Showing 297001 words to 300000 words out of 419207 words

Chapter 100 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1501

bude bude kofofin gidan ga Salma na mata fada a bayanta ta bari haka baida kyau.
Ki shigo gida kina masu bincike sai kace an turo mu muzo mata rashin mutunci sai naji tace wa yar uwar .
Halan gidan tane da sai da izinin ta zamu yi komai gidan dan uwan mu ne fa ba nata ba kuma kin dai san dole in duba abinda tazo dashi tunda taki ba kowa tsaraba sai yan dakin su kawai ta aikowa katon jakka maman su ikilima ta gani take fadawa mama ranan.
Don haka wanan shegiyar sai mun nuna mata gadara da isa akan dan uwan mu zata shiga hankalin ta.
Jin hakan yasa raina ya baci nasan ba zuwan girma da arziki sukai min ba ke nan ina shine bada Nafisa ba da take wanan magana haka .
Don haka ina jin abinda ta fada tana shirin bude kofan dakin yaya nace wanan wani irin rashin tarbiyane haka kuma Nafisa ?
Gaba daya suka juyo don basu san ina tsaye a wurin ba da suke magana nace ya haka zaki shigo min gida kina bincike kamar an turo ki kiyi min hakan ?
Gidan ki fa kikace ta fada tana min wani irin kallo a wullakance nace kwarai kuwa ko gidan ki ne wanan ke na tambaye ta ?
Tace magana barnan baki amma dai kin san gidan dan uwan mu ne na jini daya ko don haka zan iya yin komai fiye dake a gudan nan ma tunda ke auren ki kawai yakeyi .
Nace mijinane tare muke kwana muke tashi tare a shimfida daya muyi komai tare a gidan nan dani dake yanzu wafi kusanci dashi cikin mu.
Au har wani gadara kikeyi dashi na kuna kwana tare kuna tashi tare dashi kwana nawa ya rage maki kuyi tare dashi.
Nafisa kinsan abinda kike fadi kuwa kizo gidanta kina fada mata maganan banza haka kamar wata sa,ar yin ki matar yayan mune fa yanzu.
Kyale ta anty Salma dama abinda tazo yi mun ke nan dadin abindai itama mace ce kamata gidan wani zata tafi ba zata tabbata a gida wurin mama ba.
Sannan da kike fadi kwana nawa ya rage mina gidan nan ko yanzu dai na bar gidan nan na riga da na shamci kowa don ko yanzu aka kashe biri, biri yai barna don tun ba yau ba aka so ya sako ni bai sake ba .
Yanzu ko ko ya saka ban saku ba don mun riga da mun zama daya dani dashi yanzu rai uku ba wasa bane Nafisa koma ki fada wa wanda ya turoki da ya makara wallahi yar zakanya ta girma.
Nafisa tace da mamaki wanan magana ke nan nace mama ba sa,ar yina bace kin sani kedai da kikazo fada min baki da baki dake nake zance yanzu.
Nafisa dama saidana fada maki ki bari yanzu gashi kuna kokarin haddasa tashi wani sabon tashin hankali kuma.
Fatima don Allah ku bar wanan zancen haka kada yai maku nisa yakaiku inda ba a so kuma yakai nace Anty salma ya kai mana dama da gaiya tazo gidan nan don ta fada min abinda taga dama a gamay dani.
Iya kadai ace yaya ya sake ni ko badai raina zai rabani dashi ba ai kuma rabamu akayi da karfi da yaji bada son ranshi ba kinga ashe ba ni kadai zanyi wahalan ba.
Salma tace haba Fatima don Allah ki daina biye mata kuna wanan abin haka bai dace a tsakanin ku ba gaskiya.
Nagode anty salma insha Allahu nagode bazan kara tanka mata ba kuzo mu zauna a falo.
Anty salma idan kin fito ki samay ni gida tace ta fita tana bakaken maganganu na rakata da harara .
Fatima kun zo lafiya ta fada tana kallona sai lokacin na juyo na kalleta da kyau tunda suka shigo ban mata kallon kyau ba.
Anty salma mun samay ku lafiya ya gida yaya yara da maigida na tambayeta cikin nuna mata kulawa.
Ta danyi murmushi tana fadin kun shige England kuyi shiru abin ku haka har kun tara iyali haka masu yawa ?
Nace kai anty salma nice dai ai aka kwara da ban zuwa gida shikan ai ko yaushe kuna ganinsa a kasan nan.
Mun zauna munyi hira sosai da ita take ban labarin tayi karatu baya auren mu sai dai takardan ta baiyi kyau ba mijin ta kuma yace ba zai sake barin taci gaba da karatu ba.
Mun tashi munyi sallah muna cin abinci saiga yaya ya shigo gidan ranshi a bace ganin salma a gidan bai hanashi ya tambayeni ba a cikin fushi.
May ya hadaki da Nafisa kuma don kawai tazo gidan nan zaki mata rashin mutunci har kina mata gori.
Ni din nan dai yaya ita baka tambayeta ko mai ya kawo har nayi mata gorin da tace nayi mata din ba.
Shiru ya danyi na wani lokaci kamar mai nazarin magana na a lokacin kafin ya bude baki cikin natsuwa da kwantar da murya yana fadin.
Na fada maki ki kara da hakkuri ga duk wani abinda za ai maki ki daure ki shanye amma baki dauki magana ta da muhinmanci ba kika biye mata kuka saida hali keda ita.
Har mama ta kirani sai abinda ya bace mata a baki yau shine bata fada min ba a kanki.
Kayi hakkuri yaya don Allah Nafisa bata da gaskiya don a gabana akai komai wallahi don tare muka shigo gidan nan da Nafisa.
Sai kayi hankali dasu yanzu akan matar ka tunda kasan komai basai na fada ma ba.
Amma ba hujja bane ace mun shigo gidan nan da gadara don kawai muna takama gidan dan uwan mu ne nan muce zamuyi abu cikin gaba gadi.
Mumafa matane muna da yan uwan miji bazamu so suzo suyi muna yadda nafisa tazo tayiwa Fatima gaba gadi ba gaskiya.
Salma ita ba zata koyi hakkurin zama da yanayin su ba har lokacin da Allah zai sa wanan abin ya lafa tunda tasan yanzu mama tana da cikin mu a ranta.
Wanan abi yasa nake ta gudun zuwan mu gida tuntuni na dauka zuwa yanzu Zarah tayi wayau sanin irin halin da muke ciki na barazanan mama a kan mu.
Na gaji dajin maganganun shi nace yanzu yaya mai nayi cikin wanan maganan da kake ganin laifina don Allah ?
Yanzu daidaine ace Nafisa ta shigo gidan nan ta dinga shiga wurare har dakin kwanan ka wai tana duban abinda muka zo dashi.
Dakina fa kikace ya fada a fusace nace ga anty salma nan tana mata magana tace wai sai taga komai da muka shigo kasan nan dashi.
Nan anty salma ta kwashe komai daya faru ta fada mai yace shine daidai nafisa ashe bata da hankali haka ban sani ba ?
Jin yana fadin haka na mike na bar su zaune na shige dakina sai da anty salma zata tafi ta aika maria ta kirani na fito nace anty salma zaki wuce ke nan tace eh fatima.
Daga nan gidana zan wuce don yanzu nasan hardani mama tana can hake dani idan naje yau ba zan shata da dadi ba.
Ledan dana fito dashi na mika mata ina fadin anty salma ga wanan kiyi hakkuri dashi kafin kayan mu yazo don Allah a gaida sauran yaran da maigidan ta amsa da ta gode shima ya ciro kudi mai yawa ya bata yana fadin sai mun shigo wurinta.
Bayan tafiyanta na juya na nufi hanyar shiga dakina yace ina zaki baki ban abinci ba ?
Ban dauka kana jin yunwa yanzu bane na fada ina kallon shi yanayin fuskanshi ya sauya.
Yace kina nufin bazan maki fada ba har kike nuna ban isa ba a gaban mutane da wani kike son inji Zahrah da maganganun su mama koda naki yanzu ?
Ni yanzu wani abin kuma na kara yi bayan wanda akace maka nayi kuma ka yarda dashi.
Dole in yarda zahra tunda na fada maki tun farko kema kuma kin sani auren mu da zaman mu ba son shi mama da wasu a cikin gidan mu sukeyi ba.
Gashi har mama yau tana kirana da wai ina bare bare akanki da yan uwan ki na watsar da nawa yan uwan na kama naki.
Don Allah zahra ina kara rokon ki ki kawar da kanki ga duk wani abunda mahaifiyata da yan uwana zasuyi maki ki bari in rabu lafiya dasu kamar yadda ko wani da yake son rabuwa da mahaifiyar shi lafiya.
Ta hanyan ki kadai zan iya samun haka wurin kawar da kanki da toshe kunuwan ki ga duk wani fitina ire iren haka da zasu tayar nan gaba don kawai su samu dalilin fakewa ta hanyar tuzuraki bukatan su ya biya.
Aurena ya samu tangarda wanda bazan taba son hakan ya faru ba tunda kinsan kece dai ba a son zaman ki dani ko ?
Ya kawar da zancen yana fadin ki ban abinci inci banci komai tunda safe na fita gidan nan.
Banyi magana ba sai nufar wurun cin abincin danayi ina dubawa kafin ya tako a hankali zuwa wurin ya zauna har lokacin banyi magana ba.
Ina son mu koma lagos don zama garin nan naga kamar zai iya jawo muna matsala da mama.
Nace in dainice ai ba wani abinda yanzu zatayi wanda ban san manufar yin shi ba don haka ba sai har munkai ga barin garin nan ba ai.
Ko yan uwa bamu zagaya ba yaya zakai maganan komawa wani kasa kuma yanzu duka duka har yaushe muka sauka garin nan ko kwana goma bamu cika ba fa.
Gobe ina sa ran Amma zata bakunce mu gidan nan kuma idan tazo ba zan barta ta koma ba sai ta kwana biyu damu nan gidan .
Aiko wanan zancen yai min dadi sai in hada ita da murja mu zauna kwana biyu nan din in samu ta sake jikin ta da dakyau a gidan nan.
Yadda duk kikayi nadai fada maki gobe zanje in dauko ta in Allah ya kaimu da safe.
Ranan nasa aka gyara dakin da Amma zata zauna aka kara saka komai da zaiyi daidai da rayuwan ta babu takura sai jiranta kawai muke zuwa washe gari.
Sai dai duk abinda nake fadab mu da Nafisa bai fita raina ba ina nazarin maganganun data yaba min a cikin fadan sai da dare na kira mamu ina sheda mata yadda duk mukayi da Nafisan.
Sai cewa mamu tayi dama mai kike nufi ai kadan ke nan ma kika gani indai dangi mijine da kanne miji ake farawa kafin akai ga maya gaba daya.
Saidai idan ka iya hakkuri kana shanyewa sai abin yazo maka da sauki a rayuwa komai yazo ya wuce kamar ba,ayi ba haka rayuwa take.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:32 - ??5惙5惙5?: BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM SIRRATAL, LAZINA AL,ANTA ALAIHIM, , , , , ,

Washegari bayan ya karya ya fita ya ja gida saida ya shiga suka gaisa da kawu suka dan taba hira duniya dashi ya mike yana fadin zai shiga ya gaida su mama.
A falo ya samu mahaifiyar shi tana waya tana ganin shi ya shigo ta katse wayan suka gaisa ya samu wuri ya zauna saman kujera.
Dan shiru ne ya biyo baya kafin hjy tace dada jiya dai matar ka ta nuna min ta isa ta samu wuri a gidan nan har da kora min ya tayi daga gidan.
Dan murmushi yayi kafin yace mama har zarah ta isa ta kori ko dan aikin gidan nan gida balle Nafisa yar uwata.
Gashiko ta kora din an gani ta nuna yanzu suke da kai da komai naka yar uwanka bata da iko da abinka yanzu.
Mama Nafisa dai ita ta kori kanta don na samu salma a gidan ta fada min komai daya faru Nafisa itace bataje da gaskiya ba.
Ya isa ta daga mai hannu tana fadi rai bace na fahinci ka goyi bayan matar ka kaida salma ke nan .
Yanzu basu da ikom zuwa gidan ka suyi abinda ransu ke so saboda ka auro yar gwal ka aje a gidan ko kada ranta ya baci.
Mama ayi hakkuri don Allah da Nafisa da Zarah duk yarane dukkan su ya kamata a tsawata masu jiya nayi mata magana ba zata sake wanan halin ba insha Allahu.
A,a tamayi ai wurin yi ta samu don haka tana da daman da zatayi duk iya shegen da taso a gidan ka.
Dan kasa munafuncin da ka kulla lokacin da nake bugama waya akan ka sako masu ya cewa kake dani kana jiran ta gama karatu da mahaifin ku yace ka sakatane a can idan kunje.
Ashe kasan munafuncin daka kulla da kai da mahaifin ka don kawai ku bakanta min rai babawo har ka yarda ka hada zuria da wanan matsiyatan mutanen.
Tau yau dai zaman ta da kai ya kare ina son ka sallamar mata yarta ta dawo gun uwar ta suci tsiyan su tare.
Mama me tayi da zan sallame ta ya bukaci sanin dalili cikin natsuwa tace tun yanzu tana ganin ta kafu a gidan ka don ta haifa maka wa yan nan yaran masu zubin zabaya yan ruwa biyu take ganin sawun ta ya doke na rakumi a wurin tsayi har zata iya gayawa Nafisa irin maganganun data fadamata kuma wanan sakaran salma na tsaye tana ji bata iya daukan mataki akan komai ba.
Haba mama ai diniya sai ta zageki keda Nafisa ace nazo da matana lafiya kan Nafisa na saketa .
Ni nafison a bari sai idan tayi wani abinda ya shafeni ko ya shafe ki wanda kowa idan yaji yasan muna da hujja mai karfi ba za,a zargeki ba kan hakan.
Amma yanzu idan na saketa kan Nafisa ai mutane ba zasu gamsu da hukincina ba karshe ma in dorawa Nafisa baki jini kan hakan .
Ko mai mutane zasu fada su fada bai damay ni ba ba zan taba yarda maimuna da yarta suci galaba a kaina na muddin ina raye koda hakan na nufin komai nawa zai kare akansu kuwa.
Da sauri yace mama may wanan maganan naki yake nufi hakan mama don Allah akan wanan dan magana kada ki yarda shedan yai galaba a kanki ki kaucewa Allah.
Ya juya wurin da Nafisa take rakube yana fadin ke kuma ki fita harkan Zarah na fada maki ku barmu namu ya hadamu da ita idan ma zan saketa ne a lokacin zan saketa ba wanda zai zargeni akan komai.
Amma yadda kuke nufin inyi abu a cikin rashin tunane haka kowan ku nan sai wanan abinda kuke so in aikata yanzu ya shafa gaba dayan mu.
A yanayin da yake magana cikin bacin ran da basu taba ganin ya nuna ba sai jikin mahaifiyar tasu da Nafisa yai sanyi lokaci daya.
Nafisa ta matsa da sauri lokacin da yake shirin tashi tace yaya kayi hakkuru nima daga baya nasan ban kyauta ba kamar yadda Anty salma ta lurar dani daga baya.
Mama kan dago kai tayi tana fadin anya babawo mutanen nan basu gama da kai ba duk da shawaran daka bayar yana da kyau amma ni sai ina hango kamar sun gama da kaine.
Ina tsoron yadda uwarta tamayar da mahaifin ku idan ba kaima haka ake son mayar da kai din ba ji yanzu yadda ranka ya baci ka rufe ido kana fadawa kanwarka magana akan yarinyar nan.
Mama ni ba wanda ya isa ya gama dani sai Allah dayayini kawai dai raina ya bacine yadda Nafisa taje gidana tana rashin mutunci ko yaya take da zarah ai dai matatace a yanzu ko ?
Don haka ba zan zura ido suna wullakanta min aurena ba duk da irin kyautata masu danake don may ni zasu so su muzantani.
Hjy ta rasa baki magana kanta ya daure don a lokacin bata son wani yasan abinda Nafisa taje tayi min a gida.
Don haka ta rasa yadda zatayi ganun ya tubure mata a karo na farko yana fada a gabanta kan matarshi da ta tsana.
Ya sake kuma ya kafa mata wasu hujjoji yaki ya saka wai saida hujja mai karfi bai kara second ba bayan ya gama magana da Nafisa ya bar falon mahaifiyar tasu.
Mama bata taba tsinkewa da lamarin danta ba sai wanan ranan don gaba daya ya juye mata ya zama kamar na mijin zaki lokaci daya.
Part din Amma ya nufa yana shiga ya samayta zaune tana shafa mai ya zauna ba tare da yayi magana ba bayan sun gaisa tunda tsaye kafin ya kai zaune.
Jin shirun yasa Amma ta dago kai tana fadin lafiya kake ko sadauki ya danja tsuki yana fadin ba komai Amma ke nazo dauka muje gidana yau.
Yau din nan yace eh ina son kije ki dan lekamu kiga yaya muka sauka ai na gani tunda naga iyalin daka tara da idona a duniya.
Yayi murmishi yana fadin ki shirya muje na sa zarah ta shiryawa zuwan ki tun jiya zuwa na dai Amma tace ?

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login