Showing 18001 words to 21000 words out of 419207 words

Chapter 7 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1392

min duka a kai kumb tare da fadin shegiyar yarinya dazun da ake maki magana kika gudu gidan uba kika je har wanan lokacin ?
Yakara kai min wani duka ban san lokacin dana sake wani ihu mai kara ba da ya karkato da hankalin kowa gare mu.
Yar iska ba kina ganin Manjo na kama maki ba agidan nan yasa kike abinda kikaga dama yanzun.
Cikin kuka da jin zafin rikon da yai min nace may nayi ma da zaka mare ni don anga banda uwa a gidan nan kowa ke dukana haka ?
Shegiya an duke ki din kira uwar ki ta rama maki ihun dana sake yasa kowa na gidan fitowa a lokacin dama dukkan su hake suke dani.
Karawa yar iska marajin magana yarinyar nan yanzu ta fitsare a gidan nan da kike fadan haka wani ya kori uwar taki a gidan nan halan ?
Ummatu ne ke wanan maganan uwar gidan Baffa wani ihun na sake sakewa mai karfi don Manjo taji tazo ta cece ni don naga su ba hakkuri zasu bada ba sai ma zugashi yai min tsinanen duk yadda yake murdai murdai din nan.
Aikuwa manjo najin kuka na tun ihuna na farko ashe tana can tana kokarin tasowa daga daki ne sai muryan ta mukaji tana salati a bayan mu.
Tana fadin yau naga abinda yafi karfin ganina a gidan nan yanzu sadi kashe yar marainiyar Allahn nan kake son yi ko may ?
Wanan irin duka da kake mata har a dakina ina jin kara tana karasowa gurin take magana tana zuwa ta sa hannu zata kwace ni daga hannun shi ya kare rike gam don kada ta kwace yana min ketan daya saba.
Tana jan hannu na tana fadin shikata dan banza mara hankali da tunane yar nan kwara daya ta tsone maku ido a gidan nan .
Ina ga kannen ka nan baka tsawata masu su daina yawon banza ba sai wanan da aka san inda take ina nan gidan makwabta take shiga duk iya yawon nata.
Da taga yaki saki hannu nawa takai mai duka a baya tim yace wai wai wai manjo akan wanan yar kika dukeni haka yau ko sai na balla ta a gidan nan inga iya fitinan ki.
Baka isa ba dan banza uban ka ma yayi kadan ya balla ta balle kai yaron kawai sauran mutanen gidan sai abin ya koma basu dariya.
Don shi a zolaya yake mata magana inda manjo iya bakin gaskiyar ta take fada dashi zata kara kaimai duka ya sake ni da karfi na fada jikin ta da kadan mun fadi kasa Allah ya kare bamu kai kasan ba.
Tace dan kawai na gane so kake ka karasani bawai a yar abin naka ya tsaya ba yace in karasa ki in gane may manjo ki dai ji da kafan nan naki tukun.
Na dai gane zaman mu a nan ne baku so zan koma azare inda na fito da yardan Allah goben nan zamu bar maku gidan tunda na gane nufin ku.
Haba yar nan ita kadai ce a gidan nan kowa ya tashi dai A ruwa dau a ruwa yace ai da na kamata yau yadda nake so data zama a wuta.
Tace kai tafi can dan kawai kai kan bakayi hali mahaifan ka ba sam wallahi daka biyo su daka dace.
Yace halin ki na kwaso ai bakiga muna kama dake ba ta kara sukewa da yaron tana fadin ke kuma shige mu tafi kar ya karasa min ke don ba mutunci ne da su ba.
Har mun dan gwauta muryan ummatu mukaji tana fadin gaskiya babba ki dinga barin suna hukunta wanan yar.
Yanzu gashi akanta kike zagin wanan yaron haka kina wufinta shi akan yar da kika fi so a gidan koma dai yayane su duk ai jikokin ki ne kaf a gidan nan.
Saude zaki fita idona ko sai na bata maki don banyi tsufan da har sarakuwa zata wufintar dani a gidan nan daga can gefe nace Manjo kyalesu mu tafi ina jan hannun ta.
Bayan mun shiga dakine ta juya gare ni tare da fadin ke ma kingane ki bakya jin magana .
Kinfi son ko da yaushe su dinga dukan ki kamar sun samu jaka ko ?
Haka kike yi da muna gida ina kike fita yanzun kinzo nan kin koyi halin yaran banzan nan da uwayen su basa son ai masu magana.
Yanzun akan na hana yaron nan sadi dukan ki yasa saude ke son fada min maganan banza goben nan idan Allah ya tashe mu lafiya zan bar masu gidan nan indai akan nasa ido haka suna ci muna fuska ne.
Na bata rai tare da fadin nifa manjo ba da gangan naki dawowa gida da wuri ba kin ga kaina dole malle ta kwance min kai aikai min kitso an gama kuma tace sai nayi wanka naci abinci zan dawo gida saboda tasan halin gidan nan.
Tunda na dade haka ba lalai bane su bani abinci don ba bakin, ta suke ba gun sanin halin su malle tace to kin gani har makwabta sun san da bakin halin su.
Ki kama kan ki cikin yan uwan nan naki na kula ba son ki suke a cikin su ba don hakane nima bana raga masu ko kadan.
Wallahi Manjo dukan da yai min ai banso ki masa kadan ba tace rufe min baki iya karafina ke nan da dukan bai maki ba ai sai ki ramawa kan ki.
Ni dai abinda nake so dake ki koyi natsuwa ki kama mutuncin kan ki kodan mahaifin ki dake kasa kwance.
Ina jin haka bace manjo yanzun banda natsuwa ne ko may ina fadin haka na koma daga karshen dakin na zauna na bata baya alaman nayi fushi ke nan.
Kyale ni tayi na dan lokaci nasan ba zata juri ganin fushina ba da ita sai naji can tana fadin ga abincin naki dauka ki kara don nasan ma basu saka maki ba kada ma ki tambaye su don ba baki zasu yi ba.
Kyaleta nayi kamar banji ta ba sai can tace ke dadina dake baki da fahinta da wayau ni ina nufin ba baki da natsuwa bane ina nufin ki kara kama mutuncin ki da kowa mutuncin mace kimar ta.
Nagane may take nufi wanan maganan dashi na bude kunnuwa na a gurin ta kullun nasihan manjo ke nan a gare ni tun ban fahinci mai take nufi da hakan ba har na gane .
Mikewa nayi ba tare da nai magana ba na dauki kofi nayi hanyar waje tace ina kuma zaki bazaki zauna kici abincin ba nace ruwa zan debo a famfo.
Da na debo ruwan na dawo na dire a gabanta tare da dauko mata abincin data ce inci don nasan tun dan abincin rana data dan taba bata ci komai har wanan lokacin da take kokarin sadaukar da yuwanta ta bani rabon ta inci.
Dago kai tayi ta kalle ni tare da fadin yaya kuma kika aje a gabana nace Manjo kici ni a koshe nake wallahi na fada maki naci biski a gidan malle sai dana koshi .
Kai ta gyada tare da saka min albarka kamar nice na girka abincin ko na sayo aka girka nace baffa ya kamata ki sakawa albarka shida ya kawo aka dafa.
Bude abincin tayi ta ja tsuki don can yake manne a kwano har yayi sanyi kalau sosai tana shirin magana mukaji sallaman Atika a kofa.
Tana tafe da kullan abinci ta shigo ta dire a gaban manjo tare da gaishe ta tace manjo biski ne malle tace a kawo maki tasan kya so.
Manjo na washe baki tace usse, usse, malle ko ta kyauta min yau tayi min abinda naji dadi sosai ga abinci ga yar nan ta koma goshi na mata kyalli saboda gyara.
Atika tace Manjo don ma Fatima bata so gyara aida tasha gyara gun malle to ita fatiman ne idan an mata gyara sai an dauki lokaci bata kara ba.
Malama ban fa son kushe kin fini gyara ne ko may na fadi ina hararan Atikan sama da kasa da sauri tace , a,a ni na kai can.
Dallah rufe mana baki ke badon Allah yayi ki fara ba ai da bamu san iyaka ba kin gode kin kwaso iyayyen ki duka a gurin fari har makin so ki fisu da kina gyaran jikin ki aida kyaun ki badai nan ba.
Bude kulan da Atika ta shigo dashi nayi sai kamshi ya tashi a daki yana daukan ido nace kinga Atika manjo fa bataci komai ba tun kan na fita gidan nan dazun har yanzu don Allah bari ta danci wani abu kada ta fadi muna.
Nan na tursasa manjo taci abincin taci abinci ni kuma na hau ba Atika labarin yadda muka kwashe da yaya sadi lokacin dana dawo gidan ina sanda.

AMERICA

Yana zaune ya mayar da hankalin shi ga computer shi yana aiki so yake ya gama aiki dake gaban shi wani aiki ne daya kawo shi kasan daga england duk da ya kusa kammala aikin kuma akwai sauran kwana uku da yake son karawa garin kafin ya wuce.
Wayan shice tayi kara har tana batu tsukewa bai daga ba sai can ya daga wayan ya duba sunan kanin shi ya gani rubuce a fuskan wayan.
Receive ya danna kada wayan ya katse tare da fadin habbib ya kayi ne cikin muryan shi dake nuna gajiya da natsuwa.
Habbib din yacd haba bros ka shige kwana biyu ko labarin ka ba aji wanan ai sai hankalin mu ya tashi.
Yanzun ma hajjaju ne ta kirani tana fada wai kwana biyu ta nemi layinka bata samu ba shine hankalin ta ya tashi.
Sai da ya shafa goshin shi ba don zufa ba sai dai don gajiya da aikin da yasa a gaban shi yace wallahi habbib na danyi tafiya ina America sati biyu ke nan nazo wani aiki ne daga ma,aikatar mu.
Bros shine babu sanarwa kasa hankalin mum ya tashi kasan fa halin mum a kan mu yace wallahi zan kirata I will call her leter.
Gaskiya ya kama don hankalinta ya tashi sosai wallahi kasan kuma ga matsalan gidan nan yanzu dad ya birkice mata sai korafi take min ko yaushe ta rasa gane kan dad a kwanakin nan.
For what reson may ke faruwa a gidan ne wani abu ya hada su yana tambaya cikin nuna damuwa.
Wai fa akan wanan matar daya aura ne fa yake kokarin juyawa hajiya baya kaji mun dad fa duk yadda suke da mum yanzu akan wata zai juya mata baya.
Nasan duk wanan abin ba sherin kowa bane sai , , , , kai habbib mind you togue ka daina shiga zancen mata da miji don Allah.
Duk abin dad nasan ba zai taba juyawa hajiya baya ba akan wata matar diba ga yadda shakuwan su yake kai ma wai baka san halin mata bane idan an masu kishiya.
Ka daina shiga irin wanan maganan kai na miji ne idan kaji ka bata hakkuri ka kwantar mata da hankali shi yafi.
Yace ni wallahi shi yasa ban son wanan auren da dad ya kara ba tun farko don , , , ,
Kai ni ba wanan ba na fada ma ka daina shiga harkan mata don Allah zan turo maka da kudi ka tura masi gobe ita da dad din kodaya yake ma barshi dai zan turawa dad nasa da kaina .
Daga haka ya kashe wayan yana girgiza kai alaman kai mata halin su daya a gurin kishi ba yara ba ba manya ba indai har kan kishine.
Shi yama manta da kamanin wanan matar da ake cewa yar uwan su ce dad din nasu ya aura sai kuma ya ja tsuki don bai son abinda zai dagawa mahaifiyar tasu hankali ko kadan don yadda take son su haka suma suke son mahaifiyar tasu.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
16/11/2021, 22:37 - ??5惙5惙5?: YA ALLAH MUNA ROKON KA KA AZA MU HANYAR TSIRA KABAMU IKON TSARKAKE IMANI DA BAUTA A GARE KA TSARKAKKE YA ALLAH MUNA ROKON CIKAWA DA IMANIN KA A LOKACIN KOMAWAN MU GARE KA AMIN YA HAYYU YA KAIYUMU.

Alh sani yana kishingide yana kallon labaran NTA na kasa gefen shi hjy maimuna ce a zaune wacce hankalin ta baya kan tv ita.
Jin tsukin da yaja ne yasa ta daina latsan wayan hannjn ta da take yi ta kallo shi tare da fadin lafiya ko ?
A rayuwana na kijinin hurda da arnakun nan sai dai yanzun boko da wayenwan kai yasa komai zakayi a duniyan nan sai tare da su muddin kabar kasan hausan nan to ka rabu da akidar hausawa ke nan .
Shiyasa nake fadawa hajiya yaron nan ya dawo gida hakana tunda ya gama abinda ya kai shi can yau shekara nawa da kare karatun shi.
Zaman da yake can kwata kwata bai kwanta min a rai ba na fi son su dawo gida kusa dani idan ma aiki ne akwai ire iren aiyukan su a nan gida nigeria ai.
Umm,humm yaya sai nake ganin yanzu umar ba yaro bane ai don akwai sa,annin shi da sukai aure da iyali , kaga wanda ya kai munzalin rikon iyali ai ba za,a ce zaiyi wani abin asha ba yanzu.
Kai dai ka??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????wai ka bisu da addua a duk inda suke ubangiji ya tsare muna su tare da sauran yan uwa musulmai.
Ko banza indai umar ba ya canza bane kaf yaran gidan nan yafi su natsuwa da sanin ya kamata a iya sanin da nai masa a baya.
Murmushi jin dadin yabon danshi da tayi yayi tare da fadin Umar kan akwai natsuwa da tausayi wanan haka yake ba karya kika fada ba ga halin sa.
Jin shigowan mutum kamar daga sama falon yasa suka daga fuskokin su dauke da murmushi kan maganan da sukeyi na dan Alh din.
Kallo daya kowan su yai mata ya hango fitinan kishi a tare da ita gama ga yadda ta samay su a zaune din.
Kusan hjy maimuna rabin jikin ta na ga jikin mijin nasu wanda take kokarin bawa juice din shi na zalla diyan icce da yake sha duk dare kafin ya kwanta a matsayin abincin daren shi.
Da zaran ya dawo da yamma ya ci abinci ba zai kara cin wani abin ba sai yayan icen don tsaron lafiyan shi da yake yi din wanda har ya saba da hankan yanzu.
Sai da hjy jummai ta samu wuri ta zauna kafin ta fara magana da miji nata gani haka yasa hjy maimuna azaman fita daga falon mijin nasu.
Ina kuma zaki baki gama dani ba cewan Alh sanin yana mai kallon hjy maimun duk da yasan shigowan uwar gidan nasu yasa zata basu wuri su gana.
Kamar ba shi yai magana ba sai kuma ya juya inda hjy jummai take zaune yana fadin kin gan munan yanzu haka maganan umar muke kika samay mu.
Uumm, tace dashi ba tare da ta fadi komai sai dai a can cikin ranta fada take da maigidan nasu akan may zai zauna yana maganan danta da wata mace a gidan nan mafarin ya sake masu siri ke nan kuma ko.
Juyowa tayi inda suke da hjy maimuna yana fadin baida sanyi dai sosai ko cewa da juice din data kara daukowa zata zuba mashi din.
May umar din yayi kuma har kake maganan shi da wata a yanzu irin haka ai kamar wani abin ne ko ?
Wani abu kuma hjy ba zanyi maganan dana duk lokacin dana so ba sai dake ke nan, wai may yasa ku mata kuke da karamin tunane ko wani lokaci.
Kai tsaye tace maganan da na ni da kai ya shafa bada wani ba a gidan nan ko cikin yan uwa bada wani bare ba can daban.
Maimunan ce bare Jummai ?
Ta dago kanta da sauri don jin kiran da yai mata ta dan kalle shi jin sunan ta da ya kira ba sakaye don haka tasan ranshi ya baci ke nan.
Yaci gaba da fadin idan ma kina tamtamane to ki bari don maimuna ta wuce bare a gurin diyana kin fi kowa da sanin hakan kuma.
Ban san da hakan vmba sai dai idan yanzu kike kokarin raba hakan a tsakanin diyan ki da yan uwana.
To sanun sarkin yan uwa dadin abin dai kowa nada nasa yan uwan a duniya balle ai min gorin yan uwa a gidan nidai nace al,amarin diyana ni ya shafa a gidan ni kadai.
Yace haka kika dai fadi sai dai ni kuma ban lamunce da hakan ba don ba ke kadai kika haifi yaran ba.
Ummummm ashe manufar ki ke nan da kike kokarin nisanta yaran ki da kowa to bari kiji kowa yasan ni yasan ni mutum ne

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login