Showing 321001 words to 324000 words out of 347556 words

Chapter 108 - KARAN DAFI HAUSA NOVELS By Zainab Makawa.doc

24 Sep 2025

8757

ai bakwa nan ne kun dawo kuma ga lalura ai yanzu a bamu ta fada tana dan murmushi bari maigidan ya shigo muyi magana dashi na fada tace Allah ya dawo dashi lafiya.
Bayan ya dawone nake fada mai wai a kitchen su iya suke zaune yake fadin subbahanallahi akan me kuma wai dakunan suna rufe na bashi amsa yake fadin.
Banda abinki Fatima aike zaki basu wajen zama yanzu tunda kece da gida kuma su din bakinkine ai ni nauyin matar ma yai min yawa akwaita da halin alheri da alama zatayi dadin zama .
Koma ya take tunda mami ta turo muna ita zamuyi hakkuri mu zauna da ita ki duba duk yadda ya dace kiyi ya fada nace naso dakina a kasan wanda zan mayar dashi a matsayin nawa daya kuma sai na basu sauran na baki idan muyi kasan mu mata da tara tarkace.
Hakan na dakyau ai saidai ina fatan ba kinyi hakan bane donki guje min kusa dake ya fada haba dai idan nagudu gareka naje gunwa kuma.
Haka muka tsara na duba girman dakunan shiya zama min wani dake lungu dagani dama don macen gida aka ginasa saura kuma kila na yarantane.
Iyan taji dadi tana ta godiya saida na tabatar ta kwaso kayanta sun koma dakin nabar wajen daki na koma na kwanta don har lokacin banjin karfin jikina sosai.
Satin mudaya da dawowa na gama dan murmurewa muka nufi kaduna a cewanshi zamuje mu gaida mami mu dan kwana masu biyu tare da iya da wanan yarinyar mukazo malam Audi ya kwasosu sun riga isa don sai da rana mu muka bar Abuja din.
Wanan tafiyan yaso ya tayar min da ciwo don haka tunda muka iso nake kwance ban fito ba sai washegari dana fito don in karya don shi ya fita ko yaje wajen mahaifinshi.
Kunun koko nake son sha don rabona dashi tun barina gidan mahaifina wajen wata hudu ke nan yanzu ina fadawa iya sai gashi ta fita bata dadeba ta dawo da abin dama kunun har kosai mai kyau mai zafi.
Nayi masa cin hauka baifi rabin lokaci ba sai gani ina fitar dashi ta hanyan amai sosai na jirkita har saida zazzabi mai karfi ya rufeni har sai gani da karin ruwa kuma again kamar albasa banda wani sukuni a tare dani.
Kwana biyu nayi a kwance na danji sauki ina tunanen gida saiga kiran hassana ya shigo min kwatsam a tsohon waya na mika hannu na dauko dakyat ina cizan baki na kara a kunnena cikin sanyin murya nake fadin hello sister .
Amma nayi sa,a fa da wasa nace barin gwada ko zai shiga sai gashi na sameki nace ehh wallahi ai mun dawo yanzu haka ina kaduna ai banda lafiyane tunda na dawo.
What ta fada da karfi kina kaduna baki da lafiya Bantu shine gida basu sani ba nima kamar da wasa nace barin gwada layin naki gani nan zuwa yanzun nan insha Allahu ta fada.
Tana aje wayan mama ke tambayanta kafiya Bantuce muke waya wai tana gari bata da lafiya sun dawo daga wajen tun satin can ashe.
Kaiyya yanzu akan wanan kikewa mutane salati haka kamar wani abu can Allah dai kyauta kukan baku san takaici ba wallahi hassanan ta kalleta tace.
Takaici a kan me mama yanzu Bantuce zan wa bakin ciki ko rashin nuna damuwana akanta kome sai kawai ta mike tabar mata dakin ta koma dakinsu don yanzu a dakin dana bari a gidan mu suke zaune.
Nan mama din ta dinga yanka sababi tana fada sai ga jamal ya shigo yana tambayan mamansa hassana wajen mama din ta dakawa yaron tsawa tana fadin gata a kaina ka dauka ai duk kune barayin na tsunta din fice ka ban waje ai kasan inda take da zakazo nan nemanta wajena.
Baifi wani dan lokaci ba barci ya soma daukana wayan ta tayi kara ina dubawa itace take fada min gasu a falon mu zaune da kyat na samu na fito na hangosu zaune ita Usaina da jamal saisu Jamila.
Na karasa ina dan kakaro murmushin dole a fuskana na zube saman kujera suna min sannu kallona suke wai nayi kyau nida ciwo kwana biyu ya sakani a gaba duk na zube a yadda nazo.
Muka gaisa na tambayesu mutanen gida suke fadin suna lafiya Usainace ke tambayan meke damuna na danyi murmushi ina fadin gani nan dai wallahi na rasa gane kaina gaba daya tun dawowan mu kasan nan.
Jimila na kalla ina mika mata hannu tazo wajena nake fadin ina kuka kwaso min yarana yau tunda nayi aure ban gansu ba sai yau din nan Jamal ya dago yana fadin sannu Anty .
Na gyada masa kai yana kallona na danyi murmushin dole iya ce ta kawo masu abinsha saiga sadiya dauke da tire da suka shirya abinci aka aje iya na fadin hjy wai dan tuwon shimkafa na girka da miyan shuwaka ko zaki iya ci.
Dan murmushi nayi ina fadin nagode iya zan gwada ko zan iya tace insha Allahuma zaki iya ai shuwaka yana gyara baki sosai nako ji dadin cin abincin don nasha miyan sosai ban kuma ji zuciyana ya tashi ba a lokacin.
Har naji jikin nawa ya dan sake ko don ganin yan uwanane yasa na danji karfin jikina kodaya shigo ya samemu a zaune suka gaisa yake tambayana jikin nace yau da sauki sosai gaskiya.
Yace har ina zacen mu koma Abuja aje asibiti a dubaki ko mu koma waje in bakiji sauki ba su hassana suka kalli juna a fakaice tsakaninsu.
Ya duka ba tare da jin nauyi ko kunyan idanunwan suba ya dan raba hannayesa ina tsakiya yake fadin kinci abinci ko wani abu.
Na gyada masa kai yake fadin bakiyi amai bade ko nece banyi ba ya dan murza min hannayeshi saman nawa yana fadin Allah yasa aman ya bar ki ke nan.
Iyace ta girka muna miyan shuwaka shinaci wai kozai gyara min baki ya dago yana fadin amma iya ta kyauta gaskiya tayi kokari na wanan dabaran.
Hannun ya riko yana kallo kafin yace barin shiga in fito sai in zo mu karaci na dan harareshi ina fadin haba son Allah na koshi sosai wallahi yau da yan uwana naci abinci na koshi .
Murmushi yayi yana shigewa ciki suka dan kalli juna Usaina tace ikon Allah ance na zaune baiga gari ba dama ko dan kunyar sarakutan nan bayayi na dan kalleta nace awa zaiyi sarakutan ke ko wa ?
Ta kwashe da dariya hassana tace ni kunga yaran nan fa ba,asan munzo dasu ba gidan su bari mu koma gida kada a nemesu nake fadin gashi banda karfin bude tsaraba idan naji sauki zan aiko wajen hajiya a kwaso min ku.
Kuzo ku wuni min kafin ku koma don zan dan kwana biyu nan kaduna kan nakoma Abuja na fada suka tafi na mike na saneshi a ciki yake tambaya harsun tafine nace ee sunga kadawo sun sun tafi ai.
Abinci fa na fada don ganin ya kama wani tsabga kuma zan fita iya ta ban kwanta dai kiuhuta ku samu lafiya zanfi son hakan gareki ga iya nan zata ban idan na fita ai.
Nidawa kuma zan kwanta ina dan waiga bayana jin tambayan ya dakatar da abinda yakeyi ya dago yana fadin dake da baby mu mana wanan wahalan da baby ya sakaki haka aida ana karbawa mace dana karba maki kindan huta kema .
Ka yarda da abinda mutane suke fada a kaina ke nan cikine dani ko ke baki yarda ba har yanzu ke nan ya fada yana kureni da idanuwansa ban yarda ba ciki tun yanzu na fada kasa kasa ina nufar gado dan kwanciyan nake sonyi a lokacin.
Me kike nufi da ciki tun yanzu Fatima bakya son haihuwane kome kika fadi hakan fatima da sauri na gane katobaran da naso yi ina fadin niko ke son ciki tunda nima haifana akayi kawai dai gani nayi kamar ba lokacin zuwan cikin bane yanzu dai.
Baki gama cin amarcinki ba kenan daniko kike nufi ya kara kureni da idanuwansa nace haba dai ai amarcina bame karewa bane ko yaushe cikinsa nake tunda yanzu takon zai canza sallo a garemu .
Yayi murmushi ya juya idanunsa kafin ya dukar da kansa a laptop dinsa yana aikin da yakeyi ni kuma nakai kishingide na kura masa idanu ina tunane har kasan raina banso ciki gareni ba yanzu gaskiya.
Usaina baki na fadi tun a tsakar gida ta fara fadin mama Uwa sai ki shirya yarki na nan ta dawo yawon amarci da ciki sai zuba shagwaba da izza takewa mutane shiko mijin ya haukace sai rarashi yake binta dashi ko kunyan muna zaune ma baiji ba.
Daga inda mama take zaune wai ita tana aikin kayan girki tace bantu din keda ciki ciki fa kikace Usaina a,a meye abin mamaki kuma mama yarinya da mijinta kuma bafa shege ta kumsa ba balle a tsaya mamaki irin wanan..
Yanayinta ya sauya lokaci guda har bata iya boye bacin ran dake zuciyarta a lokacin ta zan karan dafi dai ke nan a sare a tusge tana tsaye kyam a tsakiyan dawa mama uwa ta aikawa mama wanan sakon a zuciyanta dasu suka san me hakan ke nufi don su hassana basu fahinci ma,anan fadin hakan da mama uwa tayi ba a zancen nasu da mahaifiyarsu ba alokacin.
Tabbas yayan tudun wada bata fadi karya ba Bantu karan dafice ta gaske ko karan dafin irin koren nan wace take tsaye kyam a tsakiyan gona don tafi dan dawa amfani a karshen dama don za a sare dawo abarshi tsaye tsakiyan gona yana nuna alaman anyi shuka a wajen mama Lanto ta jefa baki itama.
Tsam mama ta mike tsaye ta fada dakita kamar a gigice tajima a ciki tana waya tabar kayan girkin nata a wajen tsakar gida .
Har lokacin da hassana data shiga don duba tsohon cazanta taji tana fadin yar iska watau taga gidan kudi bari tun yanzu ta bude hanjinta ta fara zuba masa diya ta cika maigida da bakar zuri,a.
Yarinya kamar haihuwan iblis ina jifata kamar bana aika mata ko da jifa ko kadan baya cin mata don ko gezau ban taba jin tayi kara kan duk wani abindana aikata akanta ba .
Komai nasa ai mata duk yarinyar nan tasa kafa taketarashi batama san ina hasaran kudi a kanta ba amma ita wacan ai kinga da ta samu har yau din nan sai ya bare haka zanyi zatazo ai in har na tabbatar da cikin nan hakan zansa boka ya jefa mata itama.
Da baya baya hassana ta juya ta fita daga dakin hankali tashe don abin ya tsaya mata a rai sosai watau mama nada hannu cikin matsalan barewan matsalolin cikin gidansu kenan da kullun ake fadin cewa tanayiwa wani ??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????agidan har suke dauka karyane kazafine kawai akewa mama din dama.
Yanzu kan ta tabbatar don tama fara zargin mahaifiyar ta akan lamarin yar uwarsu Samira inko har da hannun mama a ciki wanan sherin maman tudun wadace da yaya Altine.
Ita ta ina yanzu zata taimakawa yar uwarta Bantu kafin irin abinda taji din ya faru da ita wanan zance kuma gashi banayi da wani bane balle ta nemi shawara tunda mahaifiyartace ya shafa dole ta boyeta koda ko akan sherine.
Don hakan sirine babba gareta mai taba zuciya don dole ko ta boye uwarta sai,dai gashi kuma bata son yar uwarta ta samu matsala da zai cuta mata a rayuwanta don alherin Bantu garesu ko ciki daya suka fito ya tsaya nan..
Tayi tunane kala kala karshe dai ta yanke shawara mafita da take ganin shine kawai hanyar da zatabi ba tare da wani mahaluki yaji cewa ga abinda kenan ba.
Don haka ta shirya washegari sai gidan namu tayi sa,a ta samu mai gidan a gida ganin tazo yasashi komawa dakinsa ya barmu tare a falo muna hira.
A can cikin hira take fadin Bantu magana nazo maki dashi wanda nake son ki natsu nasan banda matsala idan kece zaki fahinceni ki kuna boyeni.
Idan muka bi komai a tsanake nan ta kwashe duk abinda ya faru bayan komawa su gida ta fada min kuma ta rokeni in rufa mata asiri karna yarda su mama su sancewa zancen wurinta ya fito.
Shiru nayi ina mamaki a raina tare da kurawa hassana din ido na tsawon lokaci kafin na nisa nace Hassana duk abinda zai faru da baw da sanin ubangijinsa.
Mama bata iya sakawa ko hanawa daga kaddarana ke ma kin san da hakan don ni uwa na dauki mama har gobe a wajena.
Yau in alheri ya sameni ko sheri ko akasin hakan ya shafi mama don ya shafeku ya shafi baba dole ko itama hakan ya shafeta tunda ya shafeku.
Bantu ke nan keda kika yarda da Allah kika san hakan mama kan muddin tana tare da anty altine da maman tudun wada bata taba sanin Annabi ya faku ta komawa Allah itama.
Hassana dole ince hakan don wanan abin kunyane a garemu ace wai mama uwata uwargidan baba tana nufata da ko wani a gidan mu da kalman sheri haka.
Yau in me gidan nan yaji girman mama ya zube kuma sai yayi sharia da mama din har inda baki zata ba don sai yasa an daureta wallahi har ta wullakanta kin koga ai ba zamuji dadin hakan ya faru da ita ba.
Ban yarda na fadi wani abu mumuna game da mahaifiyarta ba a gabanta sai fadin da nayi kudin ta kawai akeci don duk abinda wani zai mun nasheri insha Allahu ba zai cin mun ba tunda ban nufi kowa da sheri a rayuwana ba.
Ashe nayi gaskiya don ko hasana ta nadi komai ta tsure mama a daki su uku ta sakawa mama din ta saurara ranan tsinawa hassana ce kadai batayi ba tana fadin Bantu din ma ta fiki hankali.
Duk da kin fallasa uwarki a wajenta bata yarda ta zageni ba ko kadan don wayau tunda tasan ranki zai iya baci taki yarda ta zageni a gabanki mijin nata in ya tashi ya kulleni har abada dan makuli ya bace.
Saida Hassana ta gaji ta fita daga dakin bayan tace ni dai ban yarda ki kulawa yar uwarna sheri bayan nasan shirin ku idan baki bari ba zan fida zancen nan wurin baba kowa gidan nan ya sani.
Ranan ina wuta mama ta saka hassana don kamar ta kasheta take ji a rayuwanta Usaina data samu hassana din da zancen tace hassana meya kaiki wanan danyen hukunci meyasa baki fada min ba tun farko kika samu batu da zancen nan.
Idan mijinta yaji fa kinsan ba zai kyale mama ba wallahi duk da nasan Bantu ba zata bari zancem nan ya fita ba har wani yaji hakan.
Aiko tun far safiya saiga maman tudun wada da ya Altine hassana na daki suka aika kiranta taki zuwa ya Altine ta sameta dakin taso nuna mata kwaya tace ina kika fito tayi cikin ya Altine din itama.
Tana fadin duk wani sheri da kuke kulawa mama ta kasa zaman lafiya da kowa kanku zai kare ai na fada don ko Bantu batai min komai balle in tsaya ku cuta mata ina ruwanku da cikin ta ko samun karuwanta.
Duk abinda zakuce min kuce min Allah yagani ba zai kamani ba don kan gaskiya na fadashi jin hayaniyasu yasa baba dasu mama fitowa mama na daga kofanta tana kwalawa anty Altine kira kada maganan ya fashe yan gidan mu suji asiri ya tonu.
Wai menene ke faruwa haka baba daya dogaro sanda ya fito yake tambaya ta fito a fusace tana fadin babu komai baba yace ke hassana meya faru haka tsakanin ku.
Nasan Altine shigowanta gidan nan ko yaushe ba alheri bane sai ta samu sheri daya kawota ta sauke hassana din tayi shiru su kuma su mama din suna tsatsaye sun kafeta da idanu.
Ina jin dai akan Bintuce don naji Altine na fadin don bintu ta shayeta yasa zata kwashi maganan mama dasu ta kai mata to ta fadawa Bintun tasa mijin nata ya kullesu har abada mama uwa ta cabe zancen tana fada.
Kar dai kardai wani sherin kike kokarin kulawa yarinyar nan tana zaune dakin mijinta lafiya kuma inko hakan ya faru ke Suwaiba da zurian ki kaf bazan taba yafe maku ba a rayuwan ku.
Assha malam assha kan ya daya ka zuzuce haka har kana batu aibanta zurian ka kan me dame Bantu din tafi matarka da yayanta kodon yanzu tana auren me arziki kuna ci ido ya rufe zaka mance harcin suwaiba a kanka.
Rakiya nasani nasani keda Altine babu alheri a tare da shigowan ku gidan nan idan dai gidan nan bada kwandala naku na ginasa ba tun sayen filinshi daga yau nayi maku kashedi da gidana in kuma kun shigo min gida bada sanina ba Allah ya isa ban yafe maku ba.
Su mama uwa aka dauku salati to hassana burinki ya cika sai malam da Bantu suyi maki maganin da uwarki ta kasa maki kike manne da Bantu din shegiya shasha tana gidanta ta mike kafa ta


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login