Showing 96001 words to 99000 words out of 347556 words

Chapter 33 - KARAN DAFI HAUSA NOVELS By Zainab Makawa.doc

24 Sep 2025

8756

shiga gida na samu gwaggo ta fara aikin abincin dare a gurguje na aje dan gyalen dana yafa a kaina na bakin rigar dake jikina lokacin.
Kayan na wurga saman katifa kana na fito ina sake fadin gwaggo sannu da gida munje mun dade harkin fito ban samu nan kusa bane shine muka taka har wani layi da kafa kuma.
Ina dai an samu abin ko ta tambaya tana dagowa nace kadan matane mun siyo zamani yanzu akan kada kukayi wanan uwar tafiyan a kasa ?
Dariya nayi na karfi kwaryan datake rigan shimkafan hausa a hannunta tare da dukawa na fara wankewa don kunyan zancen nake da kowa ko fadinma subul da baka nayi banyi niyar fadaba baro baro haka a bakina.
Saidana gama wankewa na zuba na juya na karbi dakan kayan miya da takeyi lokacin Samira ta shigo gidan da sallamanta na dago kai na kalleta.
Kayane niki niki a hannuta tayi dakin mu dashi ba tare datayiwa kowa magana saida ta dan jima a dakin ta fito tana gaida gwaggo ta dauki buta ta shige bandaki .
Ta fito take fadin wai fitsarine ya koroni gwaggoce ta bata amsa da fadin fitsari ko baida dadi idan ya taruma a mara sai nakusa dakai ya gane hakan..
Bata tsaya ba ta juya ta sake shiga daki har na gama komai na kwashe tana ciki na shiga na cire kayan in watsa ruwa na sameta kwance shame shame tana barci ga guntun cake da taci a hannun ta sai goran yought na kwali mai bafulatana data sha a gefe.
Kaina girgiza ina mamaki irin rayuwan Samira don wanan rayuwan data dauko karshensa bazai bullo a hanya mai kyau ba gareta.
Ita dai a yanzu na fahinceta kamar ta samu wani freedom din kantane tana abinda taga dama ba tare da tunanen abinda zai tafi ya dawo ba a rayuwanta.
Fita nayi naje na watsa ruwa na dawo har lokacin tana a yadda na fita na barta kwance jin motsina yasa ta dan bude idonta tana gyara kwanciyan ta.
Amma kinsan magariba ya kawo jiki barcin nan bai dace ba a yanzu mika tayi tana fadin wallahi ban ma san barci ya daukeni ba a haka ashe nayi barcinema ?
Zaune takai tana sakin hamma tayi mika tace how lucky you are Bantu wai kinsan wanan guy din daya biyoki sojane harda security dinsa ashe wurin.
Nasani na fada ina saka riga a wuyata au kin sani ashe nace ya fada min wai sojane shi to ina ruwana da hakan ya sai min abu nayi masa godiya shike nan ya tafi tunda ban aikeshi ba.
Dagowa tayi da kyau tana kallona wai bantu kanki daya kuwa waima dai kinada lafiya kuwa ni abinki ya fara bani tsoro don kin barni da Ayan tambaya a kanki ?
Kince yan gidan hjyn saudiya kaf ba soyayya kike dasu ba haka kuma bawan Allah nan ya Mahmoud yazo kin fatatakeshi kin masa kora da hali.
Yanzu kuma wanan hadaden abin son kowa yazo kince baki da ruwa dashi shima koransa zakiyine bantu don nikan har na bashi address din gidan nan daya tambaya.
Fuskana daure sosai na dago ina fadin don me zaki mun hakan ni ba wasa nazo yi kowani tsaya bata lokaci da wani ba karatu ya kawoni kuma shi zanyi in koma.
Don me kikeson mu tsaya mu dinga shiririta a kullun ki tuna da yadda su mama sukasha fama da baba kafin ya yarda muzo karatun nan kin sani sarai yadda mama ta kushe lamarin zuwanmu nan karatu.
Yanzu kuma me nayi don kawai na kula masu ra,ayina shine laifina kowa da irin rayuwansa don ko karatun ai yana son hutu ba aka abu guda kamar cin kwan mahaukaciya ba.
Ni dai ga kayan nan shiya saya maki yace na kawo maki kuma yana nan tafe naso daukan wanan turaren amma sai naji tsoro saboda kayan sojane.
Kin ko san soja ba mutuncine dashi ba don haka ga kayanki tana miko min turaren data dauka ta boye a bayan filo.
Dariya ya kubce min nace aiko yanzu baki tsiraba don ko na fada maki ko ina bazan fita ba kinga ashe baki tsira daga tarkon sojaba har yanzu.
Kinama farashi dolema ki fita wallahi ko ya aiko cikon gidan nan a sungumeki akai masa ko banza kinsan zaria da yan daukan amarya balle kin kaiga soja.
Ki sandai yadda zaki karata dashi idan yazo kayan ta kara kallo tace talauci baiyi ba bantu wai ki duba mutumin nan katinsa ya bayar aka zare kudin kayan nan da wanda shima ya sayawa kanshi.
Bari batun wasa ya wuce Bantu guy din ya hadu ya gama haduwa hundred percent gaskiya ni da nice ke yau sai na nafi kowa a duniyan nan farin ciki.
Ai bai baci ba ko yanzu zaki iya sanin yadda zakiyi sai kuci gaba dashi don zaifo masa sauki gaskiya ke rufamin asiri nifa duk shegantakana na fatar bakine dama.
Kiran sallah aka fara a cikon gari ko ina ya dauka dadin arewa ke nan dama yaren hausa da addinin su a tare suke tafiya don kusan dabi,un malam bahaushe fiye da kashi tamanin cikin dariya yana tafiyane da koyi da musulnci.
Don haka muna jin kiran kowa ya mike har ya nufi bandaki saidana kewaya naga bana sallah a ranan don haka nayo tsarki na dawo daki na zauna.
Sai alokacin na kai kallon wurin kayan zancen Samira na tsoron sojane ya fado min a raina yasa har na dan murmusa a fuskana na jawo ledan gabana ina kallon kayan dake cikin ledan dako wani ke rubuce da kudinsa dan like da dan farin takarda.
Kayan suna gabana na fitar inbi da kallo har pad din nan danaje saye na dauko leda daya tal shi saida ya sako min packed din guda biyu ashe akalla zanyi wajen shekara ban fita sayen always ba ke nan.
Mahaukaci na furta a fili kafin na mika hannu na dauko wani kwalin turare ina kallo yafi wancan daya mika min da hannusa kudin sa na duba daidai Samira na shigowa dakon daga alwala nace mata wanan yanada hankali kuwa ?
Waye ke nan ta tambaya nace wanda ya sayi kayan nan mana meyasa maza suke hakane ta duka ta dauki carpet din sallah ta shimfida tana fadin kan abinda sukeso ba.
In haka suke ya sawa ko wace mace daya gani a cikin shagon wanan abin kece dai yayiwa bajinta don ya gani shima ya kyasane.
Ciwo mara na kwana dashi sosai don haka ban samu fitowa da safe ba don maganin da nake sha idan inayi yakan sakani barcine sosai idan nasha.
Karfe biyu saura na tashi da kyat ruwa na diba naje bandaki wanka nayi na gyara jikina na fito zuwa dakin mu na samu har lokacin samira bata dakin ta fita tabar wayanta yana ta ringing.
Ban dauka ba na barshi harya katse can sai gata ta dawo lokacin ina shafa mai a jikina dauke da yar leda karama fari a hannunta tana miko min nace meye wanan kuma ?
Ki karba mana maganine a ciki aka sayo maki dazun yazo gidan nan kina barci shine na fita na fada mai yace ace kizo kuje asibiti nace baki iya tashi yanzu kika samu barci.
Shine yanzu aka turo driver ya kawo wanan maganin na fita na karbo maki ga yadda zakisha nan an zana a ciki amma sai kinci abinci zakisha.
Kallon mamaki nake mata da kyar na samu na bude bakina nace samira kika fada mashi period nakeyi don Allah ?
To waye baisan kinayi ba dama idan baki period ai abu ya lalace ke nan kuma don Allah karbi kisha da wanan wahalan da kikeyi bakiga yadda ya damu bane dana fada mashi.
Karba nayi na aje maganin gefe daya nayi kwance rigingine ina tunane can maran ya yanka min na nade ina murda baki tare da yarfa hannu ta tashi ta dauko min ruwa ta miko min maganin bayan ta baresu ta hada ta miko min bansan lokacin da nasha ba.
Bayan dan wani lokaci ya lafa min sosai har wani barcin ya kara daukana kodana tashi banji komai ba saidai jinin dake dan min rushing alokacin.
Naji dadin maganin sosai amma duk da naji sauki raina yana baci yadda rashin kunyar Samira ya fallasani a duniya don haka nasha Alkawarin cewa ba zan taba yarda mu hadu da wanan mutumin ba.
Rayuwa a yanzu yana da kalubali da yawa cikin mazan ko cikin mata gun yara ko kuma manya kai har ma da wasu tsofafin zamani.
Yau idan kai ba kowa bane ko kana da baiwa sai kaga mutanen cikin duniya basayi dakai sai idan kai din wani celebrity ne zakaga mutane suna manne maka.
Irin hakan ne nake fuskanta a yanzu lokacin da nake motsu motsu yar suyar awara lokacin duk da ina kawo wuta aji amma ba mai shiga tsabgata dan dama dama matan auren ajin muna dan mutunci dasu sama sama.
A yau ko tun bayan dawowana daga bukin zainab da hjyn Saudiya ta hadani da kayan yarta da su nake amafani a yanzu sai gashi ba kunya yan matan suda kansu suke min magana idan na shigo.
Ban yarda na sake dasuba kamar yadda na saba rayuta ko yanzun ma din haka nake gudanarwa don ina ganin irin kawancen nasu ba amana a cikinsa sai ha,intar juna da sukeyi.
Zance kusan Ezekiel da wata yar kabilan tb sai moronke su nafi shiri dasu a class din ko su shirin don mu karu da junane a iya aji hurdan mu yake dasu.
Yau shigana nikai nasan na fito yadda kayan suka karbi jikina kusan komai ya tafi kala daya don tun a gida Samira ke faman dadani wai na hadu nayi kyau matuka kodai dama nice matar nan ta dinkawa kayan nan ne ?
Mun shigo school rabuwan mu da samira ke nan na nufi department din mu da sauri hankalina yana ga jakkata da ake kiran layina naji nayi karo da mutum saida jakar nawa ya subbuce a hannuna ya fadi kasa nayi tangal tangal zan fadi hannu daya yasa ya taroni.
Duk da zafin da naji a lokacin saida nayi kokarin kwacewa daga rikon da yai min din da sauri nakuma dago kaina duk cikin lokaci guda ina kallon shi da zuman in masa masifa.
Mutanen dake bayan farin mutuminne suka kara firgitani daya ya nufoni gadan gadan hannu ya daga mai naga yaja baya da sauri sai naji yace.
Sorry hjy bakiji ciwo ba dai ko ya fada yana dan bina da kallo inda nake shafa goshina ya sake fadin bakiji ciwo ba dai ko ?
No banji ba nafada a sanyaye a daidai lokacin dana gefenshi yake miko min jakata da wayata daya fadi kasa har glass din ya dan tarwatse kadan daga kasa.
Dama kuma yana da shedan hakan don a tarwatse nake amfani dashi haka har dan mouth piece dinshima ya tabo saboda wahala amma haka nake amfani da abina yanzun kuma gashi ya kara samun matsala.
Baki na rawa nace don Allah kuyi hakkuri ban kula daku bane tafe ina fadin hakan hankalina yana kan wayata da nake ganin ya gama halakewa a lokacin.
Har hakan yasa ana iya gane yadda raina ya baci ta yadda na kalli wayan duk yana tsaye bai daga ba don haka sauran tawagan basu tafi ba.
Ki dinga kula idan kina tafiya a hanya wani dattijo dake saye da shadda a jikin shi No malam kyaleta kaddarane naso kauce mata amma kuma hankalinta naga wanan jakkar nata ki kula kin ji ke mace ce na sake dan runsunawa nace nagode .
Ya fara tafiya sauran suka bishi ruuuuu a baya don glass din idonshi bai bari a gane ko waye shi ko yanayin fuskanshi har na shiga department din mu ban juyo ba inda na samu har an fara lecture a lokacin.
Saidai ba karatu malamin yakeyi ba bayani yake masu akan wani daidai lokacin da yake fadin kunganshi kamar bature da ace anan Africa yake sai zuwa rana zai shigo amma time din daya bayar yana cikin school din nan don haka ita baiwa da hazaka babu inda bakai bawansa.
Idan ka jajircewa abu wata rana sai kaji sunan ka cikin masu hazaka ta duniya,hakan yasa har na samu shiga na zauna bai samu dakatar dani ba son haka ban tsaya sauraron karshen bayaninsa ba nabi wayata da kallo.
Yanzu malam shi din wanan kasan ne dama wani dalubi ya tambaya yace kwarai kuwa dan kuma jahar nan tamu na kaduna gashi yanzu duniya tasan dashi ta ko ina wurin ilimin kimiya ana cabawa dashi kuma.
Ta kusa dani data dan labani naji tace Sa,id ne mana dan kadunene ai kowa yasan dashi yanzu ai kasan nan gashi nan zaki ganshi a tv har VOA ko BBC su hira dashi guy din fa yakai inda ba a tsamani.
Sai naji wata tace amma kuma gatane ya kaisa dai ko tace wanan kan kin sani ai indai kasan ne sai kana da gata zakaci gaba dan tallaka aisai rabo inya rantse.
Wai yanzu dole ke nan zamu koma amfani da system ai kinji abinda ya fada dole dashi zamuyi amfani ke nan don searching ko kuma babban waya dai.
Wata sabuwa na furta a raina shiyasa baba da zamuzo yace karatun jami,a yafi karfin mu a yanzu don tallaka ba wurin zuwansa bane muna diyan tallaka muce mu jami,a zamu.
Lokacin Samira ta zugani na zugu nishi kawai nake son yi ina ganin dan kudin da nike rikewa da baikai ya taka kara ba nake ganin ai zan iya har in taimakawa Samira din data nace muyi jami,a dai asan munyi karatu.
Yanzu gashi tun ba,aje ko ina ba mun fara kasawa tunda sana,an ma na bari a yanzu don banda lokacin hada taura biyu a baki daya ga karatu ga sana,a kuma dole a yanzu nabar sana,a ga kuma kashin kudi haikan ya taso muna.
Godiyana ga Allah haduwana da mutanen arzikin nan yan saudiya danayi a rayuwata don haduwa dasu ya tallafani sosai ba kadan ba.
Zaune yake bayan mota yana amfani da laptop din shi daidai lokacin ya dago kai yana dan shafa goshinshi dayaji yai mai zafi saboda karon nan da mukayi.
A daidai lokacin dana gaban motan ke fadin Sir ka duba wanan ka gani har sun sake wanan zancen suna bashi manufa ta daban.
Jin hakan ya dago kai daga abinda yakeyi yana kallon abinda yake nuno mashi din a lokacin wanan wani photone kuma ya tambaya ?
Accident din daya faru yanzu da yarinyar nan ne har sun sake suna bashi ma,ana na daban dan kallo yayi ya kawar da kai gefe daya ya lumshe ido yana mayar da gangan jikinshi baya yabi lafiyan kujeran motan lokaci guda.
Can ya bude idon nasa da suka kade mai sukayi ja yace Abbas ka kula da wani abu wayan yarinyar nan ya fashe a lokacin da ta bugeni banson daukan hakkin wani a kaina don Allah.
Yaya za ayi sako ya isa a gareta kakai mata waya ko laptop wayan dai zaifi wanda aka kira da Abbas din ya fada kakai mata duk yana cikin adverties din company mu ya zamo karo na farko da zasu ganeshi.
Haka yayi kyau oga bari yanzu in mun sauka zan koma ya fada cikin girmamawa ga wanda suke maganan dashi.
The girl look innocent naga hakan ne a idanunta lokacin da wayan nata ta fadi naga damuwa da fargaban hakan karara a fuskanta lokaci guda.
Amma kuma bata da kama da hakan da kake tunane don gata tsab a zahirima yana kara kallon photo yake ba na bayan amsa .
Hard time ne garesu yanzun da suke karatun nan don baka gane dan me kudi da dan tallaka kai tsaye a nan sai in kana da kula zaka gane hakan garesu ni nayi irin karatun nan ina kuma kula amma wanan din kallon farko nagano wasu abu tattare da rayuwanta lokaci guda.
Sai kuma wayan ya kara tabbatar min da zargina don shine karshen da zangane hakan kaka duk hadewan mutum zaka gane shi ba wani bane daga wayan da yake riko haka kuma ita din da ace watace kana ganin zata tsaya duk taron mu tana ban hakkuri har sau biyu .
Alaman hakan kawai ya ishi mai hankali ya gane gaskiyar mutum daga ina yake nisawa yayi yana fadin gaskiyane oga na fahinci wani abu daga cikin zancen ka yanzu.
Insha Allahu nan zuwa rana sakonka zai isa gareta da yarda Allah nima na kara karuwa yanzu da zancen nan akan zamanin nan.
No ba haka bane Abbas duk l??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????okacin daka cutar da mai karamin karfi kayi kokarin gyara kuskuren ka gareshi don baka san sakkaiyan da zai biyo bayan hakan ba a karshe.
Don haka nake gudun shiga hakkin kowa a rayuwana kullun nasihan iyayyene akan na kiyayye nauyin hakkida amana akaika komai kankantans kuwa.


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login