Showing 78001 words to 81000 words out of 278032 words

Chapter 27 - JAMI'AR TSARO COMPLET by MRS SARAKIES.doc

23 Oct 2025

1040

da karene ko karya wajen biyawa kansu bukatunsu dasu,Kuma a gsky Wanda yay wa shafa wannan xaluncin gsky shima Yana amfani da kare wajen biyawa kansa bukarsa, to anan ne shafa ta samu wannan cutar,Amma muna sa Ran in Sha Allah idan akai aikin kuma a dace, ruky tace innalillahi wainna ilaihi rajiun ta dafe kanta,sai Kuma ta dago tace cikin Damuwa doc yanxu idan akai aikin xa'a dace,doc Fatima tace so baxance xa'a dace ko baxa'a dace ba,Dan wannan aikin Yana da matukar wahala, shiyasa xakiga ba'a fiya yinsa a Nigeria ba, Nigeria ma ba'a ko Ina ba,so aikin da Kuma samun lpyar ta awurin ubangiji yake saidai muyi addu'ar da patan Allah yasa adace,ruky ta ansa da Ameen,....


Doc Fatima cigaba da fadin Saidai akwai kudi da yawa, Wanda ZA'A kashe ba kadan ba,idan kun shirya zaku iya biya,babu matsala saimu tura da sunan shafa'atu,can xuwa Lagos din,Dan asata a cikin list din wadanda xa'a yiwa , aikin,Dan ba ita kadai take fama da Irin cutarba,idan kikaje asibitin Lagos din inda ake aikin suna nan dayawa sbd abinda ake ta fama kenan yanxu,zamanine Allah ya kawomu yanxu ,sabon Allah yafi yawaita, saidai muyi patan Allah ubangiji ya shirya mana xuri'a, Ruky ta sauke numfashi tace Ameen doc,indai kudine karkiji komai in Sha Allah baxai ga garaba,ko nawane nidai in har shafa xata samu lpy, doc Fatima tace shikenan ASP ,babu komai in Sha Allah, Yanxu zata qara samun cigaba,da samun sauki ,a qarqashin kulawarmu ,tunda kinga Nima Ina xuwa Ina ganin jikinnata,nida doc b,so in Sha Allah babu wata matsala Ruky ta ansa da Ameen sukai sallama cikin girmamawa sannan ta fita daga office din,.....



Bayan fitar ruky tsaye ta samu Khalil har lokacin, Amma wannan Karan Yana tsaye Yana latsa wayarsa ne, ganin ta yasa ya dago daga latsa wayar da yake ya kalleta,yasa wayar a aljihu,ya duveta da damuwa ganin yadda ranta yake a bace bayan ta qaraso kusa dashi yay qasa da murya yace ranki dade lpy kuwa, Ruky ta Dan share hawayen da take gudun karsu xubo Amma saita suka xubo, batareda ta kalli Khalil ba,tace muje waje Khalil,haka tai gaba Khalil ya biyo bayanta cikin tsananin damuwar dayaga ruky acikinta,Saida suka fita daga a department din,suka qarasa wajen wasu kujeru Wanda aka kawata wajen da flowers,ruky ta xauna ganin haka shima Khalil ya xauna, Wanda har lokacin damuwa ne,a fuskarsa, yace ranki dade lpy kuwa,.....


Ruky ta qara share hawayen ta,ta dubi Khalil tace Khalil babu lpy, Khalil angama cutar shafa, Khalil yace kamarya results din baiyi kyau bane, ruky tace Khalil results din Bai kyau yadda ake soba,doc Fatima tace dole sai an mata aiki,aikinma Bai xama lallai ace xa'a samu nasara ba,yace kamar ya,nan dai ta kwashe yadda sukai da doc Fatima ta fada masa,ta qarasa fada da cewa,wlh Khalil dole sainayi qarar lateef dole saiya fuskanci hukuncin abinda ya aikata,dole sai anbiwa shafa kadinta,ta qarasa fada tana Mai Saka tafukan Hannun ta,ta rufe fuskarta dashi,sbd kukan Daya taho mata ,Khalil shima gabadaya jikinsa yayi sanyi,yama kasa magana iya kaci kawai kallan Ruky dayake wacce take rera kukan tausayin shafa, shima Yana Jin xuciyarsa ta gama daukar zabi,jiyake shima kamarya fashe da Kukan,ganin yadda Ruky take kuka,Dan wlh abun da tausayi, nan dai yay karfin halin yin qasa da murya yace please ranki dade kiyi hkr, Ruky Bata Kulashi ba,Saida ta gama Kukanta Mai irsarta Sannan ta dago da kanta bayan ta gama Kukanta,tace Khalil wlh Allah ya Gani Ina tausayin shafa da babarta,.....


Yanxu idan Barbarta ???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?taji wannan xancen baka tunanin xata iya shiga Wani Hali ni wlh kunyar tunkararta ma xanyi da wannan xancen, wannan Wani Irin xalincine lateef ya aikatawa wannan yarinyar, Amma ya mutsike ido yace wai Bai aikataba,bayan sanin kansa yasan shiya aikata, Khalil yace ranki dade ki kwantar da hankalinki,iya binciken da mukai Nima na qara tabbatar da lateef shi yay aikinnan,sbd haka ki kwantar da hankalinki in Sha Allah xamuyi duk yadda kikace, sannan batun Kuma ki fadawa babar shafa,dole daurewa xakiyi,ki danne xuciyarki,ki fada mata, gskyr maganar,Kinga itama saitafi samun nutsuwa idan taji halin da ake ciki tunda tasan cewa,yau results din za zai fito, Kuma munriga da mun fada mata,nasan tanada tawakkali in Sha Allah xata fahimta, ruky ta Share hawayen furkar ta, tareda Sauke numfashi tace shikenan Khalil in Sha Allah xanyi trying,nan dai Khalil ya cigaba da kwantar mata da hankali, kafin daga bisani su tashi su wuce dakin da aka kwantar da shafa Dan xuwa su sanar da Babar shafa duk halin da ake ciki,.....



___________?&


A bangaren AA Arab kuwa, jiya haka Yan uwansa suka Wuni suna nan nan dashi, daga kan su ummi har su ukty,Dan kusan raba dare sukai suna hira,saida ummi ta dage akan yaje ya kwanta Dan ya huta,Dan ya shawo gajiya sannan kowa ya watse Dan xuwa a kwanta, washe gari haka gabadaya ahalin gidan nasu suka fito domin yin breakfast,daga Kan ummi har kan Abba,da ukty,dasu Ameerah, gabadaya suna dining suna breakfast cikin farin ciki da Anna shuwa,Wanda suka Dade rabonsu dashi,Dan suna Jin kamar wani barin da suka rasane ya dawo garesu, babu karar komai Dayake tashi saina spoon, suna jinsu sakawai,kamar Basu da wata damuwa, shima kansa uban gayyar, jinsa yake sakayau kamar Babu abinda ya taba faruwa,dashi na kunci,sbd yau yadda yake jinsa,Wani full man dashi,gashi yau a tsakiyar ahalinsa, suna breakfast abin abin sha'awa cikin farin ciki, kowa ka Kalli fuskarsa asake take da walwala,..



SHikansa AA Arab din fuskarsa sai Wani fitar da annurin farin ciki kawai take,yau gashi a tsakiyar ahalinsa,bayan sun gama breakfast shine ya fara mikewa,bayan ya sauke kofin Hannunsa,ya goge bakinsa da tissue,yace Alhamdulillah Asaman labbansa,ummi ta dago daga cin Irish din da take ta kalleshi tace badai ka koshiba,ya kalli ummi yace eh ummi nakoshi,tace a'a Ahmad ba koshi kaiba, nasan halinka,na kin cin abinci wato har yanxu baka daina Rashin cin abincin nan ba ko,ya Dan rausayar da kai yace ummi agaban kifa,naci abincin da kika xuvamun fa, ummi ta nuna plate din dayaci abincin tace ka gafa ko Rabi baka ciba,yace ummi na koshi ne,kinsan cikina fa karami ne,ya fada Yana shagwabe fuska tareda shafa cikin,ai Mai su ukty xasuyi inba dariya ba,harda Abba da shima yake dariyar,...


Ummi itama dariyar tai,sai Kuma ta Dake tace ai gashinan suna Maka dariya,AA Arab ya wulla musu harara,ya kama hannun abul Daya taso Shima ya biyoshi,ya bar dinin din ya koma falor Yana duba wayarsa da Sako ya shigo,ga abul a gefensa,Yana wasa da gun dinsa ta wasa,ga Kuma ga tv yanayi,bayan barinsa dining din ummi ta dubi su ukty ta hararesu tana cewa,wa kuke yiwa dariya,wlh kunsan halinsa,nidai babu ruwana, Abba ya Kalli ummi da murmushi yace ya xa'ayi baxasuyi dariya ba, fateema ai abin dariyar yay,kina fa ganin yadda kike ta nan nan dashi tun jiya,aikawai hkr mukai, muke kallanku,Ameerah tace wlh Abba ,ummi tace oh Kuna kishi da Ahmad kenan, Abba yace mu bamu ce haka ba, ummi tai murmushi tace nadai Gane,aiko garama ku hkr Dan ,saidai kuyi hkr, Abba ya mike yace ya xamuyi aidama ba tun yau muka fara hkr ba,daga haka shima ya koma falo ya xauna, tareda abla dake kusa dashi,a kusa da AA Arab suka xauna,Wanda ke latsa wayarsa har lokacin, Abba ya Maida tashar Bollywood dakeyi ya koma ta labarai, .....



Itama ummi murmushi kawai tai,su ukty dai sun tashi , suka fara tattare kwanukan suna kaiwa kitchen,kafin ayi wanke wanke,bayan sun gama suka koma falor dukansu, suka xauna aka baje kolin hira Kuma,Dan gidansu AA Arab,babu ruwanasu rayuwar su suke,Mai cike da soyayyar junansu irinta koyarwar addinin musulunci da wayewa,daga iyayensu harsukansu yayan ,idan suka hadu hira ake cikin so da qaunar junansu,abindai abin sha'awa,anan ne Kuma inma da Mai matsala zai iya fadar matsalan sa,ai masa maganinta idan har batafi karfinsuba,...



Suna cikin wannan hirar ne, acikin labaran da akeyi lokaci lokaci suke dagowa,da kansu, su kalla,kawai sai aka nuno cewa,Yan ta'adda sun kai hari Wani qauye Dake nan jihar Kaduna,sun kwashe mutanan ciki, daga Yara har manya daga maxa har mata, gabadaya sai suka nutsu suna kallan labaran, Abba yace innalillahi wainna ilaihi rajiun, yanxu Allah mutanan nan baxa su daina Abinda suke,aikawar nan ba, adai dai lokacin da Kuma AA Arab ya dago daga latsa wayarsa da yake shima ya xubawa TV ido Yana kallan yadda mutane suke kwance cikin jini,....


Wadanda Kuma suka rage aqauyen suna rungume da Wanda aka karkashe,suna kukan a kawo musu dauki,wasu Kuma anmusu yankan rago,ga jini nan sai xuba yake daga jikinsu, ummi tace innalillahi wainna ilaihi rajiun, wannan Wani Irin xalincine, akeyi a jihar nan,su ukty ma gabadaya sun tausayawa wadannan mutane, zuhrah kan uwar tsoro tuni ta makale cikin ummi,....


AA Arab kan gabadaya idansa ya kada yayi jajur sbd bacin Rai, axuciyarsa yace yanxu dama ana wannan xalincin har yanxu innalillahi wainna ilaihi rajiun, Ina jami'an tsaron suke da Basu xoba har lokacin sai Yan jarida kawai,sai Kuma ya dafe kansa, adai lokacin Kuma motar jami'an tsaron ke shigowa kauyen ambulance a Bayanta,kawai saiya dago ya xuba musu ido Yana kallonsu, Yana Jin xafin abinda sukai, yanxu Dan wulakanci tun jiyan Basu xoba sai Yanxu da gari ya waye,ya kalli wayarsa yaga 12pm wato Saida safen kenan suka je,yay tsaki ya mike,....


Ummi da take hankalce dashi tace Ina xaka yace ummi babu inda xani daki zan shiga,ummi tace au ai daukata can din xaka, Abba ya Kalli ummi yace Taya xaije can a'a aiba yau xai koma aikinba, ummi ta sauke numfashi Amma batace komai ba, Abba ya Kalli AA Arab Dake tsaye Yana kallan ummi Abba yace jeka ka huta Ahmad,AA Arab yace to Abba daga haka ya haye sama Dan wlh mutanan nan sun Bata masa Rai shiyasa ma,bazai cigaba da kallo ba, Dan wlh ransa ya gama Baci, yanxu dama haka mutanan kaduna suke cikin wannan tashin hankalin, lallai dole ace ya dawo Dan gabadaya Abin babu kyan Gani ,ba lallai ya cika satinnan da aka bashi ba ,ya koma office,da wannan tunanin ya tura dakinsa ya shiga,....



___________?&

Alhaji sunusi ne, acikin dakin sirrinsa Dake can cikin gidansa na bayan gari,ga wata yarinya wacce take a buge Dan bata cikin hayyacinta svd gabadaya ba'a kawosu cikin hayyacinsu, Dan sai an gusar musu da hankali sannan ake kawo masa su,Dan ita wannan ma batafi shekara goma Sha uku ba yarinyar, haka ya dauketa ya kaita Wani daki daban ,Saida ya gama amfani da ita sannan ya dauketa ya kaita wani dakin,har lokacin yarinyar ba motsi take ba,ya jefata cikin Yan uwanta,da aka kawo masa su su biyar, Kuma dukansu babu wacce Bai anfani da itaba,Dan wannan itace ta karshe (wa iya zubillah)Kuma gabadayansu babu wacce take da alamar Rai atareda ita,...


Haka ya fito daga dakin bayan ya daura Wani Dan xani ajikinsa Baki Wanda baifi daga kugunsa ba xuwa saman guiwarsa,haka ya shiga Wani daki yay sidda barinsa aciki , sannan ya shiga toilet yay wanka ya fito,bayan ya gama shiryawa cikin babbar rigarsa,ya fito falor rike da wayarsa Dake ringing,...


Ganin babajo Ali ne ke kiransa Yay picking daga Daya bangaren babajo Ali ya kece da wata dariya, Alhaji sunusi yay murmushi yace babajo wannan dariyar fa,ta samu kenan, babajo Ali ya tsagaita da dariyar da yake yace honorable aidole nai dariya ,kunna TV kaga aikin su goga,babu musu Alhaji sunusi ya kunna TV Dake falon cikin farin ciki shima,bayan ya kunna haka ya xubawa abinda yake Gani ido Yana murmushi, Saida ya gama Gani yace shege goga,wato aiki indai dashi ne,babu na dama, Yana cikin wannan tunanin Kiran babajo Ali ya sake shigowa wayarsa Nanda nan yay picking,babajo Ali yace yaka Gani ,Alhaji sunusi yay dariya harda kyakyatawa yace komai yayi yadda muka tsara, lallai goga Dan iskan kansa ne, Babajo Ali yace kwarai kuwa aiki dashi babu nadama, ai dole mu Kara musu kudi, Alhaji sunusi yace wannan haka yake babajo,...


Babajo Ali yace nasan yanxu governor da wannan AA Arab din sunga wannan abun, Alhaji sunusi yace sosai ma, babajo Ali yace to wanna shine sankonsa na farko,Dan wannan sakon na AA Arab ne,Dan yasan cewa,babu gudu babu ja dabaya,mun shirya fito na fito dashi, Alhaji sunusi yay dariya yace dadina da kai babajo akwai tunani me kyau,...


Babajo Ali yace ai wlh tafiyar war dasu yallabai taju sukai dashi muma ita xamuyi dashi,Dan wlh saiyayi kuka da idansa, indai da mu xai Kara muxuba mugani,wlh MaiTama sai mutanan kaduna ma,sun tsaneshi wannan soyayyar da suke nuna masa Saita koma kiyayya,Dan zagon qasa kawai zamu musa, Alhaji sunusi yay dariya yace wannan haka yake babajo,wlh yarannan saiya San da manya kawari zai Kara, babajo Ali yace wlh saiyayi kuka da idansa Dan aikinnanma yanxu muka fara, Alhaji sunusi yace kwarai kuwa,Dan sai mutanan jihar Kaduna sun rasa matsugunni,dan nan gaba ma cikin gari xamu fara kawowa hari, yadda xasu tsani governor dashi kansa wannan tsinan nan yaron, Kuma haka zasu kyalemu su hkr su kyalemu harshi kansa yaron ya koma inda ya fito,babajo Ali yace wlh harna hango ranar , Alhaji sunusi yay dariya,haka Suka cigaba da tattaunawa akan yadda xasu cigaba da bullowa da sabon tashin hankalin da xai hana su AA Arab kwanciyar hankali,......





*Masu San a tallata musu hajarsu xasu iya Yin magana ta wannan number Dake qasa*






07066508376________
'?Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DC2ekqRnajZAQQvErdaWfD







*____JAMI'AR TSARO ____*



*____THE WOMEN POLICE ____*




*NA*



*____NAJA'ATU UMAR FAROOQ ____*



*____(MRS SARAKIES)____*



*=?1?QUEEN OF WRITERS ASSOCIATION (QOWA)=?1?*



*Bismillahirrahmanirrahim*



_______season one ep 3?? 4??



_________?&


A yaune Hajiya SA'A suka shirya kaiwa lefe gidansu ruky, washe gari Kuma ya kama ranar da xa'a daura auren lateef da Rukayya, akwatuna ne guda goma Sha biyu,kowacce cike take da kaya na gani na fada Dan lefenma a Dubai Hajiya SA'A ta Bada order su akayo, duk da Batasan auran Amma Kuma baxata so ace sunyi kaya wadanda ba nagani na fada ba, bataso aga karantarsu,xataso ace sunyi kayan kece Raini, Wanda duk Wanda ya Gani saiya Yaba,Kuma badan kowa tai ba, saidan lateef,Dan da ne Mafi soyuwa a wajenta,....


Wajen karfe uku aka shirya xa'a kai kayan,Wanda wannan Karan ma su Hajiya mansura ne xasu kai kamar yadda suka kai wancen na sa nanar aurenma, Kuma wannan Karan dinma ko mamah Basu kira sun fada musuba,karfe uku tana cika suka tafi kaiwa kayan , motoci biyu akayi Daya akwatunan akasa aciki,Daya Kuma su Hajiya mansura ne aciki,karfe uku da Rabi ta kaisu ,bayan sun isa haka suka sa masu aikin gidan Maza da driver da suka xo dasu suka sa su shigar da akwatunan ciki,babu musu suka shiga fiddo da akwatunan daga cikin motocin, suna direwa kasa,Saida suka fiddo dasu tas sannan suka fara daukar su Daya bayan Daya suna shigar dasu ciki,...


Babu kowa a falon sai karar TV sai Kuma hanaf Dake kan dining Yana cin abinci dan baidade da dawowa ba,gefe Daya Kuma yana latsa wayar sa,dawowarsa kenan daga wajen aiki ,mamah batanan ta fita makota dubiya, tareda baba hasiya Dan Basu Dade da fita ba,Yana gidanma suka fita,ganin anyi sallama yasa ya ansa , tareda da kallon wadanda suka shigo ,sai Gani yay ana shigo da akwatuna, kawai saiya tsaya yana kallansu, da mamaki baiyi magana ba,Dan ya fiso yaga su waye masu akwatunan,Saida mutanan nan suka gama shigowa da kayan tas ,sun kawo na karshen ne,saiga wasu mata sun shigo Wanda Bai sansuba,sai kalle kalle suke Yi,ko Wacce taci kwalliya cikin shiga ta Alfarma....


Sun shigo bakinsu dauke da sallama ya ansa musu a saman labbansa,ya kafesu da ido, Hajiya mansura cikin murmushi tace ku zauna Hajiya,matan da sukazo tare suka samu wuri suka xauna ko wacce tana Dan kalle kalle, Hajiya mansura itama ta xauna, itama ta fara kalle kalle ganin babu kowa kusan mintuna biyar ,ga hanaf ko ta kansu baibi ba,yasata cewa hanaf Dake kan dining Wanda ya dauke idansa daga kansu tun tuni, Hajiya mansura tace Dan samari Ina mutanan gidanne,hanaf yay Banxa ya kyaleta saima daukar cup din ruwa daya xuba yay ya kai bakinsa,tace Dan samari magana nake nace Ina Hajiya Halimar ko tana ciki ne,....


Hanaf ya juyo Jin ta ambaci sunan mamah, calmly yace batanan, Hajiya mansura tace to Ina ta tafi bayan tasan yau xa'a kawo kayan lefen Rukayya da lateef,hanaf ya aje kofin Hannunsa,ya taso ya nufi falon hannuwansa Daya cikin aljihun Wandansa daya Kuma wayarsa ce a Hannunsa, cikin mamakin xancen Hajiya mansura, hanaf yace wanne lefen Kuma, Hajiya mansura tai murmushi tace lafen dai lateef da Rukayya,ai nasan Hajiya SA'A ta kira ta ta fada mata xuwan mu,....


Hanaf yace gsky a'a Dan mudai bamu san wannan maganar ba,Dan babu Wanda ya bawa lateef auran Rukayya,hasalima kaf gidannan babu Wanda yasan xancen nan, Hajiya mansura cikin Dan daurewar kai da mamaki tace a'a kodai Kaine bakasan xan cenba, Amma ai kwanakima har kawowa kayan tambayar mukayi da Kuma
Kudin AURE,kodai Kaine Hajiya Halima Bata fada Maka ba,hanaf ya qara hade Rai yace a'a badai anan gidanba,may ko kunyi batan hanya ne, please ku tashi ku kwashe kayan nan ku fita dasu, ya fada Yana nuna musu kofar fita, tareda tsaresu da ido,Hajiya mansura ta hade Rai tace kai bama san Rashin mutunci,Ina Hajiya Halimar take,aiba gunka muka xoba wajenta mukaxo,....


Hanaf shima haderan yay yace Kinga MALAMA ku tashi ku bar mana gida wlh tun kafin nasa afitar mun daku,ku tashi ku kwashe wadannan useless boxes din naku,kuje ku fadawa Wanda ya Aiko Kun cewa,ni hanaf nace mu baxa mu bawa Dansa auran kanwar muba, Hajiya mansura ta mike ta nuna hanaf da yatsa tace kai karka kuskura kamin Rashin kunya,niba sa'ar ka bace, tace dama Hajiya SA'A tasan basu fadawa Hajiya Halima cewar xamuxoba ,kawai tasa mukaxo yaro karami Yana mana Rashin kunya ta kalli sauran matan Wanda suke kallan hanaf da Mamaki tace ku tashi mutafi,wlh hajiya SA'A Bata kyauta mana ba, gashi yaro karami yaxo sai gaggaya mana magana yake,shiko hanaf ko a jikinsa ya fita ya kira Wanda suka shigo da kayan yace su kwashe su ,su Maida inda suka dauko,haka suka kinkimu akwatunan suka kwashe tas,....


Su Hajiya mansura tuni sun fita daga falon sun Yi waje sunata,


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login