Showing 294001 words to 297000 words out of 419207 words

Chapter 99 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1491

kokarin gyara daurin zanin jikinta dake banyewa a lokacin.
Ina ja,irin yaron yake ka hana yarinya zama taga iyayyenta don iya shege ko ?
Amma may kuma nayi yayi tambaya cikin natsuwa yana zaune gaban mota ya sakewa yara Ac suna zaune a baya.
Yo ka matsawa yar mutane tafito tafito ku tafi daga zuwanta kamar ba gidan su tazo ba .
Amma dai Amma kinsan matatace dai ko ko wani lokaci ina iya sata ta fito yaran nan sungaji basu huta ba tun shekaran jiya da muka taso dasu.
Kaga ja,iri mara kunyar banza ni kake fadawa matarkace yo ai basai ka fada ba tunda gashi ka nuna muna iko da ita.
Ya dan sake murmushin dole fuskan shi ya nuna gajiya a lokacin yana fadin Amma zancen kike so idan kina son zama da mune sai ki shirya inzo in daukeki mu tare can gidan mu huta tare ko ?
Da sauri nace daga inda nake wallahi daya fi muna sauki yaya mu zauna muna kallonta ko kuda ba zan yarda ya taba min ke ba Amma.
A, a karya kukeyi ja,iran yara ku daukeni ku kaini gidan ku ku wahal dani ina zaune kalau yace min don Allah shiga mu tafi na kalli murja nace murja ku shiga muje keda Fauziya don Allah.
Baice muna komai ba suka bude baya suka shiga har lokacin Fauziya tana dauke da Sultana data banye a bayanta.

Sallamu Alaikum ta fada daga kofa tare da fadin hjyn salma na dakine tana tambaya Nafisa dake zaune da waya a hannun ta tace tana ciki ta kwanta ne.
Ta juya zata koma maryam banyi barcita fada daga kofa kinzo tsegumin ganin abin mamakin da yaran nan sukayi ko ?
Wallahi kamar kin sani hjy wai dama ashe sun haihu ni ban taba jin labari ba a gidan nan yadda kika gansu haka na gansu maryam.
Maryam dani yaron nan yake wasa harni zai rainawa hankali akan yar??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????inyar idan nayi mai magana yace indan bashi lokaci karatu takeyi idan ta kare zai turota.
Da zan ganta sai ganin su nayi da iyalinsu abinda banson akai sai da ya kaimu gare shi ta fada tana hade zuciya.
Hjy yarinya ta koma kamar wata sarauniyar mata a gurin gwajin kyau ai shike nan dama burin Alh ke nan ya kuma cika.
Shigowan salma ke nan gida da goyon yarta wani kallon mamaki tayi masu lokacin da ta samesu tare suka gaisa take tambayan may ke faruwane mama na ganku haka ?
Uhummm salma ke dai bari yayan ku ne suka zo wai ashe har yarinyar nan ta haihu har uku amma ba wanda ya sani.
Wai wani yayana kuke magana hjy maryam dake fada mata tace umar mana da yarinyar nan Fatima kinko ga yadda yarinyar nan ta koma kamar haihuwan larabawa.
Salma ciki murnanta tace lah ashe sun zo don Allah maman ikilima har sun haihu da yaya kike fadi.
Sun haihu wallahi salma sai ma kinga yaran kamar ki sace su don kyau da daukan ido wallahi bazakice yaran kasan nan bane.
Na banza inji hjy jummai ta fada cikin kunan rai dani yaron nan yai wasa sai na nuna mashi ni ba sa,arshi bace .
Don sai na raba wana tsinanen aure na kuma rabashi har ita da yaran mugata tsiya.
A,a mama don Allah don Allah mama ki barshi da matar shi tundai yana son abinshi kinga har da zuria a tsakanin su kuma yanzu.
Mama abu batun yau ba kina nuna adawan kin wanan auren gashi yanzu har ankai ga hayayafa haka yara kunce har uku don Allah dai mamaki barshi da iyalin shi dai.
Ke rufa min baki marasa kinshin zuciya sakarai da bata taba wayau naki na barsu din aiduk ku dinne barayin na tsunta dake dashi.
Salma ta dago kai ta kalli uwar tare da fadin ni gaskiya nake fada maki mama kin dai san rabo yana kashewa yana rayawa kuma.
Da yanzu rabon yaran nan su fito ta tsatson fatima da yaya ya kashe ki fa mama idan kwananki suka kare kana jayaya da Allah ne mama ?
Lalai salma ke sakaraice karan ma ta karshe a daidai lokacin Nafisa ta dawo falon tana fadin anty salma don baki ga yadda fatima ta koma bane wallahi ko ke da kinji wani iri a ranki.
Tace wani iri namay nafisa bayan nasan Allah bai raba daidai ba tun farko kowa rabon shi yake ci ke nafisa wallahi in wanan halin zaki dauki zaki samu matsala a rayuwan ki kuwa.
Nan su ukun suka haye salma da fada da zagi karshe ma bata zauna yinin da tace zatayi ba tayi masu sallama zata tafi.
Har takai kofa uwar tace wallahi naji wana magana ya fita sai na saba maki fiye da tsanmanin ki bata dai ce komai ba tayi dariya tana fadin ni mama ba sune gabana ba yanzu kowa ya iya gidan shi dai ta fice.
Hjy maryam ta dade suna mayar da zance da sarakuwa har da basu labarin irin matsa min da yayi in fito mu koma gida don yara.
Shike nan maryam yanzu kin fara fahintar abinda nake hangowa a cikin auren yaran nan ko ?
Duk da hjy maryam bata fahince taba sai dai tace kwarai kuwa hjy ai na dade da gano manufarki ba yau .
Hjy Jummai tace yadda maimuna ta sakani bakin ciki nata sai yafi nawa don ita ga saki kuma in saka ya karbe yaran muga ta tsiyan cin arziki.

Muna shiga gida yaya ya kwalawa maria kira ta fito da sauri daga part din su tana zuwa yace ta ba yara abinci suci tai masu wanka su kwanta.
A daidai lokacin muka karaso ciki tare da su murja part din shi naga ya shige bai ko waigomu ba.
Nan falo muka zube muna hira da murja sosai inda a wurin ta na ji wasu abubuwan da akayi a bayana wanda take ban labarin su.
Ban lekashi shi kuma bai fito ba saida naga lokacin sallah yayi na mike na shiga wurin inda samu bai daki yana bandaki a lokacin.
Kara budan kofan shi ya dakatar dani daga juyawan da nayi zan bar dakin na juyo ina fadin na dauka baka tashi bane ai kana kwance.
Yanzun kika tuna dani kina can kin samu yan uwanki yau kin manta dani na danyi murmushi ina fadin.
Haba yaya yaya zan manta da kai yau dai kawai ina bata lokacinane da yan uwa saboda farin ciki yau gani a gida duk da ka hanani zama da Amma muyi hira yaushe rabo da juna.
Sai gyara hannun jallabiyan jikin shi yakeyi yana fadin zaki jamin masifan fadan ta akaina da zagi idan ina cewa kiyi abu gabanta kina mun gardama ya fada lokacin da ya dauki tasbahan shi zai fita.
Bayan na fito na samu murja a dakina har tayi alwala nima alwalan na shiga nafito nayi sallah muka dawo falo muka zauna don cin abinci.
Lokacin ne ba nemi Fauziya dake can leke da Sultana tun yarinyar na mata kiuya har ta dan fara sakin jiki da ita don daukanta da takeyi da goya ta.
Murja ta kira mukaci abinci a tare duk yadda tayi yarinyar taci abinci taki ci saima kukan da tasa a karshe na karbe ta daga hannun fauziya din.
Ya shigo ya samu muna leke da Fauziya data bar abincinta ta dawo inda yarinyar take saman jikina sai daya shigo ya karbe ta daga hannu na fauziya ta rabu da yarinyar don bata iya zuwa gurin shi.
Ya dan zauna a falon sai dai bai kulamu ba din ya kula su murja sun sha jinin jikin su dashi tun lokacin daya zauna wurin yana rarashin yar shi.
Mikewa yayi da yarshi a hannu ya nufi dining ganin hakan na mike daga inda nake zaune ina muna cin namu abincin a kasa saman kafet.
Abincin na bude ina tambayan shi abinda zan zuba mai yaci sai da ya lumshe ido kamar baison magana lokacin yace ke may kikaci ?
Tuwo naci don shi nave suyi mun ya lumshe ido yace zubamin irun shi kawai yaran fa suna barci har yanzu na bashi amsa ita wanan ma goyon da ta samu wurin fauziya shine taki kwanciya.
Ya sake lumshe ido tare da mika hannu ya dauki cup din dake aje yana tsiyaya ruwa kadan ya kurba da bisimilllah yasha.
Yaja abincin bayan ya wanke hannu ya fara diba yana kaiwa a bakin shi har lokacin Sultana tana a jikin shi naso in karbe ta ya daga min hannu na barshi da ita.
Daga inda nake zaune wayana yai kara na dauka nasan mamu ce don ita kadai keda sabon layina ina dauka take fadin kin tafi min da yarinya bayan kinsan tana zuwa hadda.
Mamu a barta yau mana mu wuni a tare da ita don Allah gobe sai ta tafi idan Allah ya kaimu kinsan halin karatu nan ba wasa a cikin sa ki dawo min da ita kafin lokaci tafiya karatu yayi.
Murja kinji mamu wai Fauziya ta koma gida barta idan na tashi tare zamu koma anji ai daga inda yaya yake zaune ya miko min murya yana fadin ba tace akaita gida ba ta tashi in sauke ta fita zanyi yanzu idan nagama.
Mikewa nayi na shiga dakina na fito da wani babban jakka nace ki kaiwa mamu ki ce zamuyi waya murja ma na mika mata ledan ta nace kafin kayana ya iso ki fara amfani da wanan.
Fita yayi suka bishi baya har bakin mota na rakasu suka wuce ya sauke su a daidai get din gidan bai shiga ba yace akwai inda zai tafi yana sauri.
Kamar mai jiran tsamani hjy maryam ce zaune da yaranta sun zubawa kofan shigowa get ido suna hira sama babban tabarma idan tana son yin wani gulma haka sukan wuni zaune waje don ganin kwam.
Ganin fauziya tafe da babban jakka tana ja saida murja ta bude get ta shigo ta kama mata sukaja zuwa dakin mamu suka aje.
Daga inda suke zaune suka zuba masu ido saida suka shige da jakkan mai kamar jirgi part din ga tsawo ga nauyi da alama kayane masu yawa a cikin sa.
Wanan abinda ta gani ta tafi ta tseguntawa hjy jummai abinda idon ta ya gani aiko nan hankalin hajiya ya tashi sosai dole ta nemi kannenta tana labarta masu zancen zuwan mu da abinda hjy maryam tazo mata da tsegumin shi da yamma.
Ranan kamar hjy zatayi hauka a gidan hankalinta a tashe yake sai yamma kawu ya dawo daga kauyen dayaje dauri aure yazo ya samu labarin zuwan mu daga bakin yaran shi dake tasowa yan samari.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:31 - ??5惙5惙5?: BISSIMILLAHI RAHAMIN RAHIM IHDINAS SURATAL MUSTAKIN, , ,


Mun zo mun gaida kawu da imani da mamaki mu ya cika mai zuciya har ya kasa boye mamakin shi gare mu yana fadin wai kai Umar akidar turawane ka dauka ko ra,ayin kane haka nakin fadan komai wa kowa saida a ganka kwatsam da abu daga sama.
Yata harda ke kin koyi wanan akidar tashi kuma yanzu yana kokarin mayar dake haka da irin halinsa ace har zaki haifi yara har uku amma bamu da labari a nan?
Ayi hakkuri kawu na bashi amsa a cikin ladabi sai ga su hjy sun shigo falon gaida su na fara tayi kamar bataji ba saida kawu tace baki jin suna gaida ke jimmai .
Ta dan juyo tana amsa min ta juya wurin kawu tana fadin dama yaran nan nake son magana dasu a gaban ka na shigo.
Da sauri ya umar ya dago kai yana kallon ta da mamaki yana son sani abinda aka kawo mu kara wurin mahaifin shi a kai .
Ya akai haka daga zuwan ku har kun batawa mahaifiyar ku rai Umar ya akayi haka ya faru kuma ya fada yana mai kallon fuskan dan nasa cikin yanayin nuna damuwa.
Kai yaya Umar ya dukar batare da ya furta komai ba sai da yaji mahaifin nasa ya kara maimaita tambayan shi gareshi ya dago kai yana fadin .
Daddy a iya sanina bansan nayiwa mama komai ba tun zuwa asalima tunda nazo bamuyi wani maganan kota arziki a tsakanin mu ba balle ince ga wanin abinda ya hadamu da ita.
To ke kinji kawu ya fada yana kallon mama tare sa canza yanayin fuskan shi yana fadin jimmai bana son haka ga yaran nan.
Ki bar yaran nan suyi rayuwan su babu tsagwama a ciki haka kwanaki habbib ya kawo min kara ki akan iyalin shi .
Wanan dalilin yasa nayi karan wana yanzu gurin ka don ina son a tambayar min shi ko yanzu ya samu wasu iyayyen da suka fimu ne ban sani ?
Da har wana yarinyar zata tara iyali haka ban sani ba kuma banko ji labari a gurin wani ba sai kawai in gansu kwatsan da yara sunzo muna don may raina ba zai baci ba Alh ?
Kawu yace wanan kina da gaskiya don yanzu haka zancen da mukeyi da su kenan kika shigo falon nan.
Sai abinda nake so dake ya kamata yanzu ki fahinci halin Umar don halaiyanshi sai hakkuri don na fahinci haka Allah ya hallice shi yadda yake shiru shiru hakama komai nasa yake tafiya.
Ni dai ina daga gefe nayi shiru na kama bakina tunda ba wanda ya ambace ni a cikin zancen nasu.
Banga laifin shi ba ai tunda ita wace yake bare baren akanta ta kama uwarta ai shidai ne ake kokarin rabawa yanzu da tashi uwar .
Yaya ya dan murmusa tare da fadin bare bare kuma mama akan me zan dinga wani bare bare har in manta dake ?
Tace gashi kuwa wai har kaine da shiga dakin maimuna ka kasa shiga dakin maryam ka gaida ita don kawai kana auren yarta ko mai ?
A natse ya dago kai yace mama koda na shiga part din ai yanzu ba laifi bane don gaisuwa dai kawai saboda akwai nauyi mai girima a tsakanin mu .
Don yarta tana a matsayin matata kinga dole munzo in shiga in gaida ita.
Ko mama ta manta a gaban kawu take tace da dan bata babawo a gabana kake kiran wanan yarinyar da matarka ?
Jimmai ba matarsa bace ko zaki raba abinda Allah ya hadane gaisuwa a tsakanin su shine abin tashin hankali kuma yanzu?
Kin manta har gobe ina zuwa gidan yayaki gaida shi da sauran yan uwan ki girmana sukayi ko haihuwana da nake zuwa gaidasu da girmana.
Don haka ban son irin maganan nan kin bar yaran nan yadda sukazo a cikin farin ciki su gama su koma lafiya hakana.
Nan mama ta fara fada cikin tashin hankali tana fadin abinda ke cikin ranta a lokacin tana cewa dama abinda aka kulla ke nan don kawai a jaye mata da daga gare ta.
Da kawu yaga tashin hankalin yai yawa ga yaran har sun fara rudewa da masifan mama suna kuka suna make muna a jiki.
Fatima dauki yaran nan ki tafi dasu idan na gama zan shigo in dauke ku mu tafi nan na dauko yaran muka fito daga part din kawu zuwa wurin su mamu don ban shiga ba da muka shigo.
Na shiga muka gaisa har lokacin yaran basu bar kuka ba nima idona da hawaye a rude mama ke tambayana na kasa fada mata komai.
Murjace tace ya wuce hjy ce don naji muryan ta a gurin kawu yanzu da zan shigo da sauri mama tace may kuma kukai mata daga zuwan ku.
Sai an mata wani abu tunda neman nayi takeyi dama a hankali nace wai don may yaya ya shiga gaida mamu da muka shigo bai shiga wurin maman su ikilma ba.
Yau naji kitihi a gidan nan yau kuma har turashi ake ya gaida maryam a gidan nan har ta manta da ita da bakinta tace ba wanda ya haifa mata diyan.
Har ya fito muka tafi ban samu shiga wurin mamu ba ranan sau murja naba sako ta fada mata mun tafi.
Kwana biyu bamu shiga gidan ba gani ina son zuwa mu zauna da ita in mata bayanin kayan dana tura akai mata kafin inzo har zuwa lokacin ban samu bayani da ita ba.
Nafisa da salma suka zo gidan saidai basu samu yayan su a gida ba ya fita tunda safe maria suka samu a falo da yar aikin mu tare da yara suna hira.
Ina kwance a daki saiga maria tazo tana fada min anyi baki suna falo a zaune nace gani fitowa yanzu ki basu abin motsa baki tace na umurci su Asiya su basu ko.
Na mike da kyat don duk jikina banjin dadin shi yai min nauyi haka kawai ranan koda na fito ina jawo kofana sai nayi arba da Nafisa tana

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login