Showing 63001 words to 66000 words out of 419207 words

Chapter 22 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1439

fito yi sai ka bari har diyan gidan su fito ka binciki sirin su a wajen su ni kaga tafiya ta.
Ido kawai ya tsura min da mamakin irin karfin halina yar ficiciya dani nake wanan zancen ga fuskana a boye da duk wani surana a cikin hijjabi.
Haka a raina kuma ina tasbihi akan irin baiwan da Allah yayiwa wanan mutumin dake tsaye a gabana.
Tsayi, hasken fata kamar balarabe dashi kyau fuska, ga uwa uba wayewa da na hango karara a fuskan mutumin.
Don Allah ki taimaka ki shiga ki fadawa hjy jummai cewa Umar ne danta a waje yake masu sallama ya fadi a takaice yana gyaran tsayuwan shi.
A hankali na maimaita sunan nace Umar Umar din da nake jin Amma na yawan maganan sa ko da yaushe ?
A she Umar din bature ne ma sai na dan ja tsuki ina fadin ni yanzu makaranta zan tafi dadai zaka samu wani ka aika da zaifi don ina ganin ma ba wanda ya tashi a gidan yanzu.
Ko ni don zan tafi islamiya ne yau muna da tulawa yasa ka ganni nan yanzu, ido kawai ya tsura min yadda nake zuba ba gajiya da magana.
Ki taimaka don Allah ki sanar masu nace wai kai ba kace gidan ku bane to ka shiga mana ni ban san abinda zai hada ni da part din nan na su a raina ma mutum wayau da safen nan.
Ganin kamar ma baiji abinda nake fadi ya mayar da hankalin shi ga wayan shi yasa na juya ina gunguni zuwa cikin gidan har kofan hjy jummai na je sai da na tsaya nayi shawara na fara nokin din kofan da karfi don nasan ko na tsaya bugawa a hankali ba bude kofan zasuyi ba shiyasa nayi masu na mahaukata .
Da zagi a bakin Nafisa ta fito tana fadin wani dan rainin wayau ne haka ke dukan kofa kamar gari zai tashi da safen nan ?
Arba mukayi ta galla min harara nima na mayar mata take fadin ke lafiya kika zo muna haka da sassafen nan kina dukan muna kofa.
Idan kin gama ki fadawa maman ku wani yana mata sallama a waje yace wai ace Umar ne danta yazo ina fadin haka na juya don in wuce.
Ta riko hannu na tana fadin ke hjy sa,ar kice da zaki mata wanan wasan da sassafe haka nace akan may zan mata wasa haka ?
Nace na saba wasa da kene abinda yace in fada ke nan na fada maki tare da galla mata harara ina fadin, ni sakeni in tafi don Allah .
Idan baki fada ki bari sai bayan na fisge hannu na daga rikon da tayi min na fara tafiya naji ta sake wani ihu.
Karan Ihun da ta sake ne ya sa na dan juyo ina kallon ta na tabe baki na bar gurin da sauri ina fadin kamar wani basarake yazo gidan.
Tun ban karasa fita ba naji gida ya rude ihun yan part din hjy jummai suka nufo waje da gudun su hjy jummai jikin ta har rawa yake don daukin ganin dan nata.
Yana ganin na fito yana tsaye kamar yadda na barshi saidai wanan karon ya dan jingina da motar daya fito daga ciki.
Na kalle shi sau daya na dauke kaina ba tare da fadi komai ba na nufi hanyar islamiyan mu da kafa sai dai ban yi nisa ba yaya Ahmed ya tsaya a gabana da mota.
Yace ba nace ki daina fitowa ke kadai da wanan safiya haka ba baki tsoron a sace ki wani kallo nayi mai daga cikin nikaf dina a raina ina fadin kamata za a sace ?
Ya bude min motar na shiga ya tayar muka dauki hanya sai lokacin nake gaida shi da kwana ya amsa min tare da fadin ina sauran suke nace suna gida sai dai ban sa zasu samu zuwa ba yau dan sunyi bako a gidan wani ne wai Umar yazo yanzu.
Cikin dan zaro ido yace Umar kika ce nace haka yace sunan shi daya turani in masu sallama.
Umar dai dan Alh yazo garin nan bayan su habbib da suka zo nace eh haka yace sai dai ina ganin kamar wanan din ko bature ne ko balarabe.
Yace kiji nace dan hajiyane da Alhaji zaki wani ce bature ne shi ki dai iya kanki dasu don ba mutunci ne da su ba koga kannen su.
Sai dai muna zuwa na samu ana dawowa daga islamiyan wai malam ba zai samu fitowa ranan ba haka yasa muka juya muka nufo gida.
Basu shiga ciki ba har lokacin da Ahmed din ya sauke ni suna farfajiyan gidan ana murnan zuwan bakon su .
Ahmed din bai tafi ba shima daya sauke ni ya shigo su gaisa dashi nikan nazo na raba su har su Amma da mamu da Alh kai kowa na gidan yana waje a lokacin har bakin da suka zo din.
Shiko bakon sai dadi yake ji na ganin sa a cikin dangin shi suna nuna mai so da kaunan juna a lokacin.
Haka nayi kokarin raba su zan wuce sai muryan Amma naji tana kwala min kira A ruwa ke Aruwa na juyo inda nake jin muryan nata.
Da hannu tayi min dakuwa tana fadin kinci gidan ku baki ganmu bane ga yayan ku daya dade da bata yau ya gane hanyar gida yazo.
Kai na daga na kalli bakon sau daya nace Amma nafa riga kowa ganin sa gidan nan don nice ma ya aika in fadi zuwan shi.
Na juya da tafiyana da suke kira na yauki da yanga zan wuce abina da mamaki gaba daya suka bini da kallo.
Don kin masa iso sai ba zaki gaida shi da zuwa ba kamar yadda kowa ya fito taron sa a gidan .
Naji kamar in fasa ihu don tsohuwar na son ta takura min kan gaida shi nace kai Amma duk wanan taron da kukayi a kansa bai isa ba sai na cika zai sani ?
Ke kan anyi yarinyar kawai a nan gaisuwan zai rage kiko kara ki idan kinyi yarinya sai gardama kamar arnan farko .
Muryan Alh ne yake fadin Hajiya kyale ta ko banza kada ya shamce ta kisa ta gaida tobashin ta akan dole balle tace sun gaisa da yazo.
Bai kai ga rufe baki ba muryan hjy jummai ya tare shi tana fadin hajiya data gaida shi da karta yi ai duka daya ne.
Ki duba nan duk yan uwa ne suka baibaye shi ta ko ina kika diba a gidan nan don haka barta kawai ta rike gaisuwan ta.
A daidai lokacin da takuran Amma yayi min yawa har na isa dan kusa dashi inda suke saye da yan uwan shi da suka baibaye shi.
Fari sol dashi sai yanzu zaka gane hakan da yake a tsakiyan kannen shi duk da suma di farare ne sol dasu.
Yana cikin suith bakake masu taushi da tsada agogon hannun shi baki sai sheki yakeyi a tsintsiyar hannun shi daya dan fito waje daga saman kot din jikin shi.
Ga bakin gashin kansa dana dan sajen daya bari a fuskan shi ya kwanta lub a jikin shi yana sheki daganin sa ba sai an fada ma ba duniya tana yayin sa a lokaci .
Duk da fuskokin su yana dauke da fara,a banda nasa dake a daure wanda babu alaman sauki a cikin sa ba sai an fada ba kansan irin mutanen ne da babu wasa ga al,amarin su dagani dai zaiyi wuyan sha,ani duk wanda yasan jan aji da isa yasan ya zauna ga wannan bakon dan Alhajin da yazo .
Sai na kasa bambamta shi da kanin nasa habibbi wayafi wani jin kai a cikin su don dan dama dama shi wanan Aliyu kamar ya fisu saukin kai a cikin su.
Ina mamaki yadda yan uwa zasu baibaye mutum ya kasa fara,a gare su haka zai kai shekara talatin ga haihuwa ko kasa da hakan .
Yana da tsayi sosai don zan iya cewa mahaifiyar su ya kwaso wurin tsawo sai ya zarta ta yana da dan lange langen jiki ba sosai ba wanda ke nuna ya jiku da ilimi ya goge sosai da duniya.
Cikin yar murya da sai ka saurara zaka jini nace sannu da zuwa ya hanya ?
Na fadi ina kallon amma cikin jin haushin takura min da tayi din a lokacin na wuce abina fuuu cikin gida ba tare da na tsaya bin ta kowa ba a lokacin don haka banji amsan shi ba ga gaisuwan da nayi mai din.
Ina jin Aliyu na fadin big bros haka unexpected ka diro muna kasan nan dai na shige su na nufi hanyar part din mu ba tare da naji sauran maganan su ba.
Su salma dake gefe suka tabe baki tare da fadin wanan da itace yar gidan nan bamu san inda tsiyanta zai tsaya ba .
Uwar ta amsa da fadin tsiyar abin tsiwanta ya tsaya ga agolacin gidan ku don dole ko tabi mutane.
Ni yanzu banda takaici a rayuwana, dama ita din ba mace bace ta dubi rufin asirin da Allah yai min naku don duk cikin ku babu na yardawa.
Ga ilimi da rufin asiri Allah ya bani ta ko ina haukan yar ficiciyar yarinya da uwarta ke ingizo ta tai muna rashin kunya ba zai taba damuna ba.
A cikin wani kasalalen murya yake fadin mu shiga daga ciki ko ku huta nima da gajiya a jikina yanzu haka.
Sai lokacin ya tuna da drivovin daya bari a kofan gida inda yace wa Aliyu yasa a sauke mai kayan shi akai sashen Amma don shi bakon Amma ne a gidan.
Ran hjy jummai baiso haka ba ga kuma kowa a wurin haka ya sakata dariyan wayayya aka wasance da fadin aiko ka kyauta babawo don ka wankewa hajiya laifinta wurin Aliyu ke nan don dafa isowan shi garin nan suka fara fada kanka inji mama hadiye dake fadi cikin dariyan fara,a.
Yace ai gwago ni na hannun daman Amma ce tun asali bana iya mantawa da Amma cikin rayuwana har abada don ta ban gatan da ban iya mantawa da ita.
Nan dai aka wasance hjy na ganin irin ganimar da danta ya shigo dashi akan idon kowa kattan mutanen nan sukai ta jida suna kaiwa part din Amma.
Sai wasu ne yake cewa a wuce dasu part din mahaifiyar tasu ba yadda ta iya dole ta sa ido tana kawaici ba don ranta ya so hakan ba.

Ni dai har na kwanta in dan huta can naji muryan mamu na fadin ina anty ku take suka ce ina ciki na kwanta sai gata dakin ta shigo.
Sayadi barci kike ko may a lokacin na dago ina fadin na kwanta ne in huta mamu munje islamiya ance malam tafiya ya kamashi yau ba karatu.
Tace Allah ya dawo dashi lafiya sai dai sayadi duk wanan nasihan da nake maki kamar baya aiki a kunnen ki.
Yanzu ace kin shigo gidan nan kin gama a cikin yanayin farin ciki ki iya kada kanki zaki tafi ba tare da tsayawa ba badon gwago tayi maki magana ki gaida yayan ku ba ashe ba zaki gaisheshi ke nan ba.
Nace mamu sai da na gaishe shi fa nice ma ya fara gani daya iso a kofan gida na fadawa su part din su gashi a waje.
Mamu ta daga min hannu tana fadin idan zaki gyara wanan halin naki ki gyara don ni kike jawa zagi a gidan nan.
Ace kaida dan uwanka ba zaka gaisa dashi ba sai an tilasta maka gaisuwa da yake da lada a wurin Allah.
Amma ke ko yaushe sai abinda za a zageni akanki kikeyi gaskiya bazan kyaleki a kan wullakaci ba ta juya ta fita daga dakin ranta a bace.
Muryan Alh naji a falon mu lokacin yana tambayan ta dawa take fada haka take hasala tace ni da yarinyar nan ne sayadi wallahi wanan halin nata na nakasa ban son shi Yaya.
Yace haba may ye a ciki ina ko kannen nasa kinga ai basu san shi ba balle ita da tazo gidan nan kamar yau.
Zata daina idan ta saba dasu wanan ai na bakinci take masu don bata saba dasu ba hakan ma nada kyau ai ki godewa Allah da halin ta yake haka kinga baki da fargaban komai da ita.
Ina jin shi bai fita ba sai da yaga ya kwantar mata da hankali a kaina ta sauko har suna yan dararakun su na ma,aurata yabar part din.
Niko ina daki raina a bace da haushin Amma ranan don itace taja min wanan fadan da batayi magana ba da kowa bai farga dani a wurin ba.
Ko banza yaya nake a cikin gidan wurin bangaren tsana da tsangwama da nake fuskanta a wurin mutanen gidan
Sai mama hadiye da yaran su da Amma nake dan raba inji sauki sai ko bangaren mahaifiyata da kowa ke ji dani.
A ranan dai murna wurin hjy jummai ba a magana sai dai a wani bangare tana cike da jin haushin yadda yasa akai masa tarkacen shi dakin Amma.
Bayan sun gama hiran su na yaushe rabo da mahaifiyar shi da kannen shi ya nufi wurin mahaifin shi tare da yan uwan nasa.
Daga can suka nufi part din su da aka gyara masu a gidan inda ya tarar da wurin kamar yadda yake bukatan shi haka yasa bai nuna masu komai ba a lokacin.
Don komai na bangaren a gyare ya samay shi tsaba sai kamshi ke tashi a ciki haka yasa ya kwanta ya huta don dama da gajiya a jikin shi sosai.
Tun shigan shi ya sauya kayan jikin shi zuwa kananan kaya ya bi lafiyan gadon dake dakin don samun natsuwa ga azumin dake a bakin shi.
Sai bayan la, asar ya tashi yayi alwala ya nufi masalcin unguwar don yin sallah bai shigo ba sai gab da shan ruwa ya shigo gidan.
Kai tsaye part din Amma yace kanin shi Aliyu ya rakashi su sha ruwa a can inda suka samu Amma a zaune tana jiran lokaci.
Yace tsohuwa mai ran karfe gani nazo musha ruwa yau a tare dake ta kalleshi cikin fara, a da jin dadi tace.
Wanan aiki sai Umar sanda mazan fama wanan hatsabibin tun da yazo sau daya ya shigo dakin nan nawa balle ace maka wanan miskilin kanin naka guda shi ko sau daya ma bai lekoni ba.
Don haka ne nima bai a cikin lissafi na Aliyu yace ga dai miskilin zaune a gaban ki ai don kin samu kuna dasawa ne dashi bai samu zagin ba da tafi kowa zaguwa a gare ki gidan nan.
Lumshe idanuwan shi yayi a hankali tare da fadin ka san ita Amma ta daban ce a wurina don har yau banji akwai mai fadana a gurin ta ba.
Dan karamin kanin su dake tare dasu a lokacin yayi caraf yace akwai yaya don wanan A ruwa din kamar ta fika fada yanzu a gidan nan don ko kuda ya taba A ruwa zakaji Amma na fadin marainiya ce ai.
Amma tace ja,iri so kake ka hadamu fada yo in ban tausayawa yar marainiyar dake cikin mu ba ai da abin baiyi dadi ba gare ku.
Don gidan nan kaf kan ku kuka sani baku son bare a cikin ku don haka ne nake tausayin yarinyar da zaman kaddara ya kawo ta cikin ku.
Daga Aliyu har umar din ba wanda yai magana sai data kare Aliyu ke fadin Amma haka mukaji abubuwa suna faruwa a gidan nan kan zaman yarinyar nan cikin ku.
Amma tace kasan ance idan baka mutu ba ba,a kare hallitan ka ba rabon dai yayan nan ne a cikin ku da maimuna ta haifa da mahaifin ku ya kashe ma yar nan nata uban.
Sai dai kishi ya haba iyayyen ku mata su gane hakan a zauna lafiya sun dauki tsanan duniya sun dora kan maimuna da yarta.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 22:48 - ??5惙5惙5?: YA HAYYU YA KAIYYUMU ALLAH KA KAWO MUNA DAUKI BA DON HALIN MU BA SAI DON DIBA GA MUMUNEI A CIKIN MU.
ALLAH KA GANI KA SANI DUNIYA TANA CIKIN WANI HALI NA NEMAN AGAJI A GARE KA YA ALLAH Jack TAUSAYA MUNA KA YAFE MUNA KURAKUREN MU, , , , , , ,


Shakuwa da so da kauna irin na tsakanin jika da kaka ne a tsakanin Amma da wanan bakon gidan daya zo daga baya.
Anan zai ci abincin sa ya zauna yana faman latse latsen wayan shi ko ya juya harshe da turancin yana hiran sa da matar shi a waya.
Don bai faye zama a wurin mahaifiyar tasa ba sai gurin tsohuwar kakan nasa dake nuna mai so da kauna fiye da kowa a cikin ahalin ta.

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login