Showing 318001 words to 321000 words out of 419207 words

Chapter 107 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1408

ba harda wa yanda suka girmay shi lokacin.
Shiya banyi mamaki ba lokacin da yazo gidan nan da matarsa merry don nasan irin nacin da mata ke gwada mai ta gwada mashi har ya yarda da ita.
Ni dai abinda nakewa gudu da tsoro shine asiri tun dawowan hjy sabuwa garin nan da zama gaba daya hjy ta fada harkan bokaye da malamai inma da tanayi dai a boye take abinta amma yanzu a filin Allah take lamarin ta.
Saidai ni abinta bai faye damuna ba tunda ina bin dare ina fadawa Allah matsalolina ya kuma amsa min na gani.
Mamu nidai idan abin zai zama fitina gara in tsira da rayuwana kowa ya kama gaban sa .
Da sauri tace kina ko da hankali sayadi mai yasa kikaji manya na fadi anyi hakkuri da yanayin aure mai dadi ko mara dadi duk a kan yarane fa.
Kan yaro sai ke mace ki danne komai naki kiyu hakkuri ki barwa Allah al,amarin sa komai da zai faru da bawa Allah yasani.
Don yara wasu mata ke zaune gidan mazajen su suna cin boni gun kishiya da miji don sun kwamace da wata ta ba yaron su tarbiyan banza garasu suba abinsu mafi ingancin tarbiya tun zamaninda da ake da sauran imani balle yanzu da imani yai karanci ga zukatan mutane.
Idan kinyi hakkuri komai yazo mai wucene a gurin Allah sai a koma kamar ba,ayi ba daga baya.
Mamu amma aini nayi karanta da shanye irin wanan abinda kike lissafo min na fada ina kallon fuskanta.
Tace kaiyya sayadi hakkuri ga yaro da babba aka san shi balle ban sa a raina cewa don mijiki ya auri yar wurin hjy sabuwa zai juya maki baya yadda kike tsamanin zaiyi ba duk dako itama yar uwasa ce kuma iyayyen su zasu tsaya sosai a kan auren na sani.
Kedai ki kwantar da hankalin ki Allah ya saukeki lafiya ayi a zauna lafiya ba shike nan ballema shida baida ra,ayin aje mata a guri daya irin namun nan may zai damu mutum .
Ba zama wuri daya ke sakawa mata kyashi da hassadan junan su ba haka abu yakici yaki karewa ko yaushe.
Ranan mun dade da mahaifiyata muna hiran abu daya saida likacin sallah yayi muka tashi mukai sallah da cin abinci na shiga wurin Amma.
Washe gari na tashi da niyar zuwa gidan Anty salma da tazo tana min korafin naki zuwa wurin ta dama ina da niyar zuwa wanan matsalan yazo muna na dawo gida.
Sai ranan nayi waya da drivern gidan yaya akan ya kawo min motana zan fita dashi kwalliya sosai muka sha dagani har sultana fauziya da murja.
Rigan dake jikina basai an fadawa mutum an kashe naira a gurin sayen shi ba dayai wani tafiya Dubai ya sawo min shi ga sultana da ta kwaso farin mu kamar yar turawa kwaliyan dan riga pink da wando dogo har ribon da ta kalman kafatan adon pink ne da fari a jikin ta.
Daidai mun fito ke nan daga wurin Amma da muka shiga sallama aka turo get din cikin gida za,a shigo.
Ban damu da kula matan da nagani suna shigowa gidan ba a lokacin don hankalina yana ga wayan da nake da Aisha muna dariya ina tafiya salo salo kamar da kamar da gangan nakeyi banko san inayi ba.
Wani irin kallon kishi da tsana suke aika min daga inda suke suna kallon yanayin shiga na a cikin rudewa.
A hankali tacewa uwar wanan kuma a gidan nan take ne tana magana kasa kasa kamar rada ga uwar.
Wata kila bakuwa sukayi wanan motar da muka gani waje muna magana kai amma dai wanan ta hadu wallahi.
Taji ina ace haka ta samu haduwa koda rabin nawa ne aida tasan dole mijin da take muradi ya so ta.
Ga mace kamar balaraba sak da ganin ta yar wani ne ko matar wani a kasan nan irin yaran nan ne da suka taso a cikin hutu kinga fatarta wani irin luf luf dashi kamar wace bata shiga rana dan cikin jikina daya turo ta kalla tace ciki dai yanawa wasu mata kyau wallahi.
Ita kadai take zancen ta a zuciyan ta sai taji duk irin kwalliyan data fito dashi suna yauki daga ita har uwarta duk sun muzanta a gurin.
Ganin sun danzo kusa damu yasa na dan barwayan ina fadin sannun ku da zuwa ina wunin ku.
Mun saba da gaisuwa irin na tura da zaka hadu da mutum baka san shi ba ku gaisa.
Tana mamakin jin muryana daya dan girgizata sosai bamu kara kulasu ba mama hadiye ne ta fito tana fadin Fatima ku biya gidan saratu don Allah ku gaisheta na amsa da to mama da cewa gidan kanwar mama hadiye din.
Bari na dan riko abin da zamu kai mata nace ina sake hannun sultana zuwa part din mu da sauri.
Ba yar ba har uwan saids gaban ta ya fadi uwar tace kardai nace wanan ce matar yaron nan dama ?
Da wanan mamakin suka shiga wurin hjy da sukazo dubawa don tun maganan su Nafisa ta kwanta ciyo.
Shine suka zo dubata don yanzu zumuncin su ya taso sosai a tsakanin su idan ba a hadu ba ana makale da waya.
Hjy dake zaune tana ta dago tana dan murmushi tana masu sannu da zuwa.
Suka amsa da um kedai hjy muna shigowa muka hade da wata mace data dauke muna hankali yanzu gidan nan.
Hjy tace a gidan nan kuka ganta Nafisa dake gefen ta zaune tunda tayi masu sannu da zuwa ta kawar da kai gare su tace Fatima ne fa suke fadi yanzu da zan shigo na gansu zasu fita ita da murja.
Na,ima tace na shiga uku itace fatiman matar Umar dama anya kuwa kuwa Umar zai soni yana da wanan matar haka ?
Da sauri hjy jummai tace inkiji soma ai daya ke nan ai sai yayi maki so da kaunar da bai taba yiwa wata mace irin shi ba indai ina raye.
Mu zuba dani dasu zaki sha mamaki ke dai kawai mu samu yanzu mu shawo kanshi a samu ayi wana abin gida bai koshi balle in barwa daji ganima .
Iya gudun shi nake kallon nan gaba bausan sanda zai kawo kafan shiba gidan nan da kansa yana rokon gafaran mu.
Hjy sabuwa tayi dariya tace tun yaushe wasa yake damu ai don dai kawai ma ya zama namu ana daga masa kafa.
Mikewa Nafisa tayi ta bar falon zuwa daki waya ta dauko tana tsegun tawa salma zancen da sukeyi a falo tana jan tsuki.

Muna fita gidan muka shiga mota nida murjane a gaba fauziya da yarta suna baya zaune suna dan hiran yara.
Wai fatima kin san wa yan nan da suka shigo gida yanzu nace wasu mutane ke nan don ni har na manta dasu a raina.
Tace wa yanda kika gaiyar mana da zamu fito nace OK matan nan ai ina ga wurin hjyn su yaya suka zo ko ?
Itace fa Na,iman da ake fadi yaya zai aura din ta fada tana kallona wanan din da suka shigo yanzu fa murja na tambaya ina kallon ta.
Ita face da uwarta ina fada maki kaina girgiza ina runtse idona duk da ban masu kallon kyauba amma na danyi tunanen kamanin su.
Ban taba zaton zanji abinda naji a raina ba lokacin da sauri nace innalillahi ina kallon hanya.
Suma bakiga irin kallon kurullan da suke maki bane da suka shigo ba lokacin kila suma sun gane ki ne suke kallon ki.
Suka sani na bata amsa ina kallon ta tare da fadin sai fa kin mun kwatance don ban iya kai kaina gidan yanzu gaskiya.
Tana mun kwatance muka isa gidan tun a waje na gane salma na cikin wani yanayi don har yanzu gidan na a yadda na san shi a baya ba,a gyara komai ba daga gidan.
Nan dai muka shiga bayan nasa Fauziya ta riko abinda muka kawo mata sallama mukayi daga kofan shiga tana ciki ta amsa muna.
Tana fito da gani girki takeyi a lokacin mamakin ganin mu tayi wanan lokacin yau a gidan nan nace gidan ki kuwa yau dai gamun zo falo ta kaimu tana kame kame aiki yai yawa bata samu ko gyaran falon ba yau.
Muka zauna muna gaisai tana tambaya mu mutanen gida ranan mun sha hira tanayi tana duban girki har yayi ta zubo muna mukaci tare bayan azahar sai ga maigidan ya shigo cin abinci dama tace muna kila ya dawo don ba kullun yakan samu dawowa gida ba.
Allah ya taimaka sai gashi ranan ya dawo tundaga waje yake kallon bakon motar daya gani kofan gida haka ya daure ya shigo gida da sallama tare da zullumin wanda zai sama a gidan.
Kasa nake zaune na sake jikina muna hira dan kwalina yana saman kaina na rufa ya shigo da sallama.
Muka karba tare da mai sannu da dawowa da mamaki yake kallona tare da fadin wa nake gani haka kamar Fatima gidan yau nace nice yaya.
Duk cikin mu ni kadai ke masa wanan karan kiran shi da yaya tun farko kuma yana jin dadin hakan har cikin ran shi.
Gaisawa ya zauna mukayi sosai yana tambayana yara nace suna lafiya baban su ya tafi dasu suna gurin shi.
Kefa may kikeyi a garin nan har yanzu sai nayi mai dariya kawai anty salma tace kamanta na fadama tana gida yace amma na dauka laluran cikine ya tsayar da ita aiko ?
Shiru yayi na dan lokaci kafin ya mike yana umurtan ta takai mai abunci a daki tunda muna gurin .
Nan ta barmu ta shiga hidiman mijin ta muna dan hira da murja sama sama a gurin na lura da akwai biyayyan aure sosai da salma take mai don yana shigowa gaba daya sai naga ta daburce min .
Sai da ya gama na mike ina tambayan ta ya kare cin abinci ne ina son magana dashi taje ta fada mai yace in shigo tashi yayi saman kujeran da yake zaune ya koma bakin gado ya zauna.
Na shigo da sallama muka kara gaisawa yace banji dadin jin kina gida haka zaune kuma ban sani ba don yanzu na rage shiga gidan tun bayan auren mu da salma bana shiga kamar yadda nake zuwa dacan.
Nace yaya dole na zauna gida abubuwa sunki canzawa ta bangaren hjyn su salma har yanzu dani nan dai na kora mai dan bayanai da suka faru.
Yace ni abin yana ban mamaki wanan hali na hajiya har kullun ita bata amfani da girman ta da shekarun ta.
Yanzu shi Alh dayace ki zauna gida yana ganin hakan shine mafita ga zancen ku ?
Nace yaya ni hakan yafi mun sauki gara kowa ya zauna a matsayin shi zai fi abinda ke daga min hankali shine kullun dan zance kadan tayiwa mamu gori da zagi da cin mutunci.
Zuciyata ta fara gajiya da wanan abin yaya don ba zan yarda ina ganin mahaifiya ta ko yaushe a cikin tashin hankali yaya meye laifin mamu a cikin barin ta da mahaifiyar ta tayi ?
Yace ni yanzu ba wanan ba don in da sabo ai hjyn ki ta saba da halin wanan matar hakana zaman ki gida shine bangane nufin Alh ba.
Nace yaya koma dai maye ni ba zan koma gidan yaya Umar ba taje tayi mashi auren gatan da tace zatayi mai din kowa ya gani ba shike nan ba.
Yanzun gida nake son zuwa kwanan nan tunda nazo banje gida na dubasu ba idan na dawo zan fara maganan aiki tunda ina da takarduna zaman nan ba zai fitar dani nan gaba.
Yace a,a Fatima kada kiyi haka ki bari a zauna ai magana zan tuntubi Alh da zancen nasan ba zai boye min komai ba daga ciki in yaso sai mu san abinyi daga baya.
Yaya ba zanso kai mai magana ba don ni abin yanzu ya fita mun a rai ba zan iya daukan cin fuskan da akewa mahaifiyata ba yaya a kaina.
Fatima shi aure da kike gani ta wuce nan ya fada yana murmushi shi umar din ai badashi kike da matsala ba yanzu don mahaifiyar shi sai kice kin hakkura da mijin ki da diyan ki ga baki daya.
Zamu zauna da Alh duk abinda ake ciki zan kira hjy muyi magana itama hakkurin data saba shi zatayi.
Kin gani nan sai da na nuna mata nima na iya ta barmu muka zauna lafiya da salma gidan nan yazu ta fita batun yar nata wai ta yafe min ita.
Yakai inda nake sin zuwa nace kai hjy ho dama yaya zanso muyi magana sai ga sultana ta shigo tana kuka a dakin tana nema na.
Saida na lalashe ta tayi shiru yace wayan can yaran su ance mazane kika haifa da farko ko ?
Nace mazane yaya kafin ince dama zancen Anty salma nake son zamuyi dakai idan mun samu lokaci don naga yanzu kamar kana saurine ?
Yace wani abinne tace nayi kuma haba yaya me zakai ma anty salma harta kawo karanta gareni kawai dai ganin dacewan abin yasa nace tunda dai ni zaman kanwarka nake a gare ka zan ma magana ko za a samar mata aiki ko wani sana,a mai karfi wanda zata rike kanta kamar yadda mata sukeyi a zaman nin ba sai mace ta dogara ga abin namiji ba .
Dan murmushi yayi kafin yace Fatima nasan da wana gata nan ki tambaye ta kiji nidai ga tsarina ba zan yarda da aikin gwaunati ba.
Ko karatun da tayi mijin ki shi yazo ya rokeni alfarma naji nauyin shi na yarda taje karatu.
Salma bata da wayau fatima da kike ganin ta ga kazanta da ace ni mai ra,ayi tara matane da yanzu na dade da kara aure don halin salma.
Nace abin ko bai mata kyau ba nayi mata magana dazun da muka shigo kuma ta dauku alkawarin zata gyara.
Yanzu dai naji yaya ba zaka barta tayi aiki ba zaka barta tayi sana,a mai kwari koda a cikin gidane don ta huta zaman banza .
Da alama zancena yana bashi dariya don murmushin da yake sakewa a fuskan shi idan nayi yasa na gane hakan.
Fatima yanzu shahon mu ba kamar da bane can baya kuma ni kin san a karskashin wani nake har yanzu dukiyan mutanene amana a hannu na na fada mata tayi hakkuri har Allah ya bani wani dama in samu dan kudi in bata tasamu abin yi dashi.
Na sani yaya ba wai ina nufin kai kaimata a yanzu nasan yanayin da kasan nan ke ciki da halin da kuke ciki dan uwan ta dai ne zai mata idan ka yarda.
Fatima kin san halin hjyn su sarai yin wani abu ga yarta yana iya jawo muna matsala daga baya mussanman ma idan abin ya fito daga bangaren su.
Nace yaya kada ka dubi wanan yanzu idan ana dubun halin hjy komai ba zaiyi ma yan uwan shi ba ita ta kwammace yai ta bata kudin tana bin wani hanya dasu.
Yace Allah dai ya kyauta Fatima halin hajiya sai ita muyi ta hakkuri tunda Allah ya hadamu dasu.
Wayan shi da yai kara ya katse muna zance ya tsaya daukan waya a daidai lokacin na mike ina fadin yaya na gode zamu tafi gaba har gidansu mama muke son zuwa yau din nan.
Na fito na dauki jakkana na suba kudi a ciki yana fitowa daga dakin naji yana fadin ke barin baki dan wani abu a saya maki biscuit ko yana kokarin lalaben aljihun rigan shi ta gefe.
Da sauri nace a,a yaya don Allah ka barshi ni ga wanan dama na riko maka lokacin da muka zo ban samu kawo maka tsaraba kayi hakkuri da wanan ina mika mai kudin daga cikin daki da yake tsaye a kofa.
Yace Fatima kamar abin bin bashi ni ko wanan mutuncin da kike min keda mahaifiyar ki kun maidani tankar dan uwan ku na jini ai ya isheni daku .
Babu komai yaya don Allah ka karba ina dashine aina baka da bandashi gurin ka ai zanzo nima in samu yaji dadi yana fadin kwarai kuwa fatima yasa hannu ya karba yana min godiya.
Sai bayan ya karba yace kai kai kai Fatima kudine fa masu yawa kika miko min nace yaya ka wuce nan a gareni idan inada wanda yafisu sai in baka babu kyashi.
Godiya yai min sosai ya fita yana mun sallama sai bayan ya fitane na kalli anty salma da ido nace ko dan rakiya baki mai kiji ko yana da wani maganan da zakuyi tunda gamu a wurin.
Mun zauna da ita munyi magana sosai bayan la,asar muka fito gidan zuwa gidan mama saratu da kanwar mamu mama

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login