Showing 180001 words to 183000 words out of 278032 words

Chapter 61 - JAMI'AR TSARO COMPLET by MRS SARAKIES.doc

23 Oct 2025

1034

firgici da tashin hankalin daya shigeta lokaci D???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?'aya, kallan ta kawai take harta qaraso cikin gidan ga idonta yadda ya kada yay jajur kamar wacce aka watsawa barkono aciki,da ka ganta kasan itama ba lpy ce ta kawo ta gidan ba ......


Tana qarasowa ta sauke kayanta a tsakiyar gidan ta zauna a qasa dab'as tana sauke numfashi sbd gajiyar datai haka ma 'ya'yan ta da Suma suka samu wuri suka zauna kusa da ita Dan tafiyar kafa sukai tun daga Tasha har unguwar tudun wada.baba asabe ta kalli lawisa kamar me koyon magana ta ce "lawisa lpy kuwa? na ganki agida yanxu? Ta fada kamar zata saki Kuka , lawisa ta fashe da kukun da take ta k'ok'arin taga batayi shi ba ta ce "Babar mu lurwanu ne baya bamu abinci munfi wata Daya rabon daya kawo mana kwayar gero gidan, bare Kuma kayan abinci ballan tana har mu samu muci abincin Dani da yaran, idan nai managa Kuma saiya hau xagina Yana cimun mutunci,ga Rashin mutunci da yake min kala kala babu dare babu Rana,shekaran jiya Kuma kawai yaxo ya ce "na kwashe kayana nada Yara daga Dakinsu" na ce "meyasa? dakin Yara nefa" budar bakinsa sai kawai ya ce "wai nidai na kwashe mana" banyi masa musu ba na kwashe kayan ,Ashe shi da akwai abinda xaiyi ,sai jiya da Rana muna xaune a tsak'ar gidan kawai naga mata suna shigowa da kaya na mik'e tsaye na Sha gaban su na ce "lpy? saiga lurwanu ya shigo daga bayansu wai in Basu hanya su wuce kaya zasu Saka A dakin yaran dayasa na kwashe jiya, na ce "meyasa? Budar bakinsa wai aure ya qara ya ce "Kuma matan su shiga suyi jeran na hanasu idan na isa daga haka ya bar gidan,Ina ji ina Gani suka shiga d'akin yarana suka jera kayan amaryar sa aciki ,Kuma dakuna biyu ne dama gidan ,na shige d'aki nai ta kuka ,da daddare aka kawo amarya , bayan ya shigo na fita na ce "yanzu lurwanu sbd Allah muma baka gama wada tamu da abinci ba shine zaka qaro aure? Budar bakinsa wai ya qara auran na hanashi" Niko na ce "Bai isa ba" muka hau haniya shine yamin duka jiyan sannan ya ce " ya sakeni saki biyu na tafi gida"ta qarasa fada tana Mai rushewa da gunjin kuka.....



Baaba asabe kasa magana tai sbd abinda Daya to Kare mata kirji, Dak'yar ta samu zarafin magana ta ce "yanxu shi lurwanun shine ya maidake haka? Kinga yadda kika koma lawaisa? yo ai koni da nake uwarki wlh na fiki kyan Gani" sai Kuma ta ce "innalillahi wainna ilaihi rajiun, wannan wacce Irin masifa ce take kusan Toni ,sai Kuma ta ce "na shiga uku" yanxu ku biyu kenan aka sako ban fita daga wannan tashin hankalin ba na shiga Wani ,ga mardiya itama yau satinta guda agida da jamilu ya sakoto,Ina kokarin naga ta koma na kirashi jiya shine ya qarashe mata D'aya sakin yazama uku,ga kema ansakoki wannan mazaje naku allah dai ya tsine musu albarka,yanzu ke ba saki biyu yay Miki ba? aida Baki taho ba kinyi ta bashi hkr harya sai ya hakura tukunna ,Kya kama ki taho gida bayan kinsan gidan ba isash shun dakuna garemu ba" lawisa ta ce "babarmu na ba shi hkr Kuma? Watso min da kayana yayi waje fa yayi kuma ya ce dole sai na bar masa gidansa " baba asabe ta xube a inda take zaune ta cire D'an kwalin kanta tana girgixa kai ta ce "lawisa dole mu kirashi koni da kaina na bashi hkr ki koma tun kafin makiya suyi mana dariya.....


Mardiya data fito daga dak'in baba asabe tun d'azu tana jinsu ta ce " waike babarmu sai ki dinga cewa wai mutum ya zauna karya taho? Wai Dan kada makiya suyi mana dariya? suwaye mak'iyan? idanma Dan baba maimuna kike tunani to kinsan ita babu ruwan ta da shiga abinda babu ruwanta,ke kawai burinki kar mak'iya suyi miki dariya bakya tunanin wacce makoma 'ya'yan ki zasu shiga,wlh nidai Dan Baki san Irin azabar da jamilu yake gana min bane shiyasa zakice saina koma, da wlh baza kiyi mar Marin na koma ba" baba asabe ta Daka mata tsawa ta ce"ya isheki" har yau maimuna kike karewa kike cewa Bata shiga abinda babu ruwanta Dan ke Bakisan sharrin kishiya bane shiyasa zakice haka,ke tunda jamilu ya qara she miki sakin saiki zauna kici abinda zakici agidan ita dai lawisa zata koma d'akinta Dan zansa malam ya kira shi lurwanun a waya ya Bashi hkr" lawisa ta mike ta ce "Haba babarmu yanxu baba ne ma zai kirashi ya bashi hkr? nidai wlh baxan koma ba".....


Baba asabe ta Bude Baki tana kallan ta kafin ta ce"to yanxu Dan ubanki idan Ba'a bashi hakurin ba me za'a masa ,Ina xamu kai wannan yaran da Kuka debo kuka taho Dasu,'ya'yan mardiya da ita Kanta bala'in cine dasu kamar gara ,to kema nasan da yunwa ajikinku baxa ku ga gara cin abinci ba,sbd haka wlh baxan iya ba komawa dak'inki zakiyi ke tunda ba saki uku bane" lawisa tasa kuka ta ce"wlh Allah Babar mu ni dai bazan koma ba, Dan bakiga Irin wulakancin Daya dinga yimin bane shiyasa da k'yar ma ya bari na kwana na taho yau din da haka ya ce "acikin daran zan taho" ta qarasa fada tana Mai Jan majina,baba asabe ta ce afusace "to wlh ko kasheki zaiyi saikin Koma Dan baxan tab'a yadda ku xauna agidan nan ba makota suna shigowa suna ganin ku Rid'a_Rid'a daku Kuna zawarci ba" daga haka ta Mik'e ta koma bakin murhun xuciyarta nayi mata zafi ji take Kamar tafi kowa kunci aduniyar nan sbd Bata taba tunanin Irin wannan ranar na xuwa mata ba, mardiya ta koma dak'i Jin d'anta na kuka , itama lawisa ta mik'e ta d'auki gana masgo d'in data xo dashi Wanda kayanta Dana 'ya'yanta ne a ciki ta kama hannun qaramar 'yarta sauran yaran ma suke bita ta shige d'akin baba asabe,baba asabe ta bisu da kallo tana Jin kamar tai ta rusa ihu ko zata ji Dad'i a ranta wannan Wani Irin tashin hankali ne yake kusan tota daga wannan sai wannn Saura ma bilkisu itama Allah yasa kar mijin yasa kota ,Dan idan ya sakoto itakan ta shiga uku......



Ta kwalawa zaliha kira, zaliha ta fito cikin shirin fita kasuwa ,me napep yay sallama zaliha ta ce "ya shigo ya d'auki kulolin abinci ,Babu musu ya shigo ya d'auki kulolin abincin yakaisu cikin napep din Saida ya gama tsaf sannan zaliha taiwa baba asabe sallama ta tafi ,baba asabe ta bita da kallo ganin yadda kwana biyun nan zaliha ta qara girma da kyau tayi haske,komai na halittar ta sun qara girma Bata kawo komai aranta ba illah cikar budurci ne k'ila yasa zaliha take wannan girman da kyau haka,haka nan ta mike tana Mai Jin kamar xata Fad'i sbd abinda take ji aranta .....



___________?&


An kawo su Ameenah headquarter,Saida AA Arab ya dawo sannan yaje wajensu ya sallamesu aka Basu kudin mota kowa ya koma inda aka dauko shi , Ameenah ta fito bakin heardquater anan suka had'u da su ummah da malam Auwalu sbd ba'a bari sun shiga ba , ummah tai sauri ta taro Ameenah ganin ta fito ta rik'eta tana tambayar ta da shikenan Babu komai ai ko? Ameenah tai murmushin ta me kyau ta ce "eh ummah shikenan Kinga ma sun bamu kudin mota" ta fad'a tana nuna wa ummah kudin , ummah ta karba ta k'irga taga dubu Ashirin ne ,ta mika wa Ameenah ta ce "waya Baki? Ameenah tace "Wani shugaban sune ya bamu " ummah ta jinjina kai kafin ta ce " Allah ya Saka Masa da Alkhairi, malam Auwalu ya qaraso wurin Yana kallan Ameenah ya ce "kin fito Ameenah ?sannu Ameenah kinji?Dan Allah ki yafe min ?Ameenah tai murmushi ta ce "baba baka min komai ba dama auran Kabiru ne banaso Kuma gashi yanxu ya sakeni Tun jiya da muka zo" ummah cikin mamaki da Jin dadi ta ce"ya sakeki kai Alhamdulillah, Ta ya ya ko ya sakeki Ameenah? Ta fada tana kallan Ameenah, Ameenah ta ce "shugaban sune yasa su sakemu sbd ance baza su taba fitowa ba" ummah ta rungumeta ta ce "kai Alhamdulillah Amma wannan ogan nasu Allah yay Masa Albarka Allah ya biya masa buk'atunsa na alkhairi" malam Auwalu shidai Yana gefe Yana kallansu Amma baice komai ba Dan wlh kunyar Ameenah yake ji kamar me sbd Gani yake kamar Bai mata adalci ba, baima san Taya ya ya aurawa Ameenah Kabiru ba yaro Wanda Bai San tushan Saba bare ASALIN sa kawai ya dauki ' yarsa ya bashi ,shima yaji dadi da Allah baisa sun had'a xuri'a dashi ba duk da dai baisaniba ko tana da ciki yanxu ajikinta......



Ummah ta rike hannun ta kamar wacce xa'a kwace mata Ameenah ahannun tana kallan malam Auwalu ta ce "malam mu tafi Tasha muhau mota mu tafi gida tunda mungama abinda ya kawo mu"Babu musu malam Auwalu ya ce "to"daga haka suka nufi bakin titi suna tsaye suna jiran napep suka ga wata mota har tai gaba Kuma ta dawo baya ,ganin Ameenah yasa yay parking a gabansu,sudai su ummah kallan motar kawai suke harta tsaya agabansu, me ita ya fito daga cikin motar Yana zagayowa ta b'arin da suke tsaye , cikin shigar sa ta lauyoyi ,bayan ya iso ya risina ya gaida malam Auwalu dan tabbas bazai taba manta fuskar Saba Malam Auwalu ya ansa masa Amma Bai ambaci sunan Saba sbd abun ai ba yau bane an Dade, sannan ya gaida ummah, ummah ta ansa masa tana tunanin Ina tasan wannan fuskar, itadai Ameenah kallonsa kawai take.....



Bata farga ba taji barrister shamsu ya ce "baba nasan Baku Gane niba koh? malam Auwalu yay murmushi ya ce "nidai kamar naso nasan furkar nan , barrister shamsu yay murmushi ya ce "
Allah sarkie" suna shamsu Wanda ya tab'a Neman auran Ameenah Ashe karun baya Kuma Allah Bai yiba" ya *fada yana* murmushi har lokacin,ba malam Auwalu ba har ummah Saida tayi mamaki, malam Auwalu ya ce cikin mamaki"tabbas" iKon Allah shamsu dama kana nan ? Barrister shamsu Yana murmushi ya ce"wlh baba Ina nan ya bayan rabuwa ? malam Auwalu ya ce "Alhamdulillah" barrister shamsu ya ce " ya na ganku a headquarter baba Ina patan lpy?ya fada Yana kallan Malam Auwalu,malam Auwalu yay tsai cikin kunyar data lullub'e shi lokaci guda jiyake kamar karya fadawa barrister shamsu gsky Amma tunda babu yadda xaiyi Kuma baya so yay Masa qarya yasa ya ce"wlh mijin Ameenah ne wai suke kidnapping shine aka kamasu to sai jiya akaje aka dauko ita Ameenah hargida daga nan headquarter shine akace sai sunzo sunga maxajansu tukunna,gashi ma har anyanke musu hukuncin xaman gidan yari,Kuma an tilasta musu Dasu sakesu gashi ma har sun sakesun kuma Suma ansallamesu shine ka ganmu anan " ya fada cikin kunya da Wani Irin yanayi ,barrister shamsu ya ce cikin alhini "Allah sarkie" Allah ya kiyaye gaba"yanxu ai sun sallamesu babu komai koh? Malam Auwalu ya ce "eh Babu komai yanxu haka ma muna jiran abun hawane zai kaimu Tasha muhau mota" barrister shamsu ya kalli tsadaddan agogon hannunsa yaga da sauran lokaci ya ce "baba idan Babu damuwa muje na kaiku tashar yanxu ma Dan Ina da aiki ne da har gida xan kaiku,ya cigaba Kuna ZARI'A ne har yanxu baba? Malam Auwalu ya ce "eh muna ZARI'A haryanxu, Amma da ka barshi kaje kayi aikinka kawai mungode" barrister shamsu yay murmushi ya ce "Babu komai baba muje kawai, Dakyar malam Auwalu ya yarda zai hau motar barrister shamsu Dan wlh sai Yanxu yake Jin kunyar sa kamar me, ummah tai masa godiya sosai kamar ta Ari Baki, shidai barrister shamsu baice komai ba har suka shiga motar ahanya suna ta hira da malam Auwalu har yake tambayar sa suna gidan daya sani tun a Baya?malam Auwalu ya ce "eh suna nan" barrister shamsu ya jinjina kai,shima malam Auwalu yake tambayar sa ko anan Kaduna yake aiki? barrister shamsu ya ce "eh anan yake aiki" malam Auwalu yay Masa patan nasara har suka iso park din, barrister shamsu ya biya musu kudin mota sannan ya bawa malam Auwalu kudi Mai yawa ahaka suka rabu malam Auwalu Yana tai masa godiya shida ummah.....



Rukayya da Hanan Basu koma gida ba saida ruky ta raka Hanan government house ta dalilin Kiran ta da akayi , dataje matar governor ce ta aiki Hanan gidan wata k'awarta matar D'an majalisa Dake cikin garin Kaduna unguwar asokoro zata karbo mata Sako ,sanda suka je sun tadda Wani Dan saurayi agidan bayan sun karbo sakon sun fito dama tunda suka shigo cikin falon Yana zaune Yana kallansu, idansa yana kan ruky wacce ta haderai tunda taga Yana kallan ta,Bai musu magana ya fiso saisun fito waje tukunna,ya rigasu fitowa,Saida suka fito suna k'ok'arin shiga mota sannan ya qaraso wajen su Yana taku d'ai d'ai hannunsa zube cikin aljihun Wandansa,da kin ganshi kinsan Dan gidan ne,sbd yadda hutu da Jin Dadi ya bayyana atare dashi,ya taresu Yana musu magana duk suka juya suka kallansa ganin ya nufo inda suke yasa ruky tai saurin shegewa motar,Hanan ce kadai ta tsaya harya qara so ,tana kallan sa kafin ta ce lpy ? Yana murmushi tareda shafa kansa ya ce "please sister Aran k'awarki zaki bani Kona 5 minutes ne" ya fada Yana nuna mata gaban motar inda ruky ta shige Hanan tai murmushi tace "ok"daga haka ta leka window motar tana kallan Ruky wacce ta Bata Rai tana turo Baki gaba,Hanan tana yake dariya ta ce "ruky ki fito wajenki yaxo? Ta fada tana gintse dariyarta.....



Ruky tai mata Wani kallo ta d'auke kanta,Hakan yasa Hanan ganewa baxa tab'a Kulashi ba,tana murmushi ta juya tana kallon sa ta ce "kayi hkr wlh nasan tunda tak'i kulani baxa ta tab'a Saura ran kaba' ya Sha fa kansa ya ce "please sister,Hanan ta danyi murmushi ta ce "baka yarda ba kenen" wlh tunda tamin haka ni nasan baxa ta tab'a fitowa ba,ya Marai raice ya ce "shikenan I understand u,but please can u help me with her digit, ruky da take Jin duk conversation dinsu ta lek'o ta window motar ta makawa Hanan wata muguwar Harara ta ce "idan kika bashi contact d'ina wlh saina miki Rashin mutunci Hanan,tana fadin haka ta Maida kanta ciki,Hanan ta saki Baki tana kallan ta sbd with serious talk tai maganar Dan haka ta kalleshi ta ce "kayi hkr" yay murmushi ya ce "ke ki bani digit din naki tunda ita taki bani nata" Hanan ta girgixa masa kai"kafin tai magana ya ce "please karyi mini Haka inaso ne xamuyi magana Dake daga baya Dan Allah karki ce min a'a" badan Hanan taso ba ta bashi digit dinta yay mata godiya ya ce"Ameer by name " Hanan ta jinji na masa kai daga haka ya bar wajen Yana daga musu hannu, hanan ta tada motar suka bar gidan ruky sai masifa take mata ahanya kamar me ita dai Hanan batace mata komai ba tai shiru tana
sauraran ta.......





07066508376________
'?Follow the Mrs Sarakies=؋? =?1? HAUSA Novel Channel channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VbBRj1D35fLuSHibdq1Y






*____JAMI'AR TSARO ____*



*____THE WOMEN POLICE ____*



*NA*



*____NAJA'ATU UMAR FAROOQ ____*



*____(MRS SARAKIES =؋?)=?1?____*



*TAURARI (' WRITER'S ASSOCIATION ('*



*TEAM 4 GOLDEN STAR (' WRITER'S*



*Bismillahirrahmanirrahim*



______season two ep 7?? 4??



____________?&


Bayan kwana biyar Hakan yay dai dai da sati uku da dawowar ruky gida ,yanxu haka tana zaune a d'aki wajen karfe biyar ta sauko downstairs sanye take cikin doguwar riga ta Shan iska ta zaman gida sai hula akanta, hannun ta rik'e da wayarta ta qarasa saukowa ta samu mamah zaune a falor da littafin azkar a hannun ta , baba hasiya Kuma tana d'akinta,ta qarasa gunta ta zauna kusa da mamah tana kallan ta, tana kuma tuna nin abunda zata nuna mata da yadda mamah xata d'auki abun Amma haka dai ta Dake, har mamah ta ajiye azkar din hannunta bayan ta kai inda take San kaiwa ta kalli ruky ta ce "lpy Auta? ruky tai mata murmushi tana Mikawa mamah wayar Hannun ta,babu musu mamah ta karb'a tana Karan ta text message din Da aka turawa ruky,sai Kuma ta mika mata wayar tana girgixa kai kafin ta ce "nifa Auta ajiya aikin nan xakiyi bazai Yu ki dinga sa kanki acikin matsala ba,gara kawai ki hakura dashi har Allah ya kawo Miki Wani,Amma haka kawai baxan qara barinki ki koma wannan aikin na ba kici gaba da boyemin duk abinda zakiyi ba,sbd adalilin wannan aikin kika kai kanki inda Babu Wanda ya aike ki"......



Ruky ta marai raice ta ce "mamah Dan Allah kiyi hakuri na koma aikin nan wlh sunyi min ma da har suka bari nai wannan kwanakin tunda Kinga gashi har sunyi magana na koma Dan Allah mamah kiyi hakuri" ta fada kamar zata saki Kuka, mamah ta ce "nidai na fad'a miki kuma na gama magana ta" daga haka mamah ta dau azkar din ta ta cigaba da Karan tawa, ruky ta mike Tana goge hawayen Daya taru a Idon ta hayewa sama da sauri xuwa dakin ta har tana had'awa da gudu , mamah ta bita da kallo tana girgixa kai,bayan ruky ta shiga d'akinta ta xube akan gado da Dunga rusa kuka kamar wacce aka aikowa da sakon mutuwa, Dan kuka taci ba kad'an ba,har bacci ya dauketa a wannan halin.bata tashi far Kawa ba sai after magrib Aiko gabadaya jikinta sai yay week da yawa da k'yar ta iya mikewa ta Shiga toilet tana Jin kanta nayi mata ciwo ba kad'an ba,Saida ta fito ta shimfid'a dar duma ta tayar da sallah da k'yar nan ma ta idar da sallah sbd yadda kanta yake harbawa.tana salleme wa ta koma kan gadon ta kwanta rufda ciki tana ya Mutsa fuska sbd yadda kan nata yake sara mata ta runtse idon ta tana


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login