Showing 219001 words to 222000 words out of 419207 words

Chapter 74 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1445

ta a lokacin aga farin cikin da take ciki a lokacin bai musultuwa .
Yace saidai ba a samun ta sai weekend ko bayan karfe biyar a daidai lokacin tana gida ke nan don shine lokacin da ake samun ta kawai.
Ya karanto mata lamban ta loda a wayan ta cikin farin ciki tare da fadin na gode tana shirin juyawa Amma tace ni ina ta jiran ace muzo gashin cibiya sai naji shiru?
Dan kallon Amma yayi ya kawar da kai ba tare daya iya furta komai ba a wurin Amma taci gaba da fadin gashi yan uwanta wasun su suna da ciki yanzu.
Amma kin dai san ita karatu takeyi yanzu ko idan tayi ciki yanzu wa zai taimaka mata da raino da sauran su don gudun kada Amma ta gano komai.
Tace may ye aikina a nan ko aikin kakarta dake bukatan taimako sai ni in hakkura wanan boyar Allahn ta tafi don matar tana bukatan kulawa sosai.
Wata mace kuma kike magana yanzu kuma Amma ko har kin fara rudun tsufan ne hakan yanzu ?
Tace a dan maraice wanan mahaifiyar uban yar nan nake zance don tsakanin ta da A ruwa sai Allah .
Shiru yayi bai tanka mata ba sai can ya mike ya kalli Amma dake masa hiran da bai saurare yace zai tafi asibiti ya duba mahaifin shi dake can.
Amma tace ni kan ban gane wanan abin ba da na dauko maka zancen matar ka sai ka gudu ka barni anya kuwa sadauki kana kula da hakkin yarinyar nan yadda ya dace a can ?
Da sauri yaja ya tsaya guri daya yana kallon Amma kafin yace ko kinji wani abune gamay da zamana da ita ?
Tace ko daya yo a ina zanji labarin ku a gurin ka ya kamata muji komai gamay da yar nan saidai tun zuwan ka ba wanda kaiwa zancen ta a gidan nan kaf.
Hakan yasa nake zargin irin zaman da kukeyi a can da ita don yar nan Amana take a gutin ka kasani.
Ki bari in dawo indai zancen ta kike son ji zakiji komai idan na dawo shike nan ko ?
Ya fada yana kokatin fita yayin da Amma ta tsare shi dz ido tana zargin shi.
Luckyly ranan ina gida ban fita ba sai after two zamuyi pratical don haka na tsaya dan gyare gyaren gidan.
Mamu ta kasa hakkutin kirana har yamma gwada lauin daya bata take ta faman bin nombobin da kallo tayi a wayanta sai ko ya shiga.
Daga inda nake tsaye naji waya na ruri a raina na dauka anty Farida ce don nasan ba zai kirani ba shi a wanan lokacin.
Haka yasa na isa gurin don daukan wayan saidai ganin nomban Nageria yasa na tsaya wasiwasin daukan wayan ina kallon nomban karshen lamban yasa na gane layin mamu ne da don dama sauran nomban na biyun karshe ne ban haddace ba.
Da sallama a bakina na daga yayin data karba min ta bangaren ta ihu na saka sai kuma na sa kuka ina fadin mamu kukane yazo min lokaci guda.
Dan murmushi naji tayi ba tare da ta ban amsa ba har na saida taji banda niyat tsahaitawa tayi magana.
Sayadi don na kiraki kike wanan kukan hakan komay ashe dana sani da ban kira layin ki ba na barki.
Da sauri nace mamu ina kewan ku ina kewan kowa a gida nan banda kowa a nan sai Allah sai anty farida dana hadu da ita a school din mi ta zamay min kamar yar uwa.
Tace dama aure haka ya gada Sayadi idan kaji shiru lafiyace inji ba haushe muma muna kewan ki sosai kin sani a kullun sai gwaggon ki da kawun ki sunyi maganan ki hakama kannen ki.
Nace mamu bandake ke nan ko dan murmushi tayi tana fadin har yanzu dai kina da sauran wauta ashe ?
Na zunburo baki kamar tana ganina nace mamu ni yanzu banda wautan komai ni kadai fa nake rayuwana a gidana sai idan ya umar yana gidan nake tare da wani.
Dama ai idan ka auri mai mata Sayadi hakan ne ke faruwa don ba kullun yake tare da kaiba sai lokacin ka ai.
Duk da ban fahinci may take nufi ba nace mamu da gaskiyane kawu baida lafiya ?
Ta katse da fadin amma ya samu lafiya sosai yanzu don mijinki bai nisa da juyowa gare ku ai.
Yaya wurin su merry da yar ta suna lafiya nace banda labatin su mamu don ba gida daya muke zaune da su tsakanin akwai dan tazara so sai.
Sai dai wani lokaci nakan tafi inda suke amma yanzu na dade banje ba a cikin hikima da basira irin ta manya mamu ke min tambaya ina bata amsa ba tare da komai ba sai dai bata tambayeni irin zaman da nake da yaya umar ba nima ban fada mata ba.
Na tambayeta labarin amma da manjo da su Aisha ta dan ban amsa a gurguje akan suna lafiya Aisha nan haihuwa ko yau ko gobe ma .
Dan ihu murna nayi jin hakan tace salma da ikilima sun haihu wata biyu daya wuce nace ikon Allah.
Tambayan karshe da tayi mun ne yazo min a bazata tace ke yaya labarin haihuwa wurin ki ko har yanzu baki samu komai bane ?
Wani iri naji a raina na canza fuskana a lokaci daya tare da fadin mamu kin san ina karatune yanzu fa .
Sayadi ke nan karatun ki shi zai hana wani abu kardai kice min kuna wanan planning din banzanne kuma.
Ban san may planning ke nufi ba na hau yi mata shirmay sai dai abin yaro da babba a cikin shirmay na ta fahinci akwai matsala a zaman mu mukayi sallama tace idan taje asibiti zata ba kawuna waya mu gaisa.
Mukai sallama a cikin so da kauna irin ???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?ta uwa da yarta ta barni ina kewan ta ina hawaye ni kadai a gidan ina jin kamar in bude idanu in ganni a gaban mahaifiyata.

Umar yana zaune yayi wani irin zabura wani tunane yayi a zuciyan shi nayin gangancin ba mamu layi na kai tsaye ba tare da yayi worning dina ba kada in fada mata komai gamay da zaman mu.
Yana zabura ya duba agogon hannun shi da sauri sai ya mike tsaye don yasan lokacin daya ba mamu na kirana yayi don haka tana iya kirana in tona mashi asiri don ba wayau ke gareni ba.
Waje ya fita duk da likitana ciki yana duban yanayin daddyn su lokacin sai dai hakan bai hanna shi fita da sauri daga dakin ba .
Can dan nesa da mutane ya nufa ya kira layina lokacin ina zaune na saka abincin a gaba ina kallon na kasa ci sai tunane da nakeyi.
Wayana dake aje saman table din yayi kara da sauri na kalla a zato mamuce ke kiran layina lokacin.
Ya umar na gani wanan karon da sauri na dauki wayan ina mai sallama ya amsa min yadda yake karbawa nice nayi mai ya jikin kawu yace da sauki a takaice.
Zan kara magana ya tareni yana fadin ke naba maman ki layin wayan ki nasan zuwa anjima zata kiraki don haka saura ki mata shirmay da kika saba idan ta kira.
Don kika kuskura kika fada mata wani abu gamay dani ranki zai baci sosai wallahi idan na dawo garin nan don na kusa dawowa kwanan nan insha Allahu.
Shiru nayi ina sauraren shi har sai da naji yayi shiru nace wai mamu kake magana ai ta kirani ko tun rana mukai magana da ita.
Da dan karfi a razane yace what ?
Nace eh ina mai jin haushin shi a raina cewan da yayi min shirmay nake dashi a raina.
Yace makika fada mata data kira ki nace kamar ya magana tsakanina da mahaifiyata kuma saina fada ?.
Yace ke ni kike fadawa wanan maganan don rashin kunya ko may nace ni ban maka rashin kunya ba ai na daiga uwatace ta kirani ai.
Ke may kika fada mata nace kin tsaya kina min maganan banza da ina kusa dake dana doke wanan bakin mai maganan banza.
Ni zaki nunawa maimuna mahaifiyar ki ce ko mai na mayi regret din bata layin ki danayi tun farko don ba hankaline dake ba nasani.
Duk naji wani maganan da kika fada wanda bai dace ba a garin nan sai na saba maki sosai idan na dawo .
Jin yana magana kamar tababe yasa na kashe wayan da mamakin shi a raina ina tunanen may yake nufin zan fadawa mamu bayan alherin da yake min a nan din ga karatuna iba yi hankali kwance.
Matsalata daya shine kewan gida dake addabata ko yaushe bayan wanan wani hali yake zaton zan fada a gida dayake min din.
A bangaren shi kuwa yana kashe wayan Aliyu ne ta gani tsaye a bayan shi da alama duk maganan da yake fadamin Aliyun yaji shi lokacin.
Yana juyowa sukai arba da Aliyu din wani irin gilty ya kamashi lokaci guda ya daure fuska yana fadin kai kuma maynene hakan kazo ka tsaya mun a kai ina waya.
Dan murmushi Aliyu yayi, yana fadin cool down bros likita ne yace a kiraka ciki haka ya wuce dan uwan ba tare da ya amsa mashi ba.
Aliyu ya bishi da kallon maki yana girgiza kanshi cikin takaici yabi bayan shi zuwa ciki.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:19 - ??5惙5惙5?: BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM, , , , ,


Mamakin kalamin ya umar na kwana dashi a raina duk da kurciya ya hanani gano inda maganan shi ta dosa a lokacin.
Amma zuciyata bata hanani hangon ma,anan maganan tasaba sai dai bankai can inda tashi manufan ya dosa ba.
Washegari mun shiga karatun mu lafiya ban nemi anty ba don nasa yanzu ita karatun su yayi nisa tana gab da gamawane lokacin.
Bayan mun taso sai ga kiranta a wayana tana fada min ta tafi don yaronta da baida lafiya ranan.
Nayi mata Allah ya sauwaka muka kashe wayan bayan na dawo gida abinci kawai naci naga ya dace in leka gidan anty farida a karo na farko duk zaman mu tare ban san gidan ta ba ban ma taba zuwa ko layin nasu ba a rayuwana.
Shiryawa nayi duk da yamma yayi sosai na fito tare da rufe gidana na nemi taxi ta hanyan fada mai layin duk da ba nisa sai daya dan kalleni.
Ban damu da hakan ba duk da nasan manufan dan taxis din lokacin ganin yayi inda zamu a unguwar muke sanin ban san gurin ba ya hanani damuwa a lokacin.
Sunan layin da nomban gidan na fada mai sai gashi cikin dan kankanin lokaci ya ajeni a kofan gidan na biyashi kudin shi ya tafi.
Tsayawa nayi ina karewa unguwar kallon mamaki a raina duk kusan ginan iri dayane sai dai bai kai wanda nake girma ba da komai nan na gane ba cikin karamin gida nake ba ashe.
Na taka a hankali zuwa kofan na danna bell din sallaman dana gani a gidan ringing biyu aka bude kofan wata yar matashiyar budurwa ce a kofan tsaye tana min kallon mamaki.
Dan murmushi na sake a fuskana tare da fadin zainab ko don yawan kiran sunan ta da anty keyi kanwar mijin ta da sukazo da ita don kula da yaran su.
Itama murmushin ta mayar min a fuskanta tare da fadin kina neman wani ne a cikin harshen turanci tayi magana nace eh da hausa don ta gane nima ba hausace yar uwanta.
Juyawa tayi tana fadin anty farida ga wata bahaushiya yar uwan mu tana neman ki a kofa tare da kokarin jaye min daga hanyar shi don taban guri don in shiga .
Lah ikon Allah ashe kina hanya baki fada min ba fatima dan juyowa zainab tayi ta kalleni tare da mamaki a fuskan ta tace anty wanan dince fatiman dama ?
Anty tace itace Fatiman zainab yau dai kinganta a gidan mu ko ciwon daddy ya jawo muna ita zuwa gidan nan.
Zama mukayi muna gaisawa tare da tambayan ta jikin yarin nata da baida lafiya ta nuna min shi kwance saman kujera tare da fadin gashi nan yaji dama sosai na samu Abban su ya kaishi asibiti sun karbo magani.
Ban zauna ba na nufi gurin yaron tare da fadin babana ya jikin naka ina kokarin taba lafiyan jikin inji yadda yake.
Yaron ya dan dago kai tare da fadin naji sauki a hankali abinda na zo mai dashi na ciro a jaka na mika mai cikin kayan makulashen da yaya ya tara mu a gida wasu ban ma san dadin su ba har lokacin.
Yaron yai zubur ya mike tare da fadin nagode ya karbi ledan ya fara budewa a hankali ya dago kai ya kara fadin nagode anty.
Zainab ce ta matso inda muke tana fadin yau dai ciwo ya warke ke nan gidan nan tunda ga kayan kwadai an samu tana kokarin karban ledan a hannun yaron ya kabe mata hannu da sauri yana fadawa uwar.
Oya zainab dauki diyan ki zuwa ciki anty tace tana kallin zainab din a lokacin har budurwan ta mike tsaye taja hannun yaron zuwa ciki .
Sai lokacin nake tambayan ta yarta guda tace tana ciki tana barci ruwan da ke gaba ta kalla tare da fadin baki sha ruwa ba ko a kawo maki abinci ne don an kare ko ?
Nace banda yunwa yanzu gaskiya anty sai dai zuwa an jima wata kila zan dan taba na fada mata hankane don ta saki rai dani.
Har yanzun dai maigidan ki bai dawo ba kasan nan ba fatima tana kallona take maganan na dan duka ina tsiyaya ruwan dake gabana nace.
Bai dawo ba anty sai dau munyi waya ga jiya dashi har da mama ya bata layina ta kirani .
Kai amma ko ya kyau ta gaskiya dama abinda nake son tambaya ke nan yanzu ai.
Nace sai dai anty kamar an tursasa shi ya bata layina don daga baya ya kira yana min fada nan dai na kwashe yadda mukayi na fada mata komai .
Sai dan murmushi naga ta sake a fuskanta tare da girgiza kai tana fadin barazan banza ke nan yasan yana jin tsoron mahaifan sa amma baya jin na Allah dake kallon shi .
Amma ai anty yana kula dani tunda ya tsaya min a karatu gashi babu abinda na nema na rasa a rayuwata matsalata daya shine rashin yan uwa a kusa dani.
Wanan kuma nasan na dan lokaci kadan ne da zaran na gama kararuna zan koma gare su ne ba shike nan ba anty.
Ido ta zuba min tun lokacin dana fara maganata babu ko kyatawa har na kare .
Naji rata wani dogon tsuki tana fadin Fatima kin ko san may aure yake nufi a rayuwan ki ?
Mijin kine fa na sunan ma,aiki kina zuwa makaranta a gida malaman kun suna koyar daku abinda aure ya kunsa a addinance kin sani ?
Shi kansa yana tauyewa kansa hakkine akanki kuma ke kanki yana cutar da rayuwan ki ta fanni daban daban fatima.
Ke bari dai in fada maki gaskiya ki sani rashin tararyan da baiyi dake na aura taiyya yana cutar dake sosai fatima sosai.
Iyayyen ku bawai sunyi wanan hadin bane a tsakanin ku don kizo nan kiyi karatu kawai ko ya zuba maki ido haka yadda yake kallon ki.
Shin fatima ke ba mace bace baliga mai jini a jiki da zaki kwana gida daya da mijin sunan ki baki ji komai a rayuwan ki ba.
Ruwa na dauka na sake kurbawa a hankali idona suna a kanta na aje kofin a hankali nace, ko daya anty don ni a matsayin dan uwa na jini nake kallon shi .
Ko kadan ban taba mashi kallon miji a gareni ba sains yan uwan taka har matar shi duk basu gabana wallahi .
Ni dai burina kawai in ga na hada karatuna na koma gida gurin iyayyena na kai masu kwalin sun gani.
Kai amma sai kuma tace wai fatima in tambaye ki man ?
Yanzu shekara nawa kile ne nace cikin dariya sha takwasa nake yanzu zan shiga na sha tara koda nazo nan ina da shekara sha bakwai cif anty.
Gaskiya wanan dan uwan naki bai dace dake ba wallahi cutar yayi yawa wallahi .
Shiru tayi kamar may tunane kafin can tace kina jina shin wai sharan dana baki a baya kina amfani dashi fatima ?
Ta tsareni da ido tana son jin amsa daga bakina a lokacin na dan kai bayana ga makarin kujeran da nake zaune a kai nace ina wasu ban wasu gaskiya.
Yau she ma na ganshi a gidan har

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login