Showing 60001 words to 63000 words out of 278032 words

Chapter 21 - JAMI'AR TSARO COMPLET by MRS SARAKIES.doc

23 Oct 2025

1089

take cikin halin Rashin lpy babu kulawa ba,.....


Lateef ya dauke kansa daga hotan ya dawo da ita fuskar DCP, Wanda ke kallansa Yana karantar Yanayinsa,yace yanxu wannan local yarinyar xaka nunamin kace na Santa,to ta inama zan Santa da zakamin wannan tambayar ya fada Yana Kara kallan DCP , DCP Shima har sannan kallansa yake bai dawo daga mamakin sunan mahaifin lateef ba dayake,kokonton wanne sunusi MaiTaman,DCP yace no kawai tambaya nake maka,kana nufin baka taba ganin tava ko awani wurin, lateef yace cikin kosawa da tambayar,ni ko a mafarki bantaba Ganin wannan local yarinyar ba bare Kuma a zahiri, DCP ya mike yace ok
Kayi hkr yanxu dare yayi,akwai abinda nakeso na nuna Maka so bazaiyuba sai gobe,Amma in Sha Allah idan muka gama bincikenmu xuwa gobe indai muka tabbatar daba kai din bane zamu sakeka,....


Lateef ya mike ya waro Ido waje yace what ,wai kana nufin anan xan kwana tukunna ma wai zargin me kuke akaina ne,wai Wani Irin Rashin mutunci ne wannan kuje ku daukoni har gidana, Amma kuxo kunamin Wani useless questions akan wai nasan wata,watanma yarinya yar local area ,wait tukunna ma akan wannan yarinyar kake nufin xan kwana anan ne, DCP yace I'm sorry, so bari naje I'm coming,daga haka yay hanyar fita, lateef ya mike da sauri ya biyo bayan DCP saidai Yana xuwa bakin kofar aka datse daga waje lateef kamar zai haukace yace kaxo ka fitarni daga wannan dirty wurin wlh duk saina sa daddy yasa an koreku daga Aiki,harni xaku ciwa mutunci ku kawoni wannan wurin ku tsare ni babu abinda nai muku saima xargina da kukeyi , kunsan ko waye mahaifina agarinnan kuwa,wlh saika rasa aikinka,haka ya dinga sunbatu adakinnan kamar mahaukaci sai bubbuga kofar yake gashi har sannan handcuff din tana hannunsa,.....



DCP ko Yana fita direct office dinsa ya tafi,gashi lokacin har anyi sallan magrib tuntuni haka ya fada toilet yay alwala yafito ya ta-da sallah bayan ya idar,ya na zaune awurin Bai tashi ba, haryanxu mamaki yake wai Alhaji sunusi MaiTama,wanne sunusi MaiTama kardai ace Dan uwan Baban Ruky,tunda ai shima sunansa UMAR MAITAMA Kuma a yadda ya sani kanin Baban Ruky ne, Allah ya masa Rahma,...


Indai hakane,ruky ai dara taci gidane indai har ya tabbata shine yaywa shafa wannan danyan aikin,gashi Kuma ko yanxu ya tabbatar da lateef ba mutumin kirki bane tunda harya kamashi tareda da wannan yarinyar wacce kai daka ganta haka,kaga yar bariki, shi yanxu yadda xai tunkari ruky da cewa lateef shine suspect dinsu kawai yakeji, barema bazai tava fada mataba harsai ya dauko shafa gobe ya nuna mata lateef idan shine, saiya fada mata Dan ta sani,idan Kuma bashi bane zai mata bayani,...


Daga haka ya fita danya sanar Abar lateef yay sallah,Yana fita har duhu yayi sai hasken fitulu kawai Tako Ina,yatarar da Wanda suke on duty yasa suje su taho da lateef bayan sun fito dashi yace akaishi Wani Daki Kuma su cirewa lateef handcuff din yay sallah dayake dakine na musamman akwai toilet harma da wuta da komai da komai na bukata,tunda shi ba'a tabbatar da Mai laifine ba ko ba Mai laifi bane shiyasa zasu bashi kulawar ,kafin su tabbatar da abinda suke xargin,bayan sun fito haka yay musu sallama sannan ya fita bayan sunmai a sauka lpy,daga haka DCP ya bar headwater yay hanyar gidansa Yana mamakin wannan al'amari,......


__________?&


Ameenah ce kwance sai rusar Kuka take gabadaya jikinta a kumbure yake svd dukan da Kabiru yay mata daxu,kafin ya fita,dan Abu yaxo dauka ba xama xaiyi ba,sbd ya mata magana batajiba shine yay mata wannan mummunan dukan dama haushinta yake ji,Wanda gabadaya jikinta shatin dukanne,gefen fuskarta ma yadan kumbura,sbd duka tun tana kukan da karfi har dai ta dawo sauke ajiyar xuciya da numfashi ,


Saude ce ta shigo kawo mata abinci ta taddata cikin wannan halin,Dan sai kwada sallama take tundaga waje,Jin ba'a ansa mata ba, yasata shigowa dakintai maxa ta qaraso wajen ta, Bayan ta ajiye kwanan abincin tace yaya Ameenah meya sameki, Ameenah ta kasa magana sai hawaye,ke sauka ta gefen fuskarta,saude ta ruga da gudu ta tafi gida ta sanarwa babarta halin data tadda Ameenah aciki,babar saude babu Shiri ta yafo xanin goyon danta ta fito ,ta biyo bayan saude ,....


Tana xuwa ta daga Ameenah wacce ke numfashi Dakyar tuni ta taimaka mata tasa hijab dinta, ta kamata ta tafi ta kaita chemist din shafi'u,bayan tasa saude ta dauko mata poss dinta,bayan shafi'u ya dubata ya Bata magun guna ,yace in Sha Allah indai Tasha nan da anjima zata ware ai dukane da Kuma kumbura mata jikinta da yay amma idan tasha mugun gunan xata sabe in Sha Allah, haka babar saude ta bashi kudin suka fito ta raka Ameenah hargida,...


Ta Bata magun gunan,Saida ta tabbatar datasha sannan ta kwantar da ita ,tace da saude ta xauna agunta tunda bacci ya dauketa idan ta farka ta kirata,ita bari taje gida sbd tabar qanin saude Yana barci,ta fita ranta a bala'in bace saitaji ta farama Jin haushin iyayen Ameenah da har Basu tunawa da ita susan halin da take ciki Amma suka banxatar da ita Wani qaton Banxa Yana wahalar da ita,wlh dole ma ta shirya xuwa ZARI'A kwanan nan taje ta sanar da iyayen Ameenah halin da suka barta aciki,taji Kuma idan har Sunsan axabar da Kabiru yake ganawa yarsu,Dan kar watarana ya kashe musu ya saidai Akira su, sudau ki gawarta,to garama idan Basu saniba su sani su tun wuri.....







07066508376________
'?Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DC2ekqRnajZAQQvErdaWfD




*____JAMI'AR TSARO ____*


*_____THE WOMEN POLICE_____*



*NA*


*____NAJA'ATU UMAR FAROOQ ____*


*____(MRS SARAKIES)____*


*QUEEN OF WRITERS ASSOCIATION (QOWA) =?1?*


*Bismillahirrahmanirrahim*



________season one ep 2?? 7??


___________?&



Washe gari haka DCP ya tafi asibiti yaje ya dauko shafa, yay wa baba lami bayanin komai ya samu incharge din asibitin akan xai tafi da shafa Headquarter ,akwai binciken da zasuyi, dayake private hospital ne babu Bata lokaci aka barshi ya tafi da shafa wacce baba lami ta riketa, haka suka shiga motar DCP wacce ASP anas ne ke driving,, sai DCP agefensa,sai baba lami da shafa abayan motar, haka suka fita daga asibitin Wanda direct headquarter suka nufa wajen karfe 10:30am na safe,.....

Suna xuwa haka ASP anas ya fito ya budewa, DCP sannan ya xaga ya budewa su baba lami suka fito wacce ke rike da shafa har lokacin,suna fitowa direct wurin da lateef yake suka nufa , bayan sun shiga DCP ya xauna akujera yace Dasu Baba lami da shafa su xauna,akan kujera bayan sun xauna,yace da ASP anas a fito da lateef da Kuma hany, babu musu ASP anas ya ansa cikin girmamawa ya fita daga wurin, babu dadewa ya dawo tareda hany bayan ta xauna, ASP anas ya koma ya dawo tareda lateef Wanda ya cika yay fam, sbd bakin cikin Irin wulakancin da aka masa, da Kuma hany wacce tai Kuka ta godewa Allah, idanta ya kumbura yay suntum,.



Bayan lateef ya xauna a kujerar Dake passing ta DCP, DCP ya Kalli hany yace munsallameki xaki iya tafiya ,ai tun kafin ya rufe Baki hany ta mike jikinta na rawa ta fice daga wurin bayan fitar hany DCP ya Kalli shafa wacce ke kallan lateef babu ko kiftawa jikinta da bakinta na rawa, kamar zatai magana, Amma ta kasa baba lami da Batasan komaiba ta riketa shiko lateef ko kallan inda shafa take da baba lami baiyiba Dan bema kula dasu ba,shi DCP kawai yake harara,.....

DCP ya juya ga kallansa kan lateef ganin Irin kallan da shafa take
Masa ya qara juya da kallansa kan shafa wacce har lokacin kallan lateef take, DCP yay qasa da murya yace shafa'atu kinsan wannan, ya fada Yana nuna mata lateef, Wanda shima tuni ya Maida kallansa kan shafa wacce ke kallan DCP Jin abinda ya fada,ta sunkuyar da kanta kasa tuni hawaye ya fara xubo mata akai akai, DCP ya qara qasa da murya yace shafa'atu ki dago ki kalleshi da kyau, shafa ta qara share hawayen dayaki tsaya mata har lokacin ta dago ta kalli lateef, taga ita yake kallo da Mamaki,....


DCP yace shine Wannan shafa ta dauke kanta daga kallan lateef ta gyada masa kai, DCP ya sauke numfashi yace no magana xakiyi tace shine, DCP yace shine Wanda yay raping dinki, shafa tana qara goge hawayen tace shine, lateef was confused & speechless,ya fara zare ido Yana Jin duk conversation dinsu, har suka gama Amma kwata kwata Bai Gane Ina suka dosa ba, DCP ya Maida kallansa kan lateef yace mlm lateef yace ka gane wannan yarinyar, lateef yay shiru kamar gunki,Yana kallan DCP ,DCP ya qara maimaita ta masa tambayar, lateef yace wa na Gane, DCP yay murmushi yace shafa'atu mana wacce take hayin rigasa, can unguwar da muka daukoka daga can hayin sama su suke,xaka iya tuna shekara Daya da kusan Rabi, yarinyar tana tallan awara ka tareta ka daukota kace xaka siyawa Yan aikinka awarar,.....


Ka daukota ka kawota wannan gidan naka Da muka daukoka aciki lokacin ba'a qarasa ginawa ba,Yana Dan kango Amma kasa gate harma anrufa, kai alokacin ma Saura kadan ka qarasa ginin, DCP yace ka tuna inaso ka qare mata kallo da Kyau, Kuma ma ba saudaya kaje har layinsu kana daukota ba,ka aikata hakan yafi a kirga, kai saida ka lallata mata jiki ma sannan ka Rabu da ita, lateef ya kalli shafa ya Kalli DCP ya qara kallan ta Sosai yaga ko xai ganeta Amma kwata kwata ya kasa kai xancen ma da DCP yake ya kasa Gane inda ya dosa,....


Cikin fushi da bacin Rai ya buga desk din gabansa har Saida su Baba lami da shafa suka tsorata Yace wai officer kana nufin kacemin wai akan yarinyar nan kaje har gidana kuka daukoni kuka tsareni harna kwana anan sannan Kuma iya nan Bai ishekaba sai kaxo ka hadamin sharri ni nai raping din wannan kazamar yarinyar,yar mitsitsiyar yarinyar nan,,wai Dan Allah wanna Irin mutum ne kai marar tunani, da har xakuje ku hada baki kaidasu kuce ni nai raping dinta wannan Wani Irin rainin hankali ne, wlh duk sainasa ankullemin ku na rantse da Allah,tunda harni xakuyiwa sharri ,ya qarasa fada yana huci kamar zai kaiwa DCP duka da shafa,.....


Da. Baba lami da itama cikin shock din da kunnanta suka jiyo mata wai wannan hadaddan mutumin da kudi da hutu da jindadi yake bayyane ajikinsa wai shine yay wa shafa fade haba Tayaya itama saitaji dai kamar dai su DCP mistake sukai, Amma Kuma ai tuna Irin hadaddan gidan da shafa ta nuna amatsayin gidan da akai raping din nata ,ai yafi karfin ace Wani Dan tagajan dinne yayi , DCP ya hade Rai cikin tsawa yace kai kashiga hankalinka kasan agaban WA kake, harni xaka dinga yiwa shouting Dan kaga Ina lallabaka,Dane da ban tabbatar da Mai laifinba, yasa nake daga Maka kafa Amma tunda har ita yarinyar ta tabbatar da kai kai laifin to alhamdulillah, yanxu zabi yarage naka koka karba laifin da ake tuhumarka dashi ko karka karba dolene ayi bincike sosai,..



Idan harya tabbatar mana da kai kai laifin wlh dole ka karbi hukuncin duk Wanda ya aikata rape case akasarnan , sbd haka xabi ya rage naka koka ansa laifin ka kokar ka ansa wannan ruwan Kane,ya Kalli baba lami yace baba tashi a maudaku tunda dai yanxu munsamu suspect dinmu to Alhamdulillah, baba lami da itama hawayen ne ya xubo idanta ta kalli shafa Wacce ke Kuka har lokacin ga jikinta sai rawa yake tace shafa'atu Kin tabbatar da shi yay miki, shafa tace wlh inna shine baxan tava manta fuskar Saba,wlh har yau fuskarsa nake Gani tun daga ranar Daya fara daukata har xuwa lokacin Daya Rabu Dani har yau dana ganshi wlh inna shine,ta qarasa fada tana Mai rushewa da gunjin kuka,...


Baba lami ta rungume shafa itama ta qara fashewa da Kukan, sannan ta?????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? dago ta kalli lateef Wanda ke hararar su kamar Ida nunsa xasu zazzago, cikin rawar murya tace kaji tsoron Allah dama kaina Wanda ka batawa yata rayuwa,ka wulakanta ta, sannan katafi ka barta lokacin da babu mamora ajikinta, ka barta da jinya tsawan shekara Daya da Rabi wacce haryau tana kwance a asibiti,ka kash...kasa qarasawa tai sbd kukan Daya kufcemata, lateef ya mike cikin xafin nama yayi kan baba lami yace ke ya isheki idan kika qara Alakan tani da Wanda yay wa yarki wannan batancin wlh saina batarku a Doron kasar nan, DCP ne ya tareshi,ganin xai iya dukansu a yadda yake dinnan,DCP Kallansu kawai yake yana tausayinsu,yace baba kiyi hkr muje a saukeku,haka suka fita waje, DCP ya Kalli lateef Wanda ya saki baki Yana kallan wadannan Yan kauyen mutanen da har suke Alakan tashi da yayi fade, yace kana nufin kace haryanxu baka Gane yarinyar ba, lateef cikin fushi yace officer ka fitar ni daga wurinnan bansan rainin hankali,wlh Allah idan baka fitar Dani ba wlh saina sa ankullemin kai har duniya ta tashi,ya xa'ayi inbanda jahilci ku kawoni nan Kuma wai Kuna tuhumata da naiwa wannan useless din yar qauyen fyade,ta inama xan ganta da har zan mata fyde,wait,wai tayama kamarni xan iya hada jikina da wadannan da talauci ya gama rarake musu jiki,me xan samu a jikinta,wlh kafitar ni daga wurinnan, DCP ya murmushi yace wato baxaka ansa laifin da ake tuhumarka dashi ba kenan,....


Lateef ya maka masa Banxan kallo, DCP yace well saikai ta zama harsai ka ansa laifin tukunna,daga haka yay hanyar fita daga wurin, lateef yay sauri ya biyo bayansa yace kafitarni daga wurinnan Taya xan ansa laifin da bansan ni na aikata ba, DCP ya kama handle din kofar xaifita lateef ya biyoshi, haka yasa kansa ya fice saidai kafin lateef ya fita har wasu police sun tare shi sun maidashi ciki da kyar suna kokawa suna komai suka datsoshi, lateef ya dinga zaginsu Yana bugun kofar,kamar zai balla Amma babu damar fitowa,suma Basu kulashiba,haka yay ta hauka acikin dakinnan,har yay ya gaji ya daina,...



_________ ?&


Sai Washe gari akaxo xa'a tafi dashi wurin da IG da Kuma Minister tsaro kesan tattaunawa dashi,haka ya fito cikin suits brown ta armless din ciki milk, daya fito da ainihin color din fatarsa,ga sumar kansa data Sha gyara sai daukar ido take, ya feshe jikinsa da tsadaddun tura ruka masu sanyin kanshi haka ya fito cikin nutsuwa ya danna Wani Dan Abu take kofar ta wangale,ya sauka qasa Yana duba agogon hannunsa Wanda ke nuni da karfe shadaya da Rabi,.....


Bayan ya sauka qasa police din Dake jiransa yay sauri ya nufoshi tun kafin ya qarasa saukowa,yay saluting nasa sannan ya gaidashi,ya ansa masa da kulawa,. mutumin yay hanyar fita daga falon, police din ya take masa baya kafin ya qaraso har an Bude masa motar Dake tsakiyar sauran motocin,haka ya shiga gidan bayan motar yana ansa gaisuwar da dukansu suke masa,aka rufe motar ahankali,haka driver sa yaja motar suka nufi hanyar gate din,Wanda tuni Mai gadi harya wangale gate din,da daddaya da daddaya motocin suka dinga fita daga gate din har suka gama ficewa gabadaya,.....


Babu dadewa sukaje wurin Wanda shima jami'an tsaro ne Awajen kamar hauka,haka sukai parking aka Bude masa ya sauko suka mara masa baya, haryaje bakin kofar shiga wurin,anan masu mara masa bayan suka ja burki inda shi Kuma ya shige ciki kansa tsaye ,anan ya tadda su IG,Wanda Suma Basu Dade da qarasowa wurinba,yay saluting nasu tareda da gaidasu , suka ansa masa da fara'a kamar su goyashi sbd Dadi, IG ya qaraso ya rungume shi,yay patting bayansa yace u are welcome My man Ahmad Aliyu Arab wato (AA Arab) nice to meet u ,,...


Shima murmushin yay yace thanks my boss ,daga haka suka saki juna ya juya ga minister tsaro da shima ya ware masa hannu alamar yaje babu musu ya qarasa shima ya rungume shi,yace sorry for what happened to u since a year back &so is not our felt, so we are hopping to forget the issues, so please apologize us,&we nice to meet u,shidai baice komai ba har minister ya gama magana,Saida ya gama Sanna ya dago yay murmushin gefen Baki yace ,Baku kuka min laifi ba,so babu Wani Abu da xaisa na rikeku,Kuma ni tun tuni na bar abin tun time din ya wuce awurina , so da ace ban hkr ba da baxan ansa Kiran Kuba,....


Su IG da minster suka qara fadada murmushinn Dake fuskarsu sukace, thanks, minster yace so have a seat thank u very much,daga haka ya wuce ya samu wuri ya xauna, Suma duk suka zauna, sannan suka fara gabatara masa da abubuwan Daya kawosu Wanda,shine makasudun zaman nasu ,Saida suka tattauna sosai kafin suce gobe idan Allah ya kaimu zasu rakashi Kaduna su dankawa governor shi, Amma kafinnan sai sunje dashi wurin president Wanda shi ya bukaci ganin sa,haka dai suka cigaba da tattaunawa,.....



__________?&


Alhaji sunusi tsaye Wanda ke kallan Hajiya SA'A wacce damuwa ta fito qarara a fuskarta tace Alhaji bakace komai ba, Alhaji sunusi yace wai kina nufin har yanxu wayar lateef din Bata shiga, sannan tun shekaran jiya Bai kirakiba, Hajiya SA'A wacce tun jiya take cikin damuwa tace wlh Alhaji haryanxu, Kuma ni Bai taba yimin hakaba, ko bai kwana agida ba Yana kirana, Amma kaga tun shekaran jiya rabona dashi gashi nayi ta Kiran wayarsa akashe tun jiya,....


Wlh Alhaji jikina bani yake lateef ba lpy yake ba, Alhaji sunusi dashima ya fara gaskata maganar Hajiya SA'A yace Nima tun jiya nake Kiran wayarsa bana samu har Yanxu ma, Amma Gani nake Yana nan ,lpy kawai dai kila yayi nisan kiwone, Hajiya SA'A tace a'a Alhaji Dan Allah kayi Wani Abu akai mana lateef nefa, Alhaji sunusi yace toni yazanyi, Hajiya SA'A tace ka kira mana ko abokansamana, Muji ko suna tare idan ma basa tare ainasan su baxa su kasa sanin inda yake ba Koda ko basa tare ne, Alhaji sunusi yace ni bani da number Daya daga cikinsu Hajiya SA'A ta daura hannu aka, Alhaji sunusi da shima daurewa kawai yake Amma wlh shima Yana cikin damuwar Rashin samun lateef din awayar,yace meye haka , lateef din karamin yarone da zaki ta-da hankalinki har haka,sai kace bakisan halin ShaShan cin lateef ba, Hajiya SA'A zatayi magana wayar Alhaji sunusi ta hau ringing ganin bakuwar number ce yasa yaki yay picking, Hajiya SA'A


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login