Showing 141001 words to 144000 words out of 347556 words

Chapter 48 - KARAN DAFI HAUSA NOVELS By Zainab Makawa.doc

24 Sep 2025

8749

KO A KIRA WANAN LAYIN WAYAN 08036959257 NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE NAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , ,

YAR UWA KADA KI RAINA NAUYIN HAKKIN WANI A WURIN ALLAH DON MIN AMANACE HAKKI, , , , , , ,


HAKKIN MALLAKAN JUYAWA AUDIOVISUAL S ZARIA TV KEDA WANAN HAKKIN KADA WANI KO WATA YAYI GANGANCIN JUYASHI ZUWA AUDIO.

Zaman jiran Abbas na wani tsawon lokaci don ban samu ganinshi ba sai hudu da rabi ashe yana cikin wurin meeting din suna tataunawa kan kasuwanci don shine marketing manager dinsu gaba daya.
Tun daga nisa yake min kallon mamaki a inda nake zaune din, har karaso yana rike da yar karamar counter yana dannawa a hannunshi fuskanshi da alaman annurin sallah lokacin.
Hakan yasa na gane daga wajen sallah yake ke nan har ya karaso inda nake yana mamaki karara a fuskanshi kamar zai wuce sai kuma ya tsaya ganin na sada kaina a kasa yasa ya dan dawo baya.
Cikin mamaki yake fadin wai baki tafi bane har yanzu kina nan me kike jira har wanan lokacin a nan ?
Nima mikewa nayi ina fadin dare yayi kuma yau zan koma gashi har yanzu ban samu ganin Mr Abbas dakace nazo na ganshi ya bini da wani irin kallo ganin yadda raina ya dan baci har ina iya baiyanashi a fuskana lokacin.
Wayan Abbas din ya tsaya nema wayan yana kashe hakan yasa shi dan jan guntun tsuki yace bari nazo ya wuce har ya fara tafiya ya juyo yana fadin kinci abinci kuwa ?
Kai na iya girgiza masa ya juya zuwa office din shi bai dade ba ya fito da key a hannunsa a daidai lokacin kuma shi Abbas din ya fito ta wani hanya na daban da mutum ba zai sanda cewa akwai ma hanya a wurin ba ashe hanyar store din sune.
Kusan tare suka karaso Abbas ke dadin sorry shaf na manta dake a nan zaune zo mu tafi yace ba tare daya tsaya kallon Abbas din ba dake magana don haka nima na bishi baya da sauri.
Motan shi muka shiga zuwa wani gidan cin abinci mai kyau nan yan aikin wajen suka zo suna gaida mu tare da mika mashi takarda yace su ban in duba.
Duk a rude nake lokacin amsa nayi ina dan dubawa ba naga fried rice da chicken meat sai ruwa shina ce a kawo min shima ya karba ban san meya fada ba tunda baka jin magananshi sosai don yana da dan saurin magana haka don haka ni ban gane me yake fada idan yana magana .
Kamar i,i,niya kamar saurin magana haka dai nake jinshi wani lokaci duk da tsadan fidda magana gareshi ba ko wani lokaci yake magana ba.
An kawo abincin na dan dago kai lokacin shima ya dago nasa kan da tun zaman mu yake duban waya yana kallon abincin da aka aje min din a gabana.
A lokacin wanda ya kawo mashi nasa yazo tuwone na gargajiya tuwon shinkafa miyar ganye yaji agushi sai nama manyan yanka manja yasa miyan juya wani kala dashi haka.
Kunya da nauyi irin na ya mace bai bari na iya cin komai ba a wajen duk da shi ya fara ci wayanshi yai kara ya tsaya karba wayan har yakai ga dan mikewa wurin hakan yasa na danyi kokarin ci kafin ya dawo sai dai ina kaiwa a baki najishi wani iri sam bazan iya cinsa ba hakana drinks din na dauka nasha na zauna jiranshi ya dawo.
Ya dan kalleni ganin ban wani ci abincin ba yasa shi fadin ba zakici bane kuma kai na girgiza nace naci na koshi ya dan taba nashi din sai kuma ga waya ya dauka.
Yana fadin na fada maka banji dadin yadda kuka bar yarinyar nan hakana ba kasan halim mutanen mu don me ba zaka sallameta ba tunda tazo.
Hannu naga yana wankewa ya dan dago yana fadin rashi muje munkai kofa ya tsaya biyan kudi na isa wurin mota na tsaya ina jiransh sai gashi da ledoji an biyoshi baya ya bude bayan aka saka mai ya shiga nima na bude na shiga na zauna a takure wuri daya.
Har muka fara hanya waya yakeyi da wasu wani wuri naga an rubuta A,A Guest motels da manyan haruffa na bakaken kalma.
Ina dai kallon ikon Allah yace bari na danzo yanzu ya fita ya barni zaune a motan ina faman kiyasta irin abinda zanyi a lokacin don ban gane me hakan ke nufi ba dani gani da fahintar danayi wurin hotel din kwanane.
Can sai gashi ya dawo ya shigo motan ya dauki wanan ledojin daya sayo gidan abincin nan yana fadin ina ganin nan da dan dama zaki kwana a nan din da safe zanzo in daukeki sai kizo ki wuce gida .
Nagode na fada cikin makyarkyatan baki ya bude ya fito nima na fito din daga motan ina dan kale kalen wajen muka shiga ya wuce gaba har dakin da aka bani din bai shiga ba yace take care nace nagode ya fara tafiya ya dakata yace idan da wani matsala you can can any one of my number ki rike wanan katin ya miko min dan karamin katin waya na amsa ya tafi na rufo kofan sai lokacin nake bin dakin da kallo.
Dankari nidai a sanina ban taba kwana wano waje da yakai wanan wajem ba gaskiya gadone babba yaji shimfida sai abin kallo da dan madaidaicin fridge ga mirrow babba a gefe daya.
A hankali na taka zuwa bakon gadon ina aje jekkar hannuna dake rataye min a cikin jikina tare da warware gyalena na dora saman gadon.
Kafin na duba hanyar bandaki na nufi can a hankali na fara tura kofan ina lekawa ba laifi shima ya hadu da komai da ake bukata a kwaishi cikin.
Polishing na danna don nasan kalan hakan a gidan maman saudiya kana na dan watsawa bath din ruwa shima na fara tsarki kafin na dauro alwala na fito na fara saka wayata a caji kafin na fara.
Dan dube duben yadda zanyi sallah na fara a dakin don wurine da musulmi da kafirai ke amfani dashi don haka na koma daga can karshen gadon na tayar da sallah na rama sallolin da ke kaina kafin na zauna bayan addua ina tunanen duniya a kaina.
Shin dan banda uwar da zata kwaba min ne rayuwana yake tafiya a hakan kome da ace Allah ya kaddareni da shashanci a rayuwa ta hakan zan famfare in zama gurbatatta da kowa zai sheda hakan gareni.
Iya kata dai da mahaifiba shine fadimatu na yarda da tarbiyan ki kikara rike darajanki a duk inda kike ki rike mutuncin ki da kimatki ta ya mace.
Gqaggo kuma diyan nan Allah ya kai lafiya a dawo lafiya Allah ya tsare ya kare shine adduan tsakanina da ita yau da ace zan bi rudin shedan in fada wani harkan banza kokai kudin nayi haka za a karba ana saka min albarka.
Na dade a zaune ina tunane don yamma yayi magariba ya gabato sosai lokacin don hakan yasa ban kwanta ba nake jiran lokaci.
Komai baka ji a ginan dakin ko ruwa ake ko rana ko wani hayaniya mutum ba zaiji ba don haka ko kiran sallah saidai mutum ya duba lokaci kawai ya kwatanta yayi.
Hakan nayi bayan na duba time na tabbatar magariba yayi a lokacin na tayar da sallah na idar har isha,i kafin na mike zuwa bakin gadon na zauna na fara sabon tunanen banzo da komai na amfani ba a lokacin.
Ledojin nan daya shigo min dasu na kalla na jawo ma fara budewa naga hadin fruits salad ne ashe a ciki da wasu yan kayan ciye ciye haka.
Na bude dayan shi kuma snacks ne sai soyayyen naman da banci ba aka zubo min mai yawa a leda daukan komai nayi nakai cikin fridge din nan da ba komai a cikinsa amma yayi sanyi sosai haka nasaka na rufe na dawo na dan kwanta a takure waje daya.
Misalin tara naji ana min nocking din kofan gabanane ya fadi na mike zubur ina saurarawa tabbas kofanne ake kwankwasawa lokacin .
Can na nufa tare da dan duba wani kafa da zaka iya ganin maishi nan na hangoshi shi tsaye a kofan tambayan kaina nayi da meya kawo boss kuma again.
Jin an kara nocking yasa nayi saurin budewa ashe shida Abbas ne tsaye yana saye da jallabiya fara tas a jikinshi da wani plat din takalma a kafanshi.
Sai kamshi ke tashi shima Abbas din kuma yana sayene da wani wando crazy sai wata yar riga fara mai manya rubutu a jikinsa an rubuta Nice day.
Sannun ku da zuwa na fada cikin dan murya suka amsa Abbas ke fadin sorry fa Fatima naja maki kwana Abuja baki shirya ba ganin alaman kamar zasu shigone yasa na dan kauce a hanyan na koma gefe daya na rakube a wuri daya.
Sai lokacin da suka karasone naga ashe da kayama suke a hannunsu kinyi sallah dai ko shi boss din ya tambaya na amsa da eh nagode.
Kayan Abbas ya dora min saman gado kafin shima ya aje na hannusa yana fadin ga yan kayan amfanin ku nan na mata an sayo don kinja min fada yau wurin shugaba sosai fatima.
Dan murmushin bazata nayi lokaci guda nace ai kunfi kusa ba zaima fada ba a kaina yau akasi aka samu kawai to kaji kai.
Na fadama kanwatace yadda ka fusata ba zata dauka hakana ba yanzu kaji ai nace ai kanwa bata taba fushi da yayunta yace kwarai kuwa.
Fatima kinci abinci dai ko Abbas din ya fada da sauri nace dajun da zamuzo nan naci me kikaci Bashir ya fada min kin kasa cin abinci ko zamu fita a duba gari koda abinda kike so yanzu kici.
Ki daina abu kamar bakuwan fulani mana zo mu dan fita saiki daga garin No ba sai taje ba ta fadi abinda take so a sayo mata mana ya fada shi kuma Abbas din yace tazo dai mu fita don taga waje saboda gaba.
Tare dasu din muka fito daga ciki Abbas ke ja yana gefe daya muka bar cikin haraban hotel din mun dauki titi naji yace me zaki tafiyi saudiya har tsawon wata biyu ?
Bangane meyake nufi ba saida shi Abbas yake fadin kanwa dake yake yana tambayarki nace zan tafi wurin wata mamatace dake can itace ta aiko naje.
Kin tabbatar ita din mamakice daiko don yanzu duniya bata da tabbas kada sai kinje kuma zance ya canza a can din don da yawa haka ke faruwa dasu a can.
Eh ita din da maigidansu da yaransu duk a can suke zaune unguwar mu daya a nan kaduna mun dade tare dasu nasan kowa nata sosai.
Ke nan ba yan uwa kuke ba shine zaki bar gida ki tafi wajenta baki jin tsoron wani abu yaje can ya faru dake ya fada tare da dan juyowa yana kallona inda nake zaune a bayan mota.
Insha Allahu yadda kake zato ba hakan bane itace mace ta farko data nuna min kauna tsakani da Allah tasoni a yadda nake ta fitar dani kasa magana nayi na dukar da kaina kasa.
Hawayene yazo min lokaci guda badon komai ba sai tuna irin gararanban da nake fama na kuma taso a cikinsa tun ina karama dani.
Baida matsala ya sunan maigidan matan a can nace kamar Alh Adamu kabir daura tsohon ambassador tace min au gidan Ambassador Daura ke nan ?
Abbas ya fada tare da fadin can ke nan zaki ashe ai munsan su sosai ma kuwa yan uwan su,,,, kai ya isa hakan don Allah ya fada daga inda yake zaune.
Ka kaimu a sayo mata pizza da ruwan zafi ya kawar da kanshi gefe daya inda yace din ya kaimu aka sayo komai suka juyo tare dani duk dai bansan meye a acikin uban ledojin da aka tara min ba din.
Saida suka kaini har dakin da na sauka din sukai min sallama suka tafi ina godiya kayan farko na fara budewa nasha mamaki don suturan canzawane a ciki komai da zan bukata da safe yana ciki.
Sai wanan din kuma shine nau,in ciman yan birni da suke kashe miyau a yanzu nako zauna naci sosai na kora da wanan fruit salad din da yai sanyi lokacin na dauko tawul na daura nashiga ban dakin na watsa ruwa tare da alwala ban kwanta ba saida nayi nafila na roki Allah abubuwa da dama a rayuwata.
Tunda na kwanta da farko ina fargaba don haka na kasa kashe wutan duka na dan bar dum light yana haska dakin da barci ya daukeni kuma sai nasari a lokacin.
Washegari karfe shidda da wani abu na falka wanka nayi kafin inyi sallah ina idarwa na shiga har hada kayana tsab na sauya na saka daya daga cikin sabon da suka sayo min din.
Nayi packing din komai ina jiran shigowan su karfe takwas sai ga Abbas yayi nocking na bude yake fadin dama Bashir ya fadi nazo yasa kin shirya yanzu.
Eh tun dazun na shirya ai ina kwana na fada a lokacin ya amsa da lafiya ya dare kuma nace lafiya kalau Alhamdullahi.
To mu tafi ko kingama shirya nace eh ina kara bin dakin da kallo ko nabar wano abu ban kula ba a lokacin shiya tayani daukan ledojina muka fita ya mika masu key din dakinsu.
Muka nufi wajen motanshi kai tsaya yasa komai a sit din baya ya bude min na shiga shima ya zagaya ya rufe kofan ya tayar da motan muna barin haraban gidan kwanan yake fadin.
Watau hjy Fatima ina mamakin sa,an da kika taka akan boss din mu sosai wallahi don watau yana bawa lamarinki muhinmanci fiye da zaton kowa.
Jiyan nan kinji irin fadan da yai min akanki kuwa sai gashi kuma bai zauna ba saida yazo yakara ganin ko lafiya a nan din inda ya kawo ki don kwana dayan nan kawai da kikayi a ciki dubu saba,inne kudin daki daya a nan din .
Nace wanan wurin yace kwarai kuwa kinko san ai to bari dai inyi shiru ko yanzu ma yau ya tashi baijin dadine shine ya dameni da kira nazo don Allah na daukeki nakaiki ki karya a kaiki tasha ayi maki shatan mota zuwa kaduna ko zaria.
Subbahanallahi baida lafiya kuma yace wallahi dazun da safe daya kirani yake fada min ya kwana da ciwon kai mai tsanani bai iya fitowa yanzu.
To amma in ba laifi sai ka kaini nagaidashi don Allah kafin in wuce kada kuma kuga wautana ga haka tunda naji ko iyalinsa zasuyi fadan hakan idan naje.
Kai kina bawa mutum dariya Bashir ko budurwa baima taba yi badai saidai abokai irin na turawa masu nacin tsiya din nan kosu basufi a kirgasu ba gaskiya.
Bari to na biya dake duk da nasan zai mun fada kan hakan amma dai tunda kina son zuwa bari muje ki gaidashi din hakan zaifi.
Duk da nasan zaiyi fadan haka din amma muje ba matsala nima zan samu in wanke kaina daga wasu abubuwa a wurinsa ai dayake kallona dashi.
Kinsan idan ace maki yau mutum nadashi ko shi din wanine sama dakai to duk yadda kuke dashi dolene kai na bayansa ka kwanta masa don baiwan nan da Allah ya bashi.
Nasan bakisan ko waye bashirba har yanzu duba da yadda Allah ya dora mashi tausayinkine ko kauna bamdai gane wani rukuni kika shiga zuciyar shi ba har yanzu.
Don ba mutum bane shi mai saukin kai da za ai saurin hintar inda ya dosa mai yuyuwa wani manufa ko nufi ne naki a kansa duba ga yadda ya dauki lamarin naki a yanzu.
Don haka shawarata a kanki shine ki bishi a sannu har lokacin da zamu fahinci zuciyar shi akanki yanzuma idan munje na tabbatar da zaiyi fada don sanin ko waye bashir da nayi fiyema da wani dan uwa nasa na jini dake tare dashi.
Na yarda in ance nakune yazo daya yanzu dashi idan na fadi hakan banyi karya ba duba ga irin matan dake tare ko a cikin family dinsu amma bai kula kowa kamar yadda ke kika samu yana dan kula dake a yanzu din.
Idan da zasu samu hakan gaskiya da yanzu yakai ga matsaya a zuciyanshi saidai sam basu samu hakan gareshi ba sam don hakama har suke masa zargi da wani manufa.
Jin hakan yasa na dan kalloshi cikin mamaki yace ehh kinsan mutane da zargi ai sun dauka ko zaman shi a turai yasa ya fada kungiyar da ba,ason dan musulmi ya shigane mu a nan.
Zargi kala kala suke masa yanzu wanda ninasan ba hakan bane amma sun dauka har nima din a yanzu haka nake tunda muna tare dashi tip da taya don haka suke daukan nima hakan nake ai.


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login