Showing 282001 words to 285000 words out of 419207 words

Chapter 95 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1466

cikin sheshekan kuka.
Lokaci daya ya Umar ya rikice yana fadin fada min abinda ke damun ki yanzu ko muje asibiti ne dake ?
Ko gidan ne bakya so na rabaki dasu yau ganin ya rude har baisan abinda yake fadi ba yasa na dan rage sautin kukan nawa a hankali na bude baki da kyat nace yaya ka maidani gida don Allah wurin iyayyen mu.
Wani irin kallo yai min yace haba zarah baki tausayinane matsalan dake akwai a gida yafi wanan sau dubu a wurina yanzu kin sani.
Koda yake ba lalai bane ki san da hakan ke amma ina rokon ki zarah ki daure ki taimakeni ki kwantar da hankalin ki har zuwa lokacin da Allah zai saukeki lafiya ki haihu .
Izuwa lokacin komai zai kai karshe insha Allahu koba zaki iya min alkawarin komai ba na rokeki ki min wanan don Allah zarah for d sake of our urborn baby.
Na dago kai na kalleshi da sauri ni din yake kallo yana jiran amsan da zan bashi yana ganin na dago kai ya gyada min kai alaman in yarda da bukatan shi.
Ban bada amsa zancen ba don ba zan iya cewa eh ko a,a alokacin ba don irin yadda nake jin kaina.
Ganin nayi shiru ya mikar dani tsaye yana fadin muje daki in ja maki kafa ki ko zai maki dadi badon naso ba dole na bishi ya zaunar dani saman gadon tare da aje rigar jikin nasagefe daya.
Ya shiga matsa min kafan a hankali ina dan lumshe ido don jin dadin hakan da yake min din a lokacin.
Sai dai har lokacin ba wani magana don zuciyar kowan mu ba dadi a cikin sa shi yana ganin ya cutamin da yawa ga ciki ga rikicin daya taso tsakanin shi da merry.
Allah ya taimakeshi a kasan London suke ba a America ba don haka abin ya danzo mai da sauki ba kamar yadda merry din ta dauko zancen ba.
Don sam ta manta da yarjejeniyar su da sukayi kafin aure a rubuce dashi bata taba daukan wanan da muhinmanci ba don kamar da wasa sukayi shi.
Sai gashi wanan yar takardan ya rusa mata duk wani plain da alwashin ganin bayan shi tare da yan uwanshi a kan kara wasu hallita a cikin family din ta dashi.
Yayi barazanan bar mata dukiyan da take fadi akan zai bata takarda ta tafi har da yar tasu ya yafe mata.
Jin hakan har yan uwanta da iyayyen ta sun yarda da hakan daga baya merry din ta tubure masu akan sai tayi shawara da zuciyar ta ita kadai shinr aka kara basu lokaci.
Lokacin da suka fito cikin couth din dasshi da Yusuf ko kallon inda take baiyi ba ga Faith na kiran daddy daddy ya wuce ya barta a wurin zuciyar shi na masa kuna.
Kowa dake wurin saida yai mamakin hakan har yan uwanta sun fara fadin kinga irin abinda muke fada maki ga wa yan nan mutanen ke nan.
Basu da tabbas akan addinin su zasu iyayin komai lokaci guda ki kyaleshi don dole ya dawo ko don yar shi gareku.
Ku rufa min baki gaba dayan ku banson jin maganan kowa daga cikin ku idan rayuwan aurena ya samu matsala kune silan hakan gareni da yata.
Don kun hanani bin abinda mijina keso dani kun hana mu zauna lafiya dashi ga baki daya kuna ganin zamu iya juyashi a lokaci guda.
Omar ya wuce hakan da kuke tunani don yana tsaye ga addinin shi sosai hakama iyayyensa basu zauna a kansa ba.
Nan ta barsu ta shiga mota ds yarta tabi bayan shi saidai bata samay su ba taje gidan data san Yusuf a da baya gidan yanzu.
Ta juya zuwa gidan da suka samay ni gidan yana rufe kamar yadda hukuma tace a rufe shi har lokacin zama tayi tana karewa gidan kallo.
Tana mamakin yadda Omar ya zauna wata mace macen ma yarinya karama kamar fatema da ta sani a matsayin matar auren shi.
May zai samu gun wanan yarinyar da bai samu a wurin ta ba har ya iya bin umurnin iyayyen shi kanta.
Ido ta runtse sai hawaye taja mota kamar an tsikareta ta nufi gidan su ko yana can sai dai tun a haraban gidan ta gane baya gidan a lokacin.
Duk wanan haukan da merry keyi har yan uwanta basu kai ga gane akwai ciki a jikina ba har wanan lokacin ita dai zafin ta shine cewa da yayi ya a zaman matarshi nake nima.
Duk wanan abinda suke ciki ni ban sani ba don bai zauna yai min bayani yadda zan gane ba har in fahince shi.
Ni dai zan iya cewa wanan hutun baizo min da dadi ba din ga laluran ciki gana wanan halin da muke ciki ina zaune a gidan mutane a takure duk kokarin da sukeyi dani sai ban gani don ina ganin da hadin bakin su komai ke faruwa.
Ga Anty Ramla bata kasa dani ba kullun zata shigo wurina mu zauna muyi hira ta kawo min wanan ta kawo wancan haka dai take dawai niya dani a gidan.
Ni da kaina na ba kaina shawaran in sake jiki da ita wanan fushin ba zai fishini ba don ba zan iya fahintar komai a haka ba.
Ranan tana kitchen da safe tana aiki na fito na samay ta kitchen din ta juyo tana fadin mai ciki kin fito na danyi murmushi zuwa inda take ina kokarin karban wanke plate din da takeyi.
Tace rufa min asiri kada mai gidan ki ya samu kina wanan yace zan halaka mar mata kin ko san yana can amma kunnuwan sa na nan zarah.
Ban taba zaton akwai wata mace da zatazo tayi tasiri haka a zuciyar umar ba sai gashi har naga abinda yafi ma tunanena.
Zarah ki godewa Allah mijin ki yana son ki sosai da ba haka ba duk wanan barazanar da matarsa keyi akanki ne zarah.
Kin san umar ya zabi ya sadaukar da dukiyan shi akanta da komai nasa ya zauna dake ?
Nace ni kuma anty ?
Tace ke kuwa zarah ko cikin nan naki a jikin sa yake ya tsaya hakan yanzu haka duk wani shiri ya kamala duk da wanan halin na barazana ga hukuma da yake ciki amma ya gama shiri akan komai na haihuwan ki da ya dawo daga wanan tafiyan zaki sha mamakin shi kwarai
Wanan maganan da mukayi yasa naji kunyan kaina da kaina na rashin kwantar da hankalina garesu bayan nasan suna cikin barazana duk kuma a kaina.
Sai na samu kaina da jin kunyan kaina da kaina don haka na yanke a raina yana dawowa kawai in bashi hakkuri sai wata zuciya tace min akan may zan bashi hakkuri din ?


ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:29 - ??5惙5惙5?: BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM ALHAMDU,LILLAHI RABIL ALAMIN, , , , , ,


LITAFIN KUDINE GA MAI BUKATA TA KIRA 08036959257 DON TURA KUDI TA BANK KUMA ZA,A IYA TURA DARI UKU KACAL TA WANAN ACC DIN KAMAR HAKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KIBIYA KI KARANTA BA TARE DA DAUKAN NAUYI BA, , , , , ,


Na dade kwance a dakina ina tunanen hiran mu da anty Ramla da mukayi da safe.
A karshe dai na gano a kainane duk wani matsala yake tasowa a yanzu tsakanin yaya da matar shi.
Har yake kokarin sadaukar da kaddadarorin shi gareta don dai a zauna lafiya a tsakanin su.
To ni har wani mutunci ko halarci nayi mai da ya zabi hakan a kaina yanzu iya sani na ba wani so ko kauna irin na masoya a tsakanin mu.
Saidai yanzu abinda zance shine akwai shakuwa irin ta zama tare da mutuntawa irin na yan uwantaka da aurataya kawai a tsakanin mu.
Har dadin may yaji a gurina da zai sadaukar da komai a kaina har ina da wanan matsayin yanzu gare shi haka ban sani ba.
Idan hakane ya kamata in gyara halin zaman takewan dake tsakanina dashi a yanzu fiye da da can baya da nake daridari da zamana dashi.
Ta yaya zan gyara hakan kuma na tambayi kaina shawara da manya akace bai baci duk da nima macece yanzu saidai ilimina da wayo na ai baikai in gano hanyar mafita da kaina ba.
Mamu zan nema kowa da sauri nace no ba mamu ba sai wa na tambayi kaina a take amsa ya zo min anty farida ko anty Ramla.
To may zancewa anty Ramla din in naje gareta dan dama anty Farida akwai shakuwa sosai a tsakanin mu wanda har zan iya sakewa in nemo mafita a gurin ta.
Tunda dama har takan ban dan shawaran yadda zanyi in karkato kanshi zuwa gareni saida taga banda ra,ayin hakan ta daina bani shawara.
To amma ai da zan baro gida Amma tace min ni mace ce da kaina zan iya kama zuciyar mijina ba sai an koya min yadda zanyi hakan ba.
Sallaman da akayi daga kofan dakin ne ya katse min tunanena Anty Ramla ce dauke da dan madaidaicin ture a hannun ta ta shigo dakin .
Na amsa mata sallaman a hankali ina kokarin tashi zaune tare da kakaro murmushi a fuskana.
Tace ashe ba barci kikeyi ba, yau kinki fitowa waje ki dan sha iska yanzu maigidan ya dawo yake tambayan ki nace kina daki shine yace a dubaki ko lafiya kike.
Shine nace barin dan riko maki dan abinda mai ciki ke so ka zaki sha tana aje tire din a gefena take wanan magana.
Kawai dai anty na dan kwantane tace tana kaiwa zaune kodai maganan mu ta dazun ne ya daga maki hankali.
Dan dukar da kaina nayi kasa ina fadin bai daga min hankali ba anty sai dai maganan yasa na shiga wani halin tunane .
Da sauri tace tunanen may zahra ?
Sai danyi shiru sake tambaya tayi tana kallin fuskana tare da fadin wai kina mamakin abinda merry tayi ne ko may ?
Kin san ai ba tunane gare su ba dama kila da biyu ta aure shi ai da farko tana ganin zata iya juyashi zuwa akidar su.
Ko kuma wata kila don kwazon shi da himma data gani yasa ta leke may Allah kadai yasan niyar ta na auren shi tu farko.
Amma kowa yasan merry ai ba matar auren mijin ki ba abune dai kamar na rufa ido kin san halin maza abinda ka raina shi suke dauka da muhinmanci su a gare su.
Murmushi nayi tace mutum wanda keda mata haka kamarki danya shataf ga kyau ga kurciya in ba abin maza ba may zaiyi da wata merry arniya ma can.
Anty nace sai nayi shiru na kasa magana tace au kin dauka da wasa nake fadi nace ba hakabane anty sai na fara hawaye.
Subbahanallahi tace hankalin ta ya tashi a lokaci guda wanan maganan ai ban fadeshi don hankalin ki ya tashi ba zahra.
Kai na girgiza mata ta dafani tace ki bar kuka kin san kina cikin wani hali da ba,an son tashin hankali a gare ki yanzu.
Anty ba haka bane kawai dai ina kukane don zamana da yaya ban taba kyautata mashi ba a rayuwana a matsayina na matar shi kamar yadda shi yake kokarin kyautatawa rayuwana a kullun.
Kada kice hakan don shima maganan shi ke nan a kullun kan bai kyauta maki ba ya cuta maki a zaman ku ya ha,inci iyayyen kuna gida da suka bashi amanan ki ya daukoki daga gida ya kawo ki nan yana cuta maki.
Kaina girgiza tare da fadin ko daya anty yaya ya inganta min rayuwata wanda har abada zan amfana dashi koda bamu tare dashi.
Anty damuwana daya yanzu shine hanyar da zanbi in gyarawa yaya abubuwan da nayi masa wanda ni kaina nasan ban kyauta ba.
Dafa hannuna tayi tana murmushi kafin tace kai zahra akwai da wani magana tsakanin mijin da mata babu wanan abinda kike tunane yanzu.
Keda kanki a cikin hikima da basira irin namu na mata zaki gyara kurakuran ki na baya gare shi.
Ba sai kin furta mai kalman nadama da kike zaton shi zaki amfani dashi ba gareshi a, a zaki gyara mu,amulan ku ne fiye da da can farko ta hanyan yawan kulawa dashi.
Damuwan shi ya zama naki harma ki fishi kulawa ki tsaya iya inda ya tsayar dake gyara tsabatan gida da jiki har na yara ya kasance ba sai ya fada maki kiyi ba.
Kizama tankar mage gutin mijin ki kina dai ganin yadda muke a gida nan nida mijina da yaran mu.
Kifishi son yan uwan shi na jini koda ya nuna baison abinda suka zo mai da bukata a wurin shi ke ki nuna mai idan bai basu ba wazai ba.
Lokacin cin abinci tankar yadda kika san zaki ciyar da yaro na goye abinci haka ya kamata ki ciyar da mijin ki kina kula kina tarairayan abin ki.
Idan yai tafiya ko ya fita office kira na zuwa yana dawowa kina masa barka da aiki ko barka da hanya.
Ke idan kin rike wanan kawai ina mai maki rantsuwa ga Allah babu wata mace da zata zo ta fiki gareshi koda kuwa tazo da nata sallon nakin nan dai daya saba dashi har lokacin yana da tasiri a zuciyar shi.
Ina fada maki ba merry ba koda Allah yasa zai auro maki ba hausa nan gaba yar uwarki ba zata fiki komai ba gareshi.
Ajiyan zuciya na sauke ta mike tana fadin bari in barki haka nasan yanzu daddy Amar ya fito daga wanka zanje in dubashi.
Ta fice ta barni da tunane ashe abinda mamu keyi kenan wanda su hjy basu gane ba suke ganin ta sace zuciyar mijin su ga baki daya.
Don mamu idan tana da girki ba mu gane komai a gidan nan ranan bata da lokacin kowa haka bamu gane kanta sai lokacin da ta fita girki.
Tsoho ma ya ji dadin kulawa irin haka may zai hana yaro matashi dan shekara talatin da wani abu son haka kamar yaya ?
Ke nan ni nayi sakaci don rashin mai gyara min ko lurar dani hakan shine daidai gaskiya da anty Farida tace min in zama karuwan gida naji haushin ta a lokacin.
Akan may zatace in koma karuwa do kawai mijina ya soni kada ya soni in sai nayi kwarkwasa da hilla zai soni.
Ashe gaskiya tayi fushi dani wurin ganin wautana kan abinda take lurar dani din ban dauka ba Anty farida tana daga cikin masu kaunana na gaskiya ke nan.
Haka na kwana cikin tunane da damuwa washegari anty Ramla ta same ni a daki kwance tace yau dai zamu gyaran kai da jiki dake don yau sati biyu da tafiyan mijin ki nasan yanzu bai nisa da dawowa kasan nan.
Murmushi nayi kawai don jin abinda ta fada din don haka kamar yadda tace nima din ina so dama ko banza ban gane ma jikin nawa ba lokacin don ga nauyin ciki ga shi na koma gajal dani.
Gyara akai min sosai don shagon kitso da kumshi irin namu na Africa ta kaimu ance wanda ya fika dadewa yafika sanin kan gari.
Don ban taba tunanen akwai irin wanan wurin a kasan nan ba sai gashi kamar yadda miji da matan dana taba haduwa dasu ranan suka kaini wurin cin abinci ranan haka naga wurin.
Saidai abinda ya ban mamaki bai wuce irin kallon mamakin da mai shagon take bina dashi ba don tazo zata shige office din ta ana gaida ita tana wani shan kamshi .
Harta dan shige sai kuma ta juyo don hangoni a jikin mirrow din dake wurin datayi ta dawo baya.
Yaren su na yan libiya ta fara min ban san dani take yare ba sai da wace ke min gyara tace dake ake magana cikin harshen turanci na dago kai ina kallon ta.
Ta kara min yaren taji ban amsa mata ba sai ta juya da harshen turanci tana tambayana bana jin yaren su na arab ne ?
Na girgiza mata kai kawai ta dan tsaya jim tana kallona na dan lokaci kafin tayi yare da mai min kitson ta shige office din ta.
Ban kulata ba ban kuma tambayi mai kitson abinda tace ba sai da aka gama min aka fara wanke kafa da akaifa a hankali.
Saida aka gama komai naga matar ta shiga office dinta sai gasu sun fito tare da mai shagon wanan karon tana fara,a a fuskanta.
Take fadin tana son yin photo dani don ina kama da wata yar uwanta sosai muyi photo kala kala da ita a gurin kafin mu tafi.
Bata barmu mun tafi ba saida ta karbi layin wayana ni dai ina mamakin ta a raina bamu kara bi ta kanta ba muka koma gida bayan mun biya munyi dan sayayya abin bukatan mu.
A gajiye

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login