Showing 225001 words to 228000 words out of 419207 words

Chapter 76 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1492

fadin ita wanan yar uwan taka fa kuna waya da ita kuwa don ita kan nasan tarbiyan muce ta musulman hausawa gare ta..
Yayi kamar baiji mai Nasir din ya fadi ba lokacin ya share shi ga zancen kawai yana tuki abinsa.
Nasir din ya sake fadi wallahi mutumina kaji tsoron Allah ka dauki yarinya karama kaje da ita inda bata san kowa ba kana gana mata boni can.
Ya juyo a harzuke yana fadin ubanwa ya fada ma hakan duk kokarin da nake kenan banyi ba ko.
Kai Nasir nifa har yanzu kallon kanwata ko yata nakewa wanan yarinyar har yanzu.
Amma ko bakai ma kanka adalci ba abokina kana ganin yanzu ita wanan matar taka zatai maka halarci nan gaba.
Ya juyo da kyau yana fuskantar shi yace ya kamata umar ka natsu ka fahinci mai mahaifanka ke nufi da hafin auren nan gareka.
Umar baka sanin kayi sakaci da daman ka sai nan gaba kadan idan girma ya fara zo maka.
Ko kana neman wani mukami a kasan nan a lokacin zakayi dana sanin watsi da wanan daman da mahaifinka ya doraka akai.
Ya juyo shima yana fuskantar abokin nasa cikin fadin ban gane mai kake nufi ba Nasir ?
Kana tunanen zan shiga siyasa ko wani abu a kasan nan ne nan gaba ko kana tunanen zan daukowa kaina maganan da zai ja min tozarci.
Kai Nasir ya girgiza yana fadin baka dai fahinceni ba abokina mu bar zancen nan bawai ina kalubulantar matar ka bace ko daya wallahi gaba nake hango maka kawai yasa na fadi hakan.
Huci yayi gami da furzo da iska daga bakin shi yana sauke ajiyan zuciya tare da dan buga sitiyarin motar a hankali alaman jin haushi a ranshi.
Baisan lokacin dayace mata mata ba babba ba yaro a cikin su halinsu daya ne abokina in fada ma yanzu haka a cikin takuran hjy mu nake tun zuwana kasan nan .
Don har yanzu hjy bata janye maganan ta ba Nasir kan yarinyar nan taya kake ganin zan yaudari daddy in affaka wa yar karamar yarinya saboda in bata mata rayuwan ta a banza Nasir.
Duk abinda mutum zaiyi yayi zurfin tunane a cikin sa bazan taba son aiwa yata ta cikina ko kanwata yadda mama tace tana so in mayar da yarinyar nan karamar bazawara.
May karamar bazawara ke nufi Nasir in lalata rayuwan yar mutane in sako masu ita a wullakance Nasir ba zan taba yin haka ba a rayuwata yar maimuna kamar jinanane Nasir.
Ido Nasir ya zuba mai a cikin mamaki yake kallin abokin nasa can yace idan har hjy ta furta hakan batayi maku adalici ba dakai da mahaifinka abokina.
Shawaran da zan baka a nan shine kada ka yarda ka saki yarinyar nan koda daddy baya raye a duniyan nan don wanan yarinyar kamar makamine a rayuwan ka nan gaba.
Shiru sukayi gaba dayan su bayan fadin haka da Nasir yayi kowa da irin abinda yake tunane a ransa gama shi umar dake tuna zancen kanin sa Aliyu a ranshi.

Ina zaune akan kujeran dining dake falon ina karatu don test din da muke dashi satin nan kafin aje hutun chrismas da duk kasan sai faman shiri sukeyi ko ina kafi shirye shiryen zuwan lokacin sukeyi a kasan.
Wayata ta dauki ruri lokaci daya hakan yasa na duba da sauri na furta mamu again ?
Da sauri na dana dauka tare da sallama ina gaida ita ta karba min tare da fadin ga su fauziya ku gaisa kamar yadda nayi maki alkawari dazun.
Mun gaisa da kanne na dukkan mu muji dadin hakan karshe sai mamu ta karbi wayan a hannun yaran tace sayadi na amsa da naam.
Tace dazun nice na kashe wayan don jin abinda kike shirin yi a gaban kawun ki.
May nayi mamu na tambaya a maraice tace kina zaton idan kin fadi magana kadan akan zaman ki da mijin ki hakan zai iya kara jefa kawun ki cikin rikicewa.
Jin muryan ki dayayi yau bakiga yadda yake faman saka maku albarka ba duk wanda ya shigo bayan kunyi waya yasan Alh yana cikin farin ciki yau.
Jikina yayi sanyi sosai lokaci daya na kasa furta komai mamu tace sayadi ina karatun ki da abindana koyar dake idan kana cikin damuwa kayi ?
Shin kin mata da irin rayuwan gidan nan da kika barni cikin sa irin makamin da nake fani dashi gare su baki daya shine addu,a.
Sayadi kiyu ta addu,a a rayuwan ki komai yayi tsanani maganin sa Allah ni kaina na sha ji a jikina irin zaman da umar keyi dake a can.
Saidai kona fada ba yarda za,ayi dani ba don hakan magana baida amfani gare mu maganan ma tonawa kanmu asirine kawai zamuyi.
Kiyi hakkuru a tafi a hakan kodon makiya kada su gane halin da ake ciki duk nan an baza kunne da idone aga yadda zaman naku zai kaya.
Don haka karnaji karna gani kowa ban yafe ki fadawa wanan zaman ba shima ya iya boyewa shida yake namiji sayadi sai ke mace ce ba zaki iya ba.
Yanzun haka ina jin wai wai a gidan nan tun zuwan shi kasan nan uwarshi ta hasa mai wuta kan lalai sai ya rabu dake .
A tonanen ta ya riga da ya bata maki rayuwan kurciyar ki don hakan idan ya sakoki bakin ciki da rakaici ne zai cimu har kawun naki.
Don haka nake son ki kara jajircewa sosai ki bishi yadda yake son zaman ku kada ki yarda ki nuna mai gazawa a bangaren ki kan hakan.
Kina jina ko sayadi ban son inji komai gamay da zaman ku sai dai idan kiyi hakkuri gaba zakiji dadin hakan sosai don hakkuri bai taba faduwa kasa banza .
Kina jina ko sayadi na amsa mata da eh mamu tace Allah yai ma rayuwan ki albarka yabaki zuria masu albarka a sanyaye na amsa da amin naji ta kashe wayan baya ki kula da kanki ki tsare mutuncin ki data fada min.
Na dade zaune ina kuka ina tunane na duba dare yayi sosai lokacin ga ruwan sama da ake ta tafkawa kamar da bakin kwarya.
Mikewa nayi zuwa daki bayan na kashe komai na falon da nake amfani dashi ina shiga dakin na aje waya da sauran abubuwan da na shigo dashi na nufi bandaki.
Alwala na dauro na fito na shimfida abin sallah a cikin natsuwa da kulawa na gabatar da sallah na har lokacin tuwa ake sosai a garin .
Na idar na dade a gurin zaune ina tunane ga dare yayi sosai barci ya kauracemin a idona sai faman sake sake zuciya da nakeyi.
Na fadi a fili a hankali ni yaya zanyi da rayuwata anty farida ta fada min nata shawaran yanzu kuma ga mamu da nata shawaran duk dai akan abu daya ake magana wanda ni hakan ma bai damay ni ba sam.
Gara maganan mahaifiyata duk a kan hakkuri ne gareni ba wani zancen bada kai ga miji illar in daure in samawa kaina madogara nan gaba.
Kaina na dafe daga yadda nake zaune nace Allah kaimun gata ka bani mafita kan wanan mutumin idonane ya fara zubar da zazzafan hawaye lokaci guda.
Bazan kara yarda da in takurawa rayuwata ba ko kadan zan watsar da komai in kama harkan gabata.
Kada watarana azo a samu na mutu ni kadai a gida ya zama dole in fara shiga mutane kamar kowa a gari .
Tun ranan naba kaina salama ga komai yadda yaya daukeni hakan zan dauke shi nima mu zuba mu gani dashi.
Ganin za,a shiga bukin addini a kasan na yanke shawara a raina in fita in sawo abinda raina ke so tunda akwai kudi a hannuna da ban san adadin su ba idan ya ban ajewa kawai nake ban komai dasu sai dan hawa taxi da sauran abubuwa.
Mun samu hutun makaranta muna gida don haka na shirya zuwa siyayya abinda raina yake so .
Nasan dan kwanaki ya rage manyan shaguna su zasu cika da jama,a don shagalin bukukuwan chrimas da zasuyi kwana biyu kuma su rufe.
Na shirya cikin riga da siket yan kanti har kasa sai dan hijjab dina dana saka a saman kaina takalma masu dan tsini ne a kafata jakkata na dauko na rataya na fito na rufe gidan.
Iskan garin na shaka mai sayin ke kadawa don ruwan da akayi aka dauke a lokacin takawa nayi zuwa inda zan samu taxi ya kaini gurin shiga jirgin kasa da yake tafiya a saman mono rail.
Shi wanan jirgin a sama yake tafiya anyi mai yar siririyar igiyar bi wanda ke cikin jirgin zai iya hango mutane da motoci a kasa .

ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:20 - ??5惙5惙5?: BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM YAN UWA MUSULMAI DA FATAN MUN TASHI LAFIYA UBANGIJI YA BAMU WUNI MAI ALBARKA DA DARE MAFI DARAJA A RAYUWAN MU AMIN, , , , ,


Mafiyawan muna cikin jirgin a nan zamu sauka ashe gurin ya cika makil da motoci da mutane nau,i daban daban sun fito sayayya don bukin kirisimeti.
Sai dana karewa wurin kallo kafin in bi ayarin masu tafiya da kafa muka shiga cikin plazan .
Sai ka turmusa wani kati da muka saya kafin kofa ya bude ka shiga ka hau na,ura mai tafiya da kanshi zuwa sama ko kasan ginan wurin.
Muna sauka muka shiga cikin plaza din komai nasu a tsare yake gurin wanan ne farkon zuwana gurin don haka na zama ba kauya a gurin.
Gurin kayan gwagwani na fara zuwa ina duba na halal kifi da naman gwagwani na kara siyowa sai pad da nafi bukata fiye da komai a lokacin.
Na juya wirin saida turare da kayan kwaliya na zabi wanda nake so mai isata kafin in juya gurin kayan sitiru na fara duba masu mutunci na zaba.
Ba wasu kaya bane irin namu sai gown da wanduna da su t,shirt haka na garo zuwa wurin biya kudi masu yawa aka chajeni na basu katina suka cire abinsu aka saka min cikin manyan kwalaye mai dauke da tambarin shagon nasu na fito.
Wanan karon taxis na nema don komawa gida saboda nauyin kayan dana lodo lokacin har bakin get din gidan mai motar ya tsayar da motar shi.
Da taimakon shi ya kaimin kayan har kofan shiga gidan gaba daya na biyashi kudin shi ya taf??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????i sai lokacin na sauke ajiyan zuciya ganin naje lafiya na dawo lafiya ba abinda ya samay ko kadan wurin zuwa da dawowa.
Ina tura kofan gabana ne ya fadi jin kofan a bude lokacin hakana na daure ina shiga da kayan da kyat ta ciki.
A razane na juyo ina kallon shi jin muryan shi a daidai lokacin da ban zata ba daga saman benen yana fadin daga ina kike haka yanzu da wanan kayan ?
Tsare shi nayi da ido kafin in ce na fita sayayyan abinda nake bukatane .
Ya sake jefo min tambaya da izinin wa kuma dake da wa kuka fita zuwa sayayyan ?
Nace bada izinin kowa ba ni kadai na tafi naga idan sun fara bukin kirisimati komai wuya yake a kasan .
Kai tsaye nake magana na batare da jin komai a raina ba gamay dashi sabanin da can da nake magana dashi ina jin shakkun shi.
Tsaye yayi sororo yana kallon yadda nake magana ina aikin shigo da kayana zuwa ciki daga kofan gidan.
Tsaye yayi sororo tare da kare min kallo cikin yanayin mamaki karara a fuskan shi.
Sai da na gama jido komai zuwa ciki na dawo na samu ya shiga dakin sa ya rufe hakan ya ban daman shiga nawa dakin nabar kayan a nan falo daga sunan zuwa fitsari sai na tsaya na dauro alwala nayi sallah ban fito ba saida na sauya kayan jikina na sauko kasa.
Kitchen na fada dafuwa mai sauki nayi muna wanda ganye yafi yawa a cikin sa sai dan sauran abubuwa na jera muna a falo.
Wanka nayi na daura wani alwalan magariba na fito sallah na gabatar kafin in gyara jikina kwalliyan wando da yar t,shirt nayi a jikina na sauko don cin abinci.
Ban san da fitowan shi falon ba yana zaune yayi dadaya da kayan dana sayo na barsu a gurin yana kallo sai gani na fito daga daki.
Ja nayi na tsaya ina kallon shi da mamaki sai lokacin na iya tuna daga tafiya ya fito ban samu gaida shi ba na dan raba gefen kujera ina gaidashi tare da mashi yaya kawu da jiki da mutanen gida duk lokaci daya nayi mai tambaya a jere.
Dago kai yayi kamar da mamaki yana amsawa a takaice tare da fadin kayan abincin ki sun karene da kika sayo wanan ?
Basu kare ba ina dai ra,ayin canzawane kawai yasa na sayo su don kawar da zancen nace dashi ga abinci a dining yaya.
Shiru yayi min ba tare da ya amsa ba na dauka ba zaici ba don bai kula da maganata ba sai kanshi daya dafe ya mayar da bayan shi saman kujeran.
Tambayan dana jefo mai yasa ya dago kai ina fadin yaya yaya su Amma da mamu suna lafiya ?
Su kika sani ke nan ya fada yana mikewa daga inda yake ya nufi gurin abincin ciki ciki nace don nasan su zasu ce a gaidani mana.
Ya juyo yace OK to su din ma basu ce ba don ban fadawa kowa zuwana nan ba.
Mikewa nayi zuwa bakin dining din na bude abincin da sai tururin zafi ke tashi cikin cooler na fara zuba mai ba tare dana kalle shi ba.
Nima na zuba nawa naja kujera na zaune daga gefe na fara ci ba wanda ke magana a cikin mu sai abinci muke ci da sake saken zuciya.
Bell yayi kara da alaman akwai wani a waje yana son shigowa gidan da dan mamaki ya kalloni nima kallon shi nayi kafin in mike zuwa kofan cikin raina ina mamaki.
Na bude kofan a hankali ina kokarin duba kowaye a kofan wata farar fatace tsaye a kofan dauke da kwalin cake tana murmushi tace min happy chirismas tana miko min kwalin dake hannun ta.
Murmushi nima nayi don na sheda ta makwaciya ta ce matar duk da babu ruwana dasu sai wani lokaci mukan dan gaisa sama sama, da safe da ita.
Hannu na mika na karbi kwalin da take miko min nace same to you thank you wishi you many many years retune.
Matar taji dadin addu,a danayi mata tace saboda ni makwabciyar tace duk da taga ban kula kowa a layin yau dai ta daure ta kawo min kirismas gift har gida.
Nace na gode hannun daya mika zai dauki ruwan dana aje mai gefen shi yasa ta farga dashi ta dan juya tana gaidashi ya amsa mata ciki ciki.
Tambayana tayi wanan yaya kuke dashi na bata amsa da brother dinane shi tace kuna da kyau family din ku sosai wani ya taba fada min hakan kuwa ?
Nace mutane da yawa suna fada min hakan ba ita bace ta farkon fadin hakan ta juya tana fadin zata tafi ta gode da karramawan da nayi mata a gidana.
Tana fita na rufe kofan na juyo na samu ya kakafeni da idanu yana min wani irin kallo mai tatare da ma,ana.
Ban koma wurin abincin ba sai na nufi wurin kayan da nasayo ya watsar min dasu a falon na tsuguna rai bace na fara tattara kayan a hankali.
Muryan shi naji yana fadin har makwatabta kika fara janyo min a gida ashe ke wata irin yarinyace da bata jin magana haka ?
Ban iya bashi amsa ba illa shirun da nai masa naci gaba da dauke kayana a kasa ba tare da na juya ba a yadda nake.
Wayan shi da aka kira ya rabamu ranan don tunda na shige da kayana ban sake fitowa ba sai washe gari.
Ban tabbatar da yana gidan ko bayanan ba nidai na hada breakfast dashi ranan na koma daki nayi wanka na shirya cikin daya daga cikin dogayen rigunan dana sayo jiya rigan jace andan bude gefen shi don hakane ni nasaka dogon wando daga ciki don kada sharabana ya fito fili.
Ina matukar son abu kalan ja ko baki da yellow da sky clour saukowa nayi na nufi kitchen fridge na bude na dauko lemo kwalba na fito.
Yau haka kawai naji zaman ciki ya isheni don haka ina son shakan fresh air a waje.
Dan barandan gidan da mutum zai iya tsayawa yasha iska na bude na fito akwai kujeru biyu wurin da aka tanada don wanda ya tsaya wurin.
Saidai ban zauna bani staye nayi ina karwa gidajen makwabta kallon yadda suka kawata gidajen nasu da shaguna don kawai zagayowan wanan bukin nasu da muke hutu a kansa.
A yadda nake tsaye gurin daga gani babu tambaya na samu nishadi sosai a lokacin .
Saboda yadda nake tsaye ga airpiece makale a kunnena ina

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login