Showing 6001 words to 9000 words out of 278032 words

Chapter 3 - JAMI'AR TSARO COMPLET by MRS SARAKIES.doc

23 Oct 2025

1075

kanku damu ba ,mufa matane kufa maxa ne,yace inama Nima macace wlh da baxan dinga fitowa da wuriba,sbd ana daga muku kafa,tace to saikuma aka yika ana miji, xaiyi mgn ta rigashi tace yauwa Shareef ya maganar wannan case din kunje kwa danni jiyanna Raina a bace yake shiyasa ban ma tsaya ba nace sai washe gari,yace wlh DCP yace saidai xuwa gobe tukunna xa muje unguwar Muje ayi bincike,tace hmmm aishikenan,....

Amma babu Dadi a tsare mutane sannan akiyin bincike da wuri ,ni xansamu DCP din inyaso muje abinciko case din, Shareef yayi murmushi yace aidama indai kikai magana ai DCP bazai musaba,danke din ta musanman ce ,ya fada da sigar tsokana ta rarumo Wani book xata Maka masa ya kauce ya fice Yana dariya,ita Kuma tai murmushi ta jawo laptop dinta ta fara tafawa,...

Domin Shareef tare sukai police academy wudil,Kuma Dan uwantane domin Dan gidan yayar mamah ne,yanxu haka star
Tunanin ta ya katsene lokacin da Kiran wayarta ,kawarta Hanan ya ratso wayar ta ,inda ta dauka ,daga daya bangaren Hanan tace ASP ykk ,ruky tai murmushi tace lpy lau ASP to the first lady,Hanan tace hmm kedai bari wlh kinganmu yanxu nan muka dawo daga Abuja saukar mu a jirgi kenan mun raka first lady, ruky tace lallai Kuna Jin Dadi, Hanan tai kasa da murya yadda babu Wanda zaijita , ta ya Mutsa fuska tace Wani Dadi kullum kai kenan kana tafe saikace wasu bayi aike gara ke kullum kina zauna wuri Daya indai ba Wani case ne ya tashi ba,....


Ruky tai murmushinta dayake qara mata kyau tace Wani gwara,keda kinsan Irin aikin da nakesha wlh da baxaka ki marmarin dama kece niba sbd yawan da muke saidai idan case Bai taso ba,aikema kin sani,Hanan tace shikenan yanxu dai xamu qarasa government house idan na koma gida xan kiraki,a kwai maganar Dana keso muyi,ruky tace shikenan saina jiki,Hanan tace ki gaida min mamah ,ruky tace xataji,daga haka sukai sallama,...

Karfe biyar da Rabi ruky ta tashi daga aiki takama hanyar gida,inda tana xuwa ta Tarar da mamah a falor ita da Mai aikinta suna hira,inda ruky ta jefar da jakar hannunta ta yaye after din saman uniform dinta tace wash mamah na gaji, tana dora kanta bisa kafadar mamah,mamah ta shafa kanta tace sannu Auta ni dama nasan xaki gaji ,hasiya tace sannu da dawowa uwata, ruky ta kalleta da murmushi tace yauwa baba hasiya,ya gida, hasiya tace lpy lau,...

Ta mike tace mamah bari na haura sama na watsa ruwa, mamah tace shikenan auta saikin sauko ,Amma ki tabbatar kinayi ki dawo kici abinci ,karki bari na hawo saman nan na sameki Baki sauko ba,ta tura Baki gaba tace to mamah,haka ta haura sama,inda mamah suka cigaba da hira da hasiya,...

Bayan ta fito daga wanka tana cikin shafa lotion dinta masu kamshi da tsada ,taji wayanta data ajiye a bed side ,tana ringing ta duba daga Mai Kiran,take ranta ya Baci , ta kau da kanta ta cigava da shafa manta bayan ta gama ta shirya cikin doguwar riga marar nauyi da hula bayan ta tattare gashin ta cikin hulan ta bar wayarma Dan indai ta fita da wayar nan ana kira Kuma batai picking ba sai mamah tasa ta tai picking ko batai Niya ba,a daki ta barta,har lokacin ba'a fasa Kiranba tai tsaki a karo na babu adadi,ta sauka qasa xuwa falo,....

Tana sauka ta tarar da ya hanaf a falon Yana duke gaban mamah suna gaisawa da dukan alamu xuwansa kenan ,tana ganin sa ta waro ido waje tace laa ya hanaf yaushe kaxo sannunka da xuwa,yayi murmushinsa Mai kyau yace yanxu naxo Auta,ai na tambayeki mamah tace kina sama kema yanxu kika dawo daga aiki,tace wlh Yaya yanxu na dawo ya hanya yace lpy lau ya aiki kema tai murmushi tace alhamdulillah Yaya,yace Masha Allah,Tayi hanyar dining tace yaya idan kagama gaisawa da mamah kataho muci abinci yayi murmushi yace shikenan,bari mu gama haka ta Isa dining ta tsaya xaman jiransa,...


________ZARI'A________

Baba Ina wuni,baba Dake xaune a tsakar gida Amma ta bakin kofar dakinsa,inda ya bawa su ummah umarnin kowa ya shige daki ,Dan Yana so su tattuna da Kabiru daya kira tunjiya, yace lpy lau Kabiru ya fada Yana murmushi,yace yauwa aikaji abinda nafada Maka tun jiya a waya ko,to Ameenah dai ta dawo dana tambayeta saitace min wai ai Kaine ka korota,Kabiru daya sunkuyar da kai tun xuwansa kamar mutumin kirki,yace wlh baba bankori Ameenah ba,itace ma ta takuramim akan saina saketa aidama ba qaunata takeba auran dole aka mata Dani sbd haka na saketa kullum haka take min,ranar Kuma Ina dawowa gida ko xama banyiba tace ita wlh baxata xauna ba gida xata a tsakar darennan ,nace ta bari gove na kaita tace ita Bata yarda ba,saita tafi Ina shiga bayi xanyi wanka kafin nafito harta tafi sai fitowa nayi bangantaba,ni daukata ma gida taxo,....

Baba dayakejin xuciyarsa kamar ta babbake sbd takaici yace aidama nasan Ameenah karya takeyi,baxa ka tava korar taba,ita tasan Ina ta tafi,baba asabe Dake lave a bayan kofar ta tana Jin duk tattaunawar da baba yake da Kabiru aiji tai kamar ta goya Kabiru sbd Dadi,sai murmushi take , Baba yace bari na kirata ta baka hkr sannan Dan Allah kayi hkr ta koma dakinta kasan yaran yanxu sai hkr ka haifesu ne baka haifi halinsuba, Kabiru dayakejin farin ciki aransa ganin yadda duk lokacin da Abu ya hadasu da Ameenah ba'a Wani Jin ta bakinta bare a tsaya a saurari maganar ta yasa yake mata duk abinda yaga dama Dan haka cikin yin qasa da kansa yace baba ai babu komai nasan da haka daga haka baba ya hau kwalawa Ameenah kira,....

Muna cikin falon ummah axaune nida ummah da Nana da tun lokacin da baba yace mu koma daki sbd Kabiru yaxo ,muka koma nidai gabadaya kirjina dukan tara Tara yakeyi,sbd nasan Kabiru karyar Daya Saba yiwa baba zaiyi , shikuma baba ya hau kai ya xauna babu Wani bincike bare ya hadamu yaji ta bakin kowa,suman xaune nai danaji Kabiru Yana tsarawa baba karya wai har da cewa nice nace saina koma gidanmu ,Kuma wai Saida naga ya shiga wanka na fito , mutumin da Saida yamin dukan tsiya sannan yace na bar masa gidansa shine Ma ya koroni har waje,Ina rokarsa ya barni ma xuwa washe gari Amma yaki,Amma ko kunya baiji ba yake fadawa baba haka,yaushe baba xai Gane halin Kabiru,kodan samun waje yayi tunda baba Bai tava lura da taban da Kabiru yaji min ba Wanda gabadaya da xan buda jikina duka shatin dukansane Daya Sha yimin, nidai kawai Ina xauna ne Amma wlh hankalina Yana kan Kabiru daya goce Yana shara rawa baba karya ba, ban tsinke da lamarin ba Saida naji baba Yana na fito na bawa Kabiru hkr,Kuma Yana rokarsa dana koma tare da kwalamin Kiran danaji baba Yana min,...


Xubar da hawaye kawai nake Ina tausayin kaina,Nana ma duk hankalinta ya tashi ,bare Kuma umma wacce nasan da ZA'A Bude xuciyarta wlh nasan tafasa kawai takeyi,inda naji baba asabe ta bankado mana labulan falor bakinta kamar xai tsage sbd murmushi kira take a'a wai Ameenah baxa ki fitoba Baban kune fa yake kiranki ,ga Kuma mijinki yaxo,ki fito ke suke jira ta fada tana Mai kallan ummah data xuba mata ido kawai tana kallanta,saikuma tai mata Wani Irin kallo sannan ta saki labulan ta tafi,....

Haka na mike nai bakin kofar falon inda naji Nana tana tsaki kasa kasa da cewa munafukar mata kawai in Sha Allah duk Wani makircinki da sharrin ki kanki xai koma dana yayan ki,haka na fita waje kaina a qasa Dan wlh kamar xai fado haka nakeji,sbd ciwo,na tsugunna a gefan ta barmar da naga baba axaune akai Kabiru Kuma Yana daga gefan damarsa ,Wanda tunda na fito daya kalleni sau daya ya sunkuyar da kai,nace baba Gani,yace yauwa bawa mijinki hkr maxa yanxu Kuma ki tashi kiwa babarki sallama ki fito ku tafi, kukane ya kufcemin,naji muryar baba cikin tsawa Yana kuka nakira ki kimin ko me ,nace ki bawa mijinki hkr, haka na daure , na bawa Kabiru hkr,inda naji Yana babu komai,baba yace ka hkr kuwa Kabiru kota Kara baka Wani yace baba na hkr baba yace toh madallah Maza tashi kiyiwa babarki sallama ki fito ku tafi,inda na mike da gudu nai falon ummah Ina Mai fadawa kanta Ina Kuka kamar xan haukace sbd bakin ciki, ummah ma rungumeni tayi inda Nana ma ta taho ta rungumemu duka,haka muka hadu muke ta kuka ,inda saijin muryar baba asabe mukaji tana cewa a'a meya haka ba jiranki ake ba, tana fada tana vanbaroni daga jikin su ummah,ganin munki sakin juna yasata kiran baba ,tana malam kaga maimuna taki sakin yarinyar nan sun makal kale juna,...

Tana fada tana qara vanbaroni daga jikin ummah inda naji muryar baba cikin fada Yana cewa ai dama yasan ummah ce me xugani, shiyasa kwata kwata ko gidannan bayaso naxo da sunan xiyara inda naji ummah tana sakina tana cewa nayi hkr na koma dakina adai dai lokacin da baba asabe ta samu nasarar rabamu inda naji tana haba sai kace wacce xa'a kaita wuta,maxa muje kibi mijinki Yana jiranki a waje inda ta Jani da qarfin tsiya Dan tirjewa nai baba Kuma naji yana zaki nutsu ko saina xaneki ,yauwa Kabiru gatanan kuje Allah ya kiyaye,haka baba asabe ta rakoni har bakin kofa inda tasakemin hannu tana maxa kuje Allah ya kiyaye, Kabiru ayita ta hakuri yarinta ke damunta kabiru yace Babu komai Baba,inda naga ya Saka hannu a aljihu ya bawa baba Abu Wanda nake kyauta ta xaton kudine ,haka tahau yi masa godiya, ,haka Ina ji Ina Gani aka rabani da ummah da Nana da Kuma tirsasamin komawa gidan Kabiru,....




07066508376________
'?Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DC2ekqRnajZAQQvErdaWfD


*_______JAMI'AR TSARO*______


*_____THE aWOMEN POLICE*_____


______THIS STORY IS TOUCHING HEART, I WAS SPEECHLESS TO EXPLAIN IT, BUT WE SHOULD SEE ON WHAT HAPPENED TO OUR LIFE KNOW, SO, BE WITH ME U LOVE IT MORE THAN U LOVE _________
'?


*NA*

*_______NAJA'ATU UMAR FAROOQ*_______


*____(MRS SARAKIES)*____


*=?1?QUEEN OF WRITERS ASSOCIATION (QOWA)=?1?*

*Bismillahirrahmanirrahim*


_______season one ,ep 5??


_________
'?
'?

Da daddare ruky tana kwance a dakinta ta ta lulluba cikin lallaisan blanket,suna waya da Hanan,wacce take Bata lvrin xuwansu Abuja,inda ruky tai shiru tana tunani Dan gabadaya hankalinta ya bar jikinta tun tana sauraran Hanan hardai daga karshe ta dauke wuta Tama daina,jinta sbd yadda tai nisa acikin tunanin data ke,Saida Hanan tai Mata qara acikin wayar Sannan ta dawo hankanti,....

Ruky ta dauke wayar daga kunnata after a while ta Maida ta ce haba hanan saikin fasa min kunne,Hanan tace haba ruky ko bacci kika farane,ya xa'ayi naita magana Amma ki kyaleni,ruky ta harari wayar kamar Hanan ce agaban ta ,tace eh bacci nake ji, Hanan tace shikenan Saida safe ,ruky Bata Bata ansa ba ta kashe wayar tana kunkuni,saikuma ta cigaba da tunaninta akan matar nan, da yarta,tunani take yadda xatabi diddigin case din ita kadai Batare da Wani ya saniba yanxu,Wani tunani ne ya darsu aranta Kuma ta yarda dashi sosai Dan haka taji ranta ya Danyi sanyi Sannan ta qara addu'a ta kwanta bayan tayi switch off din wayarta,....


Washegari ruky Bata zarce ko Ina daga gida ba,sai gidan TV na GADANGA TV & RADIO,Dake nan jihar Kaduna,haka ta qaraso bakin gate din inda security din bakin gate din suka taho ganin wacce ke cikin motar da kaki na alamar JAMI'AR TSARO CE yasa sukai sauri suka Bude mata gate din ta shiga ciki ,tana xuwa Tai parking a inda ya dace saikuma ta Bude motar xata sauko saikuma, ta tuna cewa ai Bata ma San Ina xata nufa ba,Amma Kuma Ma tambayi baya bata sannan ta hango Wani katon building me rubutu a jiki da dukan alamu duk Wani department ns wurin yana cikin wannan building din Dan haka ta fito cikin shigarta as usual, after dress dinta kan uniform dinta sai talhat dinta Kuma sky blue sai ta rike cap dinta a hannu, ta nufi building din tana tunanin sunan mutumin,saidai Kuma ba lallai ta iya ganeshiba, Amma inta ganshi kila ta iya Gane kamanninsa,tasa kai cikin reception din inda tana shiga aka bita da kallo daga Maza har mata, Bata damu ba haka ta cigaba da tafiya cikin nutsuwa harta qarasa wajensu tai sallama suka ansa mata tareda Bata girma,ta qarasa wajen wata mace inda ta tambayeta bangaren News,matar ta kwatanta ta mata cikin girmamawa,tai godiya tai gaba,ta haura sama ta bi Wani corridor,, data hangi Wani room dayake fessing dinta,taga anrubuta daga samansa news room,haka ta qarasa ta shiga da sallama abakinta,....

Mutane biyu ta Gani suna magana suka ansa mata, suna kallanta da Dan makaki haka,to mamaki mana JAMI'AR TSARO a department dinsu duk da dai ba bakon Abu bane Amma itadai Basu taba ganin ta awurin ba,a dai dai lokacin da itama take qarewa wurin kallo,Wanda ko Wani table a gabansa akwai sunan me wurin inda idanta ya hango mata sunan da take NEMA wato Ibrahim Khalil,....

Daya ne ya kasa hkr yace ma da sigar girmamawa ta dago ta kalleshi da dara daran idanuwanta,Saida ya hadiye wani yawu da baisan ta Ina ya makale masa ba ganin wannan halittar,yace how may I help you,cikin muryarta Mai dadin sauraro tai dan murmushi tace I want see Ibrahim Khalil,ta fada tana nuna table din sa,yace ok bai karaso ba Amma nasan in Sha Allah yanxu Yana hanya,Amma kunyi waya dashi,tace no Amma Babu damuwa xan jirashi suka nuna mata wata visitors chair Dake Dan nesa dasu ta xauna ,ta dauka wayarta tana latsawa yayin da wadannan mutane suke kallan ta, ta gefan ido suna tasbihi ga ubangiji daya tsara wanna halittar, tana nan xaune kusan 10 minutes Amma Ibrahim Khalil Bai xoba Dan haka ta kalli watch din hannunta ,taga time sai tafiya yakeyi,Dan haka ta fara deciding kawai tafiya xatai ,ta dawo next Time,tana kokarin mikewa Ibrahim Khalil ya shigo office din bakinsa dauke da sallama,ga fara'a Dan daga ganinsa kinga Mai barkonci, wadannan mutanan suka ansa masa ya qarasa garesu sukai musabaha,sukace yau Kuma Ina ka tsaya, kodai daukar labaran naka ne da Jin gulma ya tsaida kai,ya dauki littafin signing a dai dai lokacin Yana Basu ansa da cewa kamar ka sani kuwa Dan abune Mai mahimmanci ya tsaidani ,muktar yace toh yanxu dai kafin ka fara xuba kayi visitor tun daxu take jiranka, officer ga ibrahim Khalil,ya fada Yana nuna masa Ruky wacce tun Daya shigo tai masa kallo Daya ta cigaba da latsa wayar ta,....

Ya shafa kansa yayi kasa da murya yace police,Yana xaro ido suka sa dariya sukace kaje mana ,haka ya shafa kansa da hannu,daya Hannunsa a aljihu ya karasa wurin ta yayi saluting nata ,ta dago ta kalleshi da idanta masu kyau,ita sai abinda yayi din ya Bata dariya,Amma ta Dake,ta ansa masa da kai ,yace may I seat ,ta daga masa kai,ya xauna a kujerar Dake gefen ta,yace ma kodai laifi nai, Tai murmushin da take rikewa tace me ka Gani,yace naga JAMI'AR TSARO ne taxo ne mana Kinga koh ai ba'a rasa dayan biyu ba,...

Tace ko Daya Ibrahim Khalil magana ce ta kawoni Mai mahimmanci wadda nake so mu tattuna iya mu biyu ,cikin girmamawa da bawa maganar ta mahimmanci yace shikenan,yanxu Ina kikeso mu tattauna din,ya fada yana Dan mamakin Kiran sunansa da tai, tace idan ba damuwa ka biyoni,haka ta mike ta shiga gaba Yana binta a baya har suka sauka kasa inda suka fito reception ,suka fita daga building din ma gabadaya suka jera suna tafiya aka bisu da kallo, har suka qarasa inda tai parking ta jingina jikin motar tace bismillahirrah ,shima yayi yadda tai har lokacin idansa a kanta yake Yana mamakin wacce Irin magana Zasuyi,

Ta sauke numfashi tace malam Khalil,sunana ASP Rukayya umar Mai Tama,ni JAMI'AR TSARO CE wacce take aiki a Headquarter ta nan Kaduna a sashe na bincike,nasan xakai mamakin xuwana nemanka da nayi, karkayi mamaki duk acikin aikinane,Amma yanxu ba wannan ba jiya naji Kuma naga hirarka da wata baiwar Allah,wacce tace anketawa yarta haddi na xalinci,wannan maganar ce ta kawoni tafada tana Mai kallan Ibrahim Khalil da Kuma yana yin daya shiga,ta cigaba da fadin,inason sanin inda matar take xaune da Kuma Wani information nata idan ka sani domin inaso ne binciki case din ne,...

Ibrahim Khalil ya sauke numfashi cikin girmamawa yace ASP ,tunda kece Kuma ke hukuma ce, bansan Wani Irin gudunmawa xaki Bada akanta tava,domin matar nan a gsky tana bukatar taimako,anan Kaduna take hayin rigasa,Nima bansan gidan tava Amma Ina da full address dinta sbd ko Allah zaisa asamu Wanda zai taiMaka mata,ta sauke numfashi tace nagode malam Khalil yayi murmushi yace girmankine ASP,tace Amma idan ba damuwa me zai hana muje tare idan badamuwa,yayi murmushi yace ba damuwa ranki dade duk lokacin da kika shirya,ni Mai tai Maka mikine,tai murmushi tace nagode sosai malam Khalil,yanxu dai ka bani contact dinka xanje aikine yanxu sbd na makara sai kirana ake ta fada tana Mai kallan wayarta da yake ta vibrate tun daxu,yace Babu komai haka ta mika masa wayarta inda yasa mata contact din nashi ta karba tai masa godiya ta Bude motar ta tashiga shima ya wuce ciki,inda tai reverse tana Mai Jin Sanya aranta,taja tsaki a dai dai lokacin da Wani Kiran ya sake shigowa wannan Kuma DCP ne ke Kiranta Dan dazu Shareef yay ta Kiranta,....

Batai picking kodaya daga cikin Kiran da ake ta jera mata ba har ta qarasa headquarter inda tana yin parking ta fito da motarta ,cikin nutsuwa ta fara takawa har department dinsu inda tana shiga ta gaisa da mutane daga nan ta wuce office dinsu tana shiga tai sallama,kafin ta karasa wurin seat dinta,tana kokarin cire after din jikinta Shareef ya shigo,ta kalleshi jin ya kira sunan on a serious,yace ruky Ina kika tsaya ne yau Baki shigo da wuriba,ga DCP sai nemanki yake,nayi ta kiranki Kuma bakya picking,gashi yanxu almost 12 ,yanxu haka


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login