Showing 156001 words to 159000 words out of 419207 words

Chapter 53 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1511

uwayen da yaro zai min son ranshi ba zan gama wahala daku ba yanzu hutu yazo kace zaka manta damu don ka samu wata mace.
Shiru yayi yana sauraren yadda mahaifiyar nasa ke kwasan fada dashi tace watau abinda nake guje maka ga auren yar wurin maimuna shine kuma zaka gwada min ga wanan mai guntun bujen naka ?
To idan ma dan abinda kake turo muna ne ta hana ka sani yanzu ba kai kadai bane mai bani don bakai daya na haifa ba.
Wani irin yaji a ranshi ba dadi hakan yasa ya shiga bata hakkuri yana kokarin kare merry akan ba laifinta bane sai dai uwar bata bashi daman korafi ba.
Suna gama waya ya cika mata account dinta da kudi masu yawa haka yasa ta daina jin zafin shi da take ji da farko.
Ranan ma ya kira Amma sun dan taba hira take tambayan shi ko lafiya taji shi shiru haka kwana biyu ya dinga tuna gida da iyayyen shi shiru haka sai hankalin mutane ya tashi ai.
Yace Amma za a gyara da yardan Allah komai zaizo da sauki insha Allahu sukai sallama.
Daga wanan karon kuma saida ya dauki lokaci bai kira wani ba duk dai kawu yana kan addua ga yayan nasa har lokacin.

Mun samu mun kammala karatun mu lafiya yanzu gidan wa yanda suka rage sai kanana mai dan girman cikin su itace yar gurin hjy maryam kanwar ilkilima a cikin masu zuwa school.
Har lokacin ba wani jittuwa a tsakanin mu sai dai ba yawa fada tunda bamu shan innuwa daya dasu balle mu hade ayi fada ko islamiyan da muke zuwa kowa tasa yake zuwa.
Mun gama da kamar wata daya ranan kawu ya shigo wurin Amma ina falon ya kalle ni yace Fatima tunda an kare karatu yanzu sai ki shirya muje bauchi ko ki gaida su.
Wani dadi naji a raina har bansan lokacin dana saki ihun murna ba suka kwashe da da dariya shida Amma.
Nan na bar kawu wurin Amma na nufi part din mu ina murna na samu mamu ina fada mata kawu yace in shirya zai kaini bauchi wurin su manjo in dubasu.
Tace yanzu yake fada min saidai yace ai ba zaki dade can ba na bata rai tare da fadin ni dai a barni can inyi koda wata uku ne mamu wallahi ina kewan su sosai.
Tace da wuya saidai ai tsakanin ki da kawun ki ne kila idan kin lalasheshi zai yarda.
Don zumudi tun ranan na fars shiri ina daukan kayan da zanyi tafiya dasu ina jefawa a yar jekkana da wanda zanyi kyauta dashi idan naje can.
Har kwana biyu banji kawu yace min komai ba nikuma ban fasa shirina ba har lokacin ba karamin kaya na kwasa ba , wai duk kyauta zanyi dasu a can idan naje.
Da dare ranan bayan kamar kwana uku da maganan ran daren jumma,a sai ga kawu ya shigo yana fadin mu shirya da safe zamu wuce.
Haba murna wurina ba a magana na matsu gari ya waye Ingani a garin misau gaban manjo da Atika inga yaya Atika ta koma itama.
Da safe muka fito a cikkn shirin mu wanan karon duk yaran zamuyi tafiyan dasu wanda hakan yai min dadi sosai a raina.
Mun sallami kowa a gidan don sai da mamu ta turani nayi sallama dasu ba don naso ba ssi da muka fito shiga motane naga ashe ba mu kadai zamuyi tafiyan ba har da wasu abokan kawu sai dai mu tamu motar dabance.
Sai na dauka kila dama wani abu kawu zaije yi can bauchi din yaga ta dace ya kaini gida.
Su Aisha har wurin motan mu suke sun min rakiya sai da muka tashi suka bar gurin sai kuma naji ba dadi a raina.
Sako mai yawa Amma ta bayar akaiwa manjo ina ta godiya kamar nice manjo din da akaba sakon.
Mun isa musalin daya da wani abu na raba wai dukda mun daka sakko da safe muka taso amma sai kusan azahar muka isa garin.
Gida yana nan kamar yadda na barshi saima kara lalacewan da yayi lokacin a idona ko don na saba da gidan kawune yanzu nake ganin hakan.
Wani dadi naji a raina na kalli gidan su Atika shima yana nan kamar yadda na barshi bayan motar ta tsaya ne na fito da zumudi mamu ta kalleni tace ki natsu mana kin san yanzu kowa idon shi zai koma kanki ne.
Hakan yasani na gyara da kyau duk da hakan banyi yunkurin yin wani sallo ba can sai dai ban san komai nawa ya canza ba a yanzu don su ganin gaba daya na sake masu ne don gani ga yayan Atika mai koramu karatu bai gane ni ba nima ban masa magana ba.
Na hango wasu gungun maza matasa zaune a darbejiyan dake duban tsohon shagon isah mai shegwo har yanzu shagon na gurin sai dai ba kamar da can baya ba da yake cike har baki muna zuwa sayen abu a gurin shi kusan duk unguwan anan ake sayen abu.
Yanzu ko shagon ya watse ba wanan kayan irin na dacan baya a shagon don har cikin shagon zaka iya hangowa daga inda muke .
Mazan ne naga sun zubo muna ido suna magana ban tsaya bin ta nasu ba na nufi hanyar shiga gidan.
Da sallama na shiga gidan mama saude ne zaune tsakar gida da daura gaba tana tsifan kai.
Jin sallaman mu ne yasa ta dago kai tana kallin mu gurun ta na nufa ina rike da yan kanne su biyu fauziya tana rike da mamu suna bin gidan da kallon mamaki.
Nace mama ina wuni tace wa nake gani nan kamar fatu nace nice mama ina murmushi a fuskana.
Tace ku fito yau ga fatu a gidan nan tana fadi da yar fara,anta sai gasu sunyo waje ruuuu daga cikin tsohon falo namu.
Fati ce nan fatin manjo fa sai ga umma ta leko itama da daura gaba a jikin ta tana fadin fatin manjo ina kuma ta fito nan ko tayi halin natane can suma sun koro, , , ,
Ganin yanayi ga kuma mamu a bayana yasa ta katse maganan datayi niyar fada gare ni ta washe baki tana fadin ashe tare kuke tafe da maimu.
Itama na gaida ita kamar yadda na gaida mama saude din da farko sai fadi mama saude take ina zasu shiga ne yaya ?
Mun barsu a waje tsaye mama tace a, a dakin tsohuwa zasu kin sani nan na juya na nufi dakin kwanon manjo da nai rayuwa a ciki a baya ya kara lalacewa har an tare shi da su leda da ragga dai sauran tarkace nasan don ruwan sama ne.
Manjo na zaune a sama tsumakara wai katifa sai ganina tayi kamar a mafalki ina fadin manjona na fada saman jikin ta.
Salati ta fara sai kuma ta fashe da kuka tace wallahi tunanen ki nake a raina yar nan nace manjo ai gani nazo tunane ya kare.
Sallaman mamu kofan dakin ya katse muna tace ashe tare kuke da uwar taki sannun ku da zuwa tana kokarin tashi na hanata don rabin jikina a jikinta yake.
Tace daga jn tashi in gyarawa uwarki wurin zama mana nace ki zauna manjo in gyara mata tace tsintsiya yana daga waje ki dauko.
Dakin ne ba mai gyaraw sai ni idan na dan ji daman jikin nakan dan kora in samu wurin sallah.
Na fito daukan tsintsiya naji yaya hamshin ya shigo yana fadin wai wa nake gani kamar fatin manjo gidan nan ya nade kafan wandon shi daya da ganin shigar shi kasan har yanzu sai a hankali.
Nayi murmushi ina fadin sannu da zuwa yaya hashimu sake baki yayi yana kallon ikon Allah kafin yace wai da gaske kece fati kika koma haka ?
Nayi far da udanuwana nace nice yaya mun samay ku lafiya ?
Sai mamakin canzawa yake ya kasa amsa min niko banga abinda sukewa mamaki a jikjna ba yace fati kin koma kamar wata baturiya haka dake ?.
Dan dariya nayi ina fadin kai yaya hashim kuma har da zolaya yace ba zolaya ko daya kin canza fati kin koma yar birni dake kamar bake bace fatin manjon dana sani.
Muryan manjo ne take fadin wai ina kike ne kin bar mutane a tsaye nace gani nan na barshi na wuce tsaye a gurin yana mamaki na.
Suma can dai ciki gulman sukeyi kan canzawan danayi cikin shekara biyu da rabin danayi rabona dasu.
Saida na share dakin na fito da shera nake fafin ai ina su anty kubura ne ban gansu iba tambayan mama saude tace sadiya tana ciki kubura ina jin ta fita.
Bayan an gama gaisawa Mamu tace ai mata magana da baffa don zasu komane su yau aka tura a kira baffa din yazo.
Bai dade da zuwa ba suka fice wajen harda mamu nan suka barni na fara gyaran abinda zan iya a dakin na kusa karasawa ne sai jin murya Atika nayi tana fafin ina Fatin take ne ?
Na yarda tsintsiyan hannu na na fito muka rungumay juna da ita a wurin mun dan jima muna hira ta tayani gyara dakin kafin su shigo sai fadi Atika keyi kin ganki kuwa fati kin canza fa ga baki daya wallahi ni dai murmushi kawai nake mata ina kallonta.
Da gani yanzu duniya ta dan basu baya ganin yanayinta kawai yasa na gane hakan koko din girshi ta fito ne ban sani ba.
An dauki lokaci a wajan don har na fara tsarguwa sai ga mamu ta shigo yara suna biye da kayana a bayan su tana fadin kije kuyi sallama da kawun ki kafin mu fito.
Atika ce ta rakani wurin shi na samu wuri na tsugun na yace Fatima kinga gida kin shige kin manta da mutane ko ?
Nayi murmushi ina fadin kawu mamu tace yanzu zaku tafi yace eh kinsan hanyan sai a hankali gara mu bishi da wuri ido na ganin ido zaifi tunda mun ga baban naki.
Nan dai yadan ja min kunne akan in natsu kwana biyar zanyi driver zaizo ya dauke ni mu koma nace kamar in kuka don ba haka naso ba ni tunda na gama karatu ai da a barni na kwana biyu nace a raina.
Hannu yasa a aljihun shi ya ciro kudi masu yawa ya bani yace ki rike wanan na karba ina godiya yacewa Atika itama ga nata ya sake kirgo wani yace i bawa mutanen gidan idan na shiga .
Muna wurin sai ga su mamu sun fito har da yan gida kawu din da sukai mata rakiya don ta jikasu da alheri dumus.
Nabar gurin kawu Atika tana biye dani na kwanta a kafadan mamu ina fadin mamu har nafara ji kewan ku fa.
Tace yau ga tsiya ni dagani mu wuce zaki ga sako acikkn hand bag dinki na saka maki kidai kula da kanki don Allah.
Uwa dadi kamar ince na fasa tsayin kuma nake ji yanzu a raina na nuna mata kudin da kawu ya bani tace kuma yabada wani fa da farko kuma a baki nace to ko in baki wanan ki tafi dasune mamu ?
Tace bar abiki yadda naga gidan nan sai a hankali ki tabbatar da kuna cin abinci mai kysu kada ku zauna da yunwa nace to mamu ina shafa kan samir daya makale mun nikuma ina jikin mamu kamar zan koma ciki.
Sai muka ba mutanen dake kallin sha,awa yadda muke abu kamar wasu ya da kanwacan haka sai ina kallo suka tafi ina daga masu hannu.
Nace mu shiga in gyara kayana kafin mu shiga wurin umma nasa ba zan fito maza ba idan naga umma yau.
Mun shiga na gyara wuri komai tsab na fito tare da Atika da kallona bai isheta ba har lokacin don har ga Allah ba Atika kawai ke mun kallon kurulla ba kowa na gidan ne.
Haka muka fito zuwa gida su Atika ban fita ba saboda sabawan da nayi yanzu sai danaje na fadawa su mama saude zan shiga gidan su Atika in gaida umma.
Bayan na wuce ne aka sa topic dina a gidan mama saude tace ai na fada maki ba dawo da ita sukayi ba baki ganin yadda iyayyen keyi da ita kamar zasu mai data ciki.
Koma dai maynene ai dai bata canza uba in kuma tasa tsiya in hana malam ya barta ta koma muga tsiya.
A gidan su Atika na shiga da murna ina kiran umma tace har nayi fushi tun dazun muna nan muna saka idon ganin ki sai ji mukayi shiru.
Na rungumay umma ina fadin umma na tsaya sallaman su mamu ne amma kina raina wallahi ranan dai mun sha hira kamar babu gobe sai dare na koma gida bayan yayan su Atika ya sawo wa mamu nama mai yawa da abin sha mai zafi nakai mata na samu ta idar da sallah har ta fara barcin wahala ba abinci.

Bayan su kawu sun dawo gida da washe gari da safe yayi waya da yaran sa maza a kan komai sukeyi su bari su hadu gida ranan talata mai zuwa.
Allah ya taimaka daga cikin su ba wanda ya fadawa hjy su don su a zaton su tasan ko may yasa yake nema su din .
Dan dama Aliyu da suna waya yake tambayan ta baba lafiya yake kuwa tace may ka gani yana nan lafiyan shi kalau,
Daga haka ya basar sai bai dauki abinda muhinmanci ba ranan sai ga Aliyu da habibbi sun iso da rana yan part din su sukai ta murnan zuwan su.
Sun shiga gurin Amma sun gaisa sai dai har yanzu babu halin shiga sauran part din gidan don basu saba ba ma dasu din.
Sai cikin dare umar ya sauka garin don haka gida shi ya nufa sai da safe ya shigo gidan nasu a natse.
Yana saye cikin bakar suith ya kara haske sosai ya goge don yanzu kusan shekara da rabi rabon shi da kasan.
Aisha ce ta fara ganin shi ta fito daga gurin mamu sai ganin mutum tayi tace yaya umar sannu da zuwa ya amsa mata a dakile kamar wanda bai gane ta ba.
Har lokacin yana jin ba dadi a ranshi don zuwan dole dole yayi ya shigo ne da niyar kwana biyu kawai ya koma don akwai aiki mai tarin yawa a gaban shi sosai.
Aisha da kamar dole har ya wuce ya nufi sashen mahaifiyar shi tace ya su anty merry da ummi karama ya amsa ba tare daya juyo ba da suna lafiya.
Suna zaune falon Amma sai gata da murna tana fadin mutanen nan abinsu kamar hadin baki jiya su yaya habbib dunzo yau kuma ga yaya umar yashigo shima.
Cikin fara, a Amma tace ikon Allah duk gaba dayan su sunzo a lokaci daya.
Allah yasa lafiya dai don uwarsu bata rasa abin tsegumi a gaban ta ko yaushe wata kila kuma wani abin suka zoyi sai dai ni ba????? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ?  kin cikina da sadauki zuwa ds wanan kafiran haka tsirara a gidan nan.
Dariya suka kwashe dashi suna fadin kai ji amma fa irin ku ne yan sa ido kan mutane.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:11 - ??5惙5惙5?: BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHEEM, , , ,


A can garin misau kuma bayan mun dawo wurin manjo na tayar da ita tare da gabatar mata da abinda aka sawo mata yar tsohuwar ta mike jikinta har rawa yake da ganin kayan dake zube a gaban ta.
Gabana ta sai da naga taci sosai sai ta dago kai tana fadin nifa nace banjin yunwa sosai don naci abinci gidan su Atika.
Tace ba zai yuyuba A ruwa yau naji kunya a gidan nan yadda iyayyen ki suka zo ko ruwan gidan nan basu sha ba haka suka juya suka tafi.
Sai ta fashe da kuka tana fadin kai duniya abin tsoro ne A ruwa lokacin da kakanku yana raye muna zaune ne garin ikko dashi.
Sai idan munzo ganin gida muke zuwa nan nahiyar a lokacin mulkin shagari kakan mai kudine sosai yana kasuwanci bayan aikin gwaunati da yakeyi.
Idan zamu zo zaki ce wani sarki ne zai sauka a garin don yawan jamma,a motoci ko tun a wacan lokacin sai mun shigo da guda uku garin nan daya yana dauke damu iyalin shi dayan kuma na makaraban shi sai ta kaya da yake rabawa itace babban mota.
Yan uwa na nisa dana kusa haka zasu dinga tururuwa a gidan mu ana zuwa gaida mu nidashi muna raba alheri gare su.
Saidai kaya mutuwa bata barin wani don wani yaji dadi tun lokacin da kasa ya rufe idon kakan ku sanadiyan hatsarin mota kamar yadda mahaifin ki shima ta wanan sanadin ya tafi haka ma kakan ku don sai gawan su kawai aka kawo muna a gida.
Kuka ne yaci karfin ta ta kasa magana juice din dake gaban ta na dauka na tsiyaya mata a kofi

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login