan fara canzawa, Tace bari muje Allah ya sawake saina dawo gobe in Sha Allah,baba lami tace ki gaida mahaifiyar ki,tai murmushi tace xataji in Sha Allah,haka ta fito baba lami xata Rakasu ta dakatar da ita, haka suka tafi inda ruky tai parking suka shiga mota,tana shiga Khalil yace ranki dade sannu da qoqari ya fada Yana murmushi, ruky ta Maida masa da martanin murmushin tace sannu malam Khalil,ai kai xanma sannu yadda ka taimaka min harnaxo ma bayin Allah nan babu abinda xance Maka saidai Allah ya Saka da Alkhairi,yayi ajiyar xuciya yace ranki dade,dolene na Baki dukkan Wani goyan baya da kike bukata daga gareni , tunda har xaki taimakawa bayin Allah nan,keba yar Siyasa ba,ba wata yar kasuwa ba,ba Kuma IG ko commissioner ba, Amma matsayinki na JAMI'AR TSARO daga Jin koken baiwar Allah nan haka kika xo domin ki taimaka masu, ai wannan ba qaramin kokari kike ba,duk da nasan baza a rasa Wanda sukaji hirar nanba Koda koh acikin manyan mutanen qasar nan ne,ni mezaisa bazan Bada goyan baya ba ,da duk abinda kike soba,wlh ranki dade Saida mukaxo gurin matar nan abin ya qara bani tausayi naga xan iya komai akai,nidai ranki wlh indai goyan baya kike nema ga gudunmawar da kike ganin xan iya bayarwa wlh xan Bada ,ki tinkareni kanki tsaye,


ruky ta sauke ajiyar xuciya, tace nagode sosai malam Khalil, samun irinki arayuwa Yana da wahalar samu ,Nima badan kaidin ba da bansan Ina xan samesu ba, Amma yadda naxo na fada Maka bukata ta,ka karba Batare da ka bani wahala ba, sannan na taso ka bansani ba ko kana da Wani uxurin,Amma ahaka ka ansa min kataho,wannan kadai ya tabbatar min da kai mutumin kirki ne, nagode sosai, yanxu abinda nakeso da kai shine kada kowa ya San muna wannan aikin dagani sai kai domin inaso komai ya xamto cikin sirri har sai munxo Gabar da nakeso asanin tukunna, Khalil yace in Sha Allah ranki dade,babu maiji, ta kalleshi at the same time tai dariya har hakoranta na bayyana masu kyau da haske,tace kadaina cemin ranki dade kafadi sunana kanka tsaye mana, ta qarasa fada cikin yar shagwaba da Batasan tayiba, ya Allah ibrahim Khalil yace aransa Yana ganin wannan kyakkyawar halittar tana masa shagawaba, Yana cewa ita wannan matar komai ma kyau yake mata,afili Kuma yace ki gafarceni wlh baxan iyaba ,sbd girmankine ai domin Allah ne ya Baki,ya qarasa fada cikin bar kwancinsa,tai murmushi again tace nidai gsky yamin girma yace nikuma Amin afuwa ,ta qara sakin Wani murmushin tace kaidaiko,yayi mata salute sai kawai ta girgixa kai ta ta-da motar tareda yin reverse ta nufi get din haka aka Bude musu suka wuce ,suna tafiya ahanya tana Dan tambayar Khalil wasu abubuwan hardai sukaxo unguwar su inda yace ta ajiyeshi a inda ta daukeshi daxu , batai musuba ta saukeshi inda tai masa godiya shima yay mata , haka kama hanyar MALALI ganin 4 Saura,....


Ibrahim Khalil Yana sauka daga motar Saida yaga tafiyar ruky ta bacewa ganinsa sannan ya wuce Yana Mai qara ,boye recording din da yayi Dan wlh shima indai ruky xata tsayawa matar nan da 'yar ta wajen kwato musu yancinsu shima in Sha Allah a shirye yake Dan ya Bada kowane Irin tai makone, Dan wannan Abu yayi Muni da yawa wannan wanne axxaluminne yayi wannan aika Aikan saikace babu xuciyar imani ajikinsa haka ya qarasa gida Yana Mai yiwa Ruky addu'ar dacewa a dukkan abinda tasa agaba,.....

Rujy tana xuwa gida ta nufi cikin falon bayan tayi parking motarta, tana shiga Bata samu kowa a falon ba da dukan alamu mamah tana dakinta xatai sallah, itama baba hasiya kila haka,batai wata wataba ta haura sama xuwa dakin ta jikinta duk gajiya , Hakan yasa tai sauri ta cire hijab din jikinta ta fara rage kayan jikinta ta daura towel,ta wuce toilet tana shiga ta tara ruwa tai wanka a cikin jacuzzi,bayan ta gama ta dauro alwala,ta fito,tana digar ruwa tana maijin dadin jikinta,haka Dan goge ruwan jikinnata da qaramin towel ta hau shafa lotion dinta,bayan ta gama ta dauka riga da Wando marasa kauri sosai tasa ta dauki hijab dinta ta tada sallah dan batai ko xuhur ba bare Kuma ASR,tana addu'ar Allah ya yafe mata,bayan ta idar tayi azkar kamar yadda mamah ta sabar musu sannan ta cire hijab din, ta Saka white nety cap wacce ta rufe mata gashinta ,haka ta shiga dakin mamah Dake kusa nata,tana budawa Bata ganta ba ta qarasa shiga ciki ta duba ko Ina Bata gantaba ganin Bata nan yasa ta saukowa kasa rike da wayar ta,tana sauka taga mamah da ya hanaf Dake operating system a dining,at the same time Kuma suna mgn da mamah ,mamah tace a'a Auta yaushe kika dawo, ta danji sanyi aranta ganin mamah ta yadda da inda ta fada mata xata,tai murmushi tace mamah dazu na dawo ,banganki a falor ba ,sainaga Kuma time din sallah yayi shiyasa nace kila kinje sallah ne,ta qarasa fada tana Mai zama a kusa da mamah ,

mamah ta kama duka hannunta biyun da nata tahada kamar wata karamar yarinya tana kallan ta,tace yanaga idan ki kamar da alamun gjy Auta,Saida gaban Ruky ya fadi Dan mamah akwaita da lura, saikuma ta basar tace mamah bacci nake ji shiyasa Kuma da naje Hanan Bata bari na hutaba,wai hira xamuyi,mamah tace ya jikin Hanan din, ruky tace da sauki tana gaidake ita da mamansu,mamah tace Ayya Allah ya qara lpy,Nima Ina ansawa,mamah tace abinci fa, Ruky tace naci agidansu Hanan Dan kada mamah ta harbo jirginta, ya hanaf yace Hi ,ta juya tace hello, ta mike Dan ta isa gunsa bataso mamah ta qara jangalo Wani abun, kafin ta qaraso ya tura system din gabansa gefe ya Mike yayi saluting nata yace the women police ,tai yar dariya tareda da rufe fuskarta tace kai ya hanaf, ya wara manyan idansa Irin nata yace ba dole naba Ina tareda officer agida ace bana girma mata aisaikisa azo a kamani ,ta qarasa dining taja kujerar Dake passing dinsa ta xauna sannan tace nidai Yaya banaso yace ni Kuma inso,tai murmushi tace me kake haka tana leka laptop in ,yace Aiki nake,mamah dai kallansu take tana murmushi ,aranta tana musu addu'ar tsari a duk Inda suke,....


*Hayin rigasa gidan Ameenah da Kabiru*

Bantashi daga baccin nan ba sai dab da magrib shima Ina tashi nai sauri nai sallan ASR sannan nai magrib Ina Jin jiri Ina komai ,Ina idarwa na dinga Jin jikina Yana min ciwo ga goshi na yadda yay suntum sbd kumbura Kuma har lokacin kaina Bai daina ciwo ba kawai dai raguwa yayi ,

Ina nan xaune ina tunanin makomata yadda ni bani da Wani yancin arayuwa ta babana Bai San Wani Hali nake ciki ba wlh da baxai dage ba akan na dawo gidan kabiru ba,Ina nan xaune ina tunani har lokacin sallan isha'i yayi haka na tashi nai sallan ,na Dade Ina addu'a akan Allah ya Ganar da mahaifina halin da nake ciki tunda ni bawai taba xama yay Dani ba yaji halin da nake ciki da kabiru ba ko Kuma yay bincike ba,bayan na idar na Dade axaune kafin naji yunwa ta dameni gashi banida ko kwayar abinci agidan bare na tashi na dafa , Amma sbd xalinci Kabiru Bai bani abinciba,Wanda aka kawomin dinma haka ya tattara ya tafi dashi Kuma nasan xuwa xaiyi ya sayar,bansan lokacin da hawaye ya xubomin ba Dana tuna bansan ma taya ummah ta hada wannan kayan abuncinma ta Aiko min dashi,wai duk Dan sbd karna naimi abinda xanci tai Hakan ,Ina xaune har lokacin kusan shadaya da Rabi nasan Kabiru tunda ya kai wannan lokacin badawa xaiyi gidannan ba ,haka tashi ganin yunwa xata halakani na tafi wajen randa ta na dinga shan ruwa wai ko zan daina Jin yinwan, haka na dinga shan ruwan nan har Saida cikina ya kulle na dinga kela amai kamar 'ya'yan hanjin cikinta zan amayo sbd babu komai acikina baba abinda nake anayarwa sai ruwa,bayan na gama nai kokarin tashi naje na kwanta Amma Ina tashi da Wani jiri ya debeni bansan na koma na kwanta ba,sbd yunwar da nakeji idona har Wani dishi dishi nake Gani,ni sainaji ciwan ma qaruwa yake kodan hadda yunwa ma ,wlh ina nan axaune bansan tsawan lokacin Dana dauka ,awurin nan ba ,da rar rafe na Koma daki na hau kangadona,sai bacci barawo ne ya saceni,....




07066508376________
'?Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DC2ekqRnajZAQQvErdaWfD


*____JAMI'AR TSARO____*

*_____THE WOMEN POLICE____*


_____THIS STORY IS TOUCHING HEART, I WAS SPEECHLESS TO EXPLAIN IT, BUT, WE SHOULD ON WHAT HAPPENED TO OUR LIFE KNOW, SO, BE WITH ME U LOVE IT MORE THAN U EXPECTED _______
'?


*NA*


*______NAJA'ATU UMAR FAROOQ_____*


*______(MRS SARAKIES)______*


*=?1?QUEEN OF WRITERS ASSOCIATION(QUWA)*=?1?


*Bismillahirrahmanirrahim*


_____season one ep 8??


________
'?
'?
Washe gari haka ruky ta tashi ta dinga tunanin yau Kuma wacce qaryar xatayi ta cewa mamah xata fita Dan tunjiya da tunanin Hakan ta kwana,jiya tacewa mamah xataje gidan su Hanan dubata,Kuma taje yauma Kuma tace xata, Amma Kuma ai ita idan tana jinya Hanan ta dinga sintirin xuwa dubata kenan harsai ta samu sauki, to itama haka xatai inyaso idan mamah ta tambayeta meyasa take fita xata fake da Bata wannan ansar,da wannan tunanin da kwarin gwaiwar ta cigaba da harkoninta kafin anjima ta shirya ta fita Dan kada ta fita da wuri mamah tace yayi wuri,Dan in taje da sassafe ma ba lallai Dr yaxo ba,Ina xaune a daki Khalil ya kirani inda yace min yaje asibitin ya Dubamu su baba lami , tana tare da shafa Kuma jikin nata babu laifi akwai Dan sauki Amma na bahaushe, tunda ai ba'a je ga ganin Dr ba, Amma dai nurses dinma suna iya bakin kokarinsu...

Inda yace Dr baxai xoba sai da yamma, Dan haka ba saitaxo ba ta bari da yamman saita xo, haka taima Khalil godiya inda yace mata babu komai ,

Wajen karfe 12:20pm, Ruky tana kitchen tana girki itada hasiya, baba hasiya sai hira take mata,inda mamah ta kwala mata kira ta wanke hannunta ta fito ta qaraso kusa da mamah Dake zaune falor tana Shan fruits, tace mamah Gani,mamah tace auta dauko min wayata a sama a bedroom Dina na kira mufeeda,haka ta haura sama ta dauko mata wayar,inda mamah tace jeki cigaba da aikin ki,tace mamah Dan Allah idan kungaisa ki Kirani Nima mugaisa ta fada da yar shagwaba Irin ta Auta, mamah tace meye anfanin wayarki ,tace mamah tana nan mana kawai dai ni da wayarki nakeso mugaisa adai dai lokacin da aka daga wayar mamah tace jeki naji haka ta wuce kitchen,mamah Kuma ta daga wayar daga Daya bangaren mufeeda tace mamah bari na kashe na kiraki ,daga haka ta kashe wayar,dama mamah tasan baxa ta tava bari suyi waya da kudinta ba,Aiko tana cikin wannan tunanin Kiran ya shigo inda mamah taga ,daga Daya bangaren mufeeda tace mamah Ina wuni ,mamah tace lpy lau mufeeda tace yasu Hanaf da Auta,mamah tace suna lpy,yasu takwara , mufeeda tace lpynsu lau mamah, mamah tace dama na kira na fada miki ne ki kira Hajiya halima ki Mata gaisuwan kaninta Daya rasu,Kinga mu munje tunda ke baki samu dama ba ya kamata ki kirata ki Mata gaisuwan, mufeeda tace in Sha Allah mamah xamkirata,mamah tace yauwa dama shine Kiran ,Kuma naji lpynku to alhamdulillah,...

Mufeeda tace toh mamah na gode sosai, Allah ya qara girma,mamah ta ansa da Ameen, mufeeda tace idan Auta tana nan ki Bata mugaisa nasan yau weekend tana gida tana wannan baccin nata,mamah tace to tana Kiran Ruky, ruky ta fito da murmushi ganin mamah na Mika mata wayar alamar kira yasata kar ba da sauri ganin sunan Mai kiran yasata fadada murmushin nata,ta karba tana xama kusa da da mamah,tace aunty mufeeda Ina wuni,daga Daya bangaren mufeeda tace lpy lau autan mamah ykk ya aiki, cikin murmushin ta Mai kyau tace lpy lau anty ,yasu mimie,anty mufeeda tace lpynsu lau,kullum sai an tamyeki kullum su burinsu akawosu gidan mamah wajen anty , ruky tai murmushi tace Dan Allah Anty ki kawosu idan akai hutu mana, mufeeda tace in Sha Allah Auta xa'a kawosu suka Dan tava hira Irin na Yan uwa sannan sukai sallama,....

Ruky ta xauna kusa da mamah bayan ta Bata wayar tace mamah Dan Allah anjima da yamma xanje na qara duba Hanan, mamah har zatace a'a saikuma ta tuno itama Hanan haka take zarya indai har ruky ce ba lpy Dan haka itama baxata hanata ba ,mamah tace shikenan Allah ya kaimu, Ruky ta ansa da Ameen cikin farin ciki , tace mamah bari na qarasa girkin,mamah tace kikedai Taya wa Dan nasan hasiya ce dai maiyi, ruky ta turo Baki tace wlh mamah nima Inayi kitambayi baba hasiya ta fada tanayin hanyar kitchen din, baba hasiya ta leko tace ita takeyi Hajiya, mamah ta tabe Baki tace xamuci jagwal gwalo kenan, ruky ta dawo falon ta kalli mamah ta turo Baki gaba ta fara bubbuga qafa tana mamah hakama zakice,mamah tana dariya tace yo aiba karya naiba nidai bantaba cin girkin kiba,tace to wlh mamah xakiyi mamaki barima kiga na gama Dan har Hanan ma nake dafawa abin dubiya Kuma saikinci,mamah tai murmushinta Irin na ruky tace ,nidai baxan Civa ruky tai hanyar kitchen Jin baba hasiya na Kiranta tana Aiko mamah saikinci,mamah dai dariya take,....

Haka ruky ta girkawa su baba shafa farfesun naman rago da Kuma lafiyayyar jollef rice,wacce Tasha hanta ,bayan sun kammala baba lami takai dining,itama ruky ta Saka Wanda taiwa su baba lami a basket sannan ta fito ta haye sama Dan xafi takeji tai wanka bayan ta fito tai sallah bayan ta Tashafa lotion dinta sannan ta Saka riga da sket Marasa nauyi sannan ta Saka hula ta sauko kasa,ta tadda Mamah a dining tana cin abinci itama tai joining nata,sannan ta Buda Wanda ta Dafama su baba lami, dama ta xuba musu Dan suci,bayan ta xuba ta dire plate din a gaban mamah, mamah ta dago ta dubeta,ruky tai murmushi tace mamah gashi kici ba yadda ta iya mamah ta dauki spoon din da take cin abinci ta debi kadan ta kai Baki,....
Ruky ta tsaya kallan mamah ganin ta qara deban Wani Wanda yafi waccan na farko ta qara kaiwa Baki,Mamah tace wayay girkin nan Ruky taiwa mamah fari da Ido tace nice mana,mamah tai murmushi tace
Hasiya ce tayi, nasan ita ta girka miki,ta fada tana ture Wanda ta fara xuba din tana qara cin Wanda ruky ta girkawa su baba lami, ruky ta kwalawa baba hasiya kira da dakinta ke kasa ,baba hasiya ta fito tace uwata Gani,.


Ruky tace Kiji mamah wai bani nai girkin nan ba Wanda naiwa Hanan, hasiya tana dariya tace Hajiya ita tai mana,mamah ta qara kaiwa Wani bakin ta tace hasiya so kike kawai kiyi qarya sbd me sunan babarkici , ruky tai dariya har hakoranta na bayyana tace baba hasiya kawomin filo nasa a bayan mamah karta fadi sbd Santi, mamah tace a'a gado xa'a kawo min ba filo, baba hasiya dariya tai tace Hajiya gsky fa uwata ta fada,mamah tace oh harda ke hasiya niba santi nai ba mamaki nai, lallai Auta ta ta zama 'yan mata sai aure ruky ta rufe fuskarta alamar kunya xata bar wajen mamah ta riketa tana dariya ta zaunar ta kan cinyarta,tana Ina xaki Auta GSKy Abinci yayi Dadi saina ajewa hanaf dan shima ya shaida,cewa Auta ta ta iya girki,ruky ta Bude fuskarta ta kalli mamah tace kin manta na iya a police academy wudil,babu Wanda yakeman girki ni nakeyi ,Rana dedene Hanan take mana ,mamah tace na yadda ai tunda nidai yanxu gashi naci, Ruky tai dariya ta kifa kanta akan kirjin mamah kamar wata qaramar yarinya,mamah tace oya tashi kici abincin kema Kona Baki a Baki,ta sauka daga kan cinyar mamah ta koma inda ta tashi,tai serving in kanta, daga haka baba hasiya ta koma dakinta tana dariya, ruky tafara ci,tace mamah karki fadawa ya hanaf cewa ninai har sai ya cinye sannan, mamah tace ni nasan dai Mai zan Masa,mamah ta rigata tashi ta wuce dakinta Dan ta kwanta ta huta before ars prayer,bayan ruky ta gama cin abincin ta wuce sama itama ta danta huta before yamma tayi ta tafi asibitin,...

Da yamma haka ruky ta fito cikin shigarta as usual na farin hijab har qasa ,bayan tasa riga da Wando daga ciki,tasa face mask ta fito ,ta sauko qasa sanin mamah tana qasa,ta wuce kitchen ta dauki abincin sannan ta fito taiwa Mamah sallama da baba hasiya, sukace ayima Hanan sannu ruky ta ansa da xataji,ta fito ta shiga mota, tana tafiya a hanya ta kira Khalil tace gatanan xuwa ,ya ansa mata da saita qaraso cikin girmamawa,bayan ta isa asibitin direct dakin da aka kwantar da shafa ta wuce ,haka ta Tarar da baba lami xaune kan sallaya ta shiga bakinta dauke da sallama, baba lami ta ansa mata tana juyowa xuwa gareta, cikin murmushi ta qarasa har gaban gadon shafa inda ta ajije abincin ta gaida baba lami,baba lami ta ansaata cikin girmamawa inda take tambayar ta mamanta, Ruky tace lpyanta lau tana ma gaidata da maijiki, baba lami tace Ina ansawa,...

Tace baba ga abinci nan abawa shafa taci inta tashi Dan bacci take,svd in Sha Allah xai taimaka wajen jin dadin jikinta,baba lami ta hau mata godiya tace jami'a a asibitin mafa ana babu abinci Koda yaushe basai kina wahalar da kankiba, ruky tai murmushi tace wannan ma daban yake,baba lami tace angode jami'a Allah ya Saka da Alkhairi, yayi miki albarka, ruky ta ansa da Ameen,tace nurses in ko suna shigowa baba,baba lami


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login