Showing 411001 words to 414000 words out of 419207 words

Chapter 138 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1409

ta kawo min don in bashi nono karban yaron nayi duk ya langabe nasan yayi kukane har ya gaji don bai sansu ba.
Habbib suka shigo tare da Aliyu don tunda sukai sallah suka tafi gida daga can sai gashi an kirasu kan anga likitoci na shiga dakin da sauri har nima ina cikin dakin ba wanda ya san meke faruwu a ciki.
Bayan sun gaisa da mutane suke tambayan halin da dan uwan nasu ke ciki ake fada masu nice dai na shiga don su suna waje tsaye lokacin da abin ya faru.
Yaya habbinb ya tako zuwa inda nake zaune mun gaisa yayi min yaya jikin na amsa mai da sauki ya gyara tsayuwa tare da tambayan hakin da ake ciki ina mai bayani.
A lokacin sauran yan uwa suka matso don jin halin da ake ciki na fara mai bayani sai ga likitan dake dubashi ya fito daga dakin nan kuma suka koma gareshi akai mai caaaa da tambaya.
Wanan ba wani abin mamaki bane a kasan mu yadda masu jinya kan tasa likita gaba da tambayan halin da mara lafiyansu ke ciki.
Nunani yayi yana fadin yanzu itace likitan nasa ai don ta karantu a wanan fannin sosai fiye da tsamanin ku.
Zuwan ta nan ya tai maka muna sosai don a halin yanzu numfashi ya koma daidai yadda muke so.
Nan dai likitan ya kara kwantar masu da hankali sosai sai a lokacin hankalin kowa ya kwanta don ana ganin sauki a gareshi.
17/11/2021, 07:26 - ??5惙5惙5?: Ganin sauki sosai ga yaya hankalina ya dan fara kwantawa sai dai a kasan zuciyana tunanen wanda yai mashi wanan aika aika yake min yawo a rai.
Don zuciyana ta kasa tsayawa wuri daya a tsakanin abu uku da nake zargi nafarko dai itace merry da nake zargin tazo daukan fansan yarta a kanshi .
Sai na biyu itace samira da mahaifiyar ta da ake zargi suna iya aikata hakan don abinda ya faru a tsakanin su yan kwanakin da suka shude.
Wanda yan uwa da abokan arziki sunfi zargin hakan garesu don tun da yaya habib yaji abindana fada bai yarda ba shi sai cewa da yayi merry tsorone da fargaba kila yasata ta bar kasan a gigice.
Shi yanzu bukatan shi shine asan inda merry da ake nema ta shiga tun daren jiya din ba,a ganta ba kada dai kuma wani abu yazo ya faru da ita nan gaba a kuka dasu daga baya kan hakam.
Ni kawai jin su nakeyi don sanin wacece merry a yanzu da nayi don sanin halinta akan komai da yadda wayewan ta yakai a America din.
Dole na gyagije ga nawa ciwon muna fuskantan nasa don ni nawa tsorone da fargaba ya saukan min da ciwo na dan lokaci guda dama.
Saidai duk da na gyagijen bai hana kaga damuwa da tashin hankali a tare dani idan ka kalleni sau daya saina baka tausayi a yadda na koma.
Hjyn su yaya ita kanta ta fita daga hayacin ta sosai don nan gurin shi itama ta wuni a ranan duk da ga yan uwanta sun mata kara don sun cika asibitin sosai.
Amma hakan bai hana hjyn zama asibitin ba itama da ka ganta bata cikin hayacin ta ko kadan a lokacin kowa hankalin shi yana a tashi da faruwan al,amarin.
Yan sanda sai aikin su na bincike kan case din sukeyi basu gane komai ba sai washe garine da dayan mai aikin wanda bai mutu ba ya farfado suka samu dan haske gareshi kan al,amarin.
Don yan sanda najin ya farfado suka garzayo dakin da yake suna mashi tambayoyi yadda abin ya faru a gidan.
Yake fada masu da misalin karfe biyun da wani abu na dare suna kwance sukaji harbi bindiga.
A inda ya gane ba hausawa bane don turancin yaji suna yi akan harbin da daya su yayi ogan su na mashi fada kan hakan yana fadin madam tace damu bata son a harbi kowa a gidan nan kai gashi yanzu ka harbi maigadi kilama ya mutu.
Yaran kawai tace mu kwashe koda ba duka bane ko daya muka samu mu dauko mata kazo zaka batawa mutane shirin su kuma.
Yace oga yana da bindiga fa a hannun shi shi yasa na harbe shi kada ya harbe mu mutumin yace ina jin haka sai na shiga cikin tarkacen dake dakin na kara lafewa sosai.
Sun kai su nawa a naka ganin da suka shigo gidan dansanda ya tambaye shi .
Yace zasu kai su takwas ko fiya da hakan do su kasu kashi kashi a gidan don har wajen gida wasu sun tsaya daga cikin su.
Nima dai rabon wahala yasa na fito wajen da niyar in gudu a lokacin danaga hankalinsu ya dauke a cikin gidan injin karan harbe harbe na fito da niyar gudu.
Sai dai ban san akwai biyu ko uku a waje ba lokacin ne suka harbeni sai dansanda ya dakatar dashi da fadin.
Kafin ka suma bakaji wani karin kalamin da zamu rike a matsayin huja ba a bakin su sai mutumin ya girgiza kai alaman baiji komai ba.
Dansanda yayi mai godiya bayan yan rubuce rubucen da yayi a takarda a lokacin ne saurayin ke fadin yallabai na tuna da wani kalma danaji sun fada kwarai a lokacin.
Da suke fadin we should rush mu bar garin nan yau komai dare kada a kama mu sai dayan yake fadin Samuel fa da aka harba yace dashi zamu tafi.
Don barshin a nan risk ne gare mu don za,a iya gane hakan ta hanyar shi don haka zamu tafi dashi ke nan.
Dan nazari dansanda ya tsaya yayi kafin ya mike yanawa saurayin godiya tare da fatan samun sauki ya fito ya leka a dakin da yaya yake kwance.
Bayan tafiyan dansandane kowa ke fadin albarkacin bakin shi kan abinda saurayin dake muna wanki ya fada wanda daga kauye ya shigo gari neman kudi dama nasir ya dauke shi aiki a gidan.
Ban furta komai ba don magana yana dan fara dauko kamahin gaskiya sai nake jin ko a can gidan mu da yaran suke zaune kamar basu tsira ba a hannun makiyan.
Don zasu iya cin masu can su dauke su tunda sunyi niyar yin hakan a kan yaran nawa haka ya jawo hankalina kasuwa gida biyu a gurin tunane yanzu.
Zuwan mamu da kawu ne ya dan kwantar min da hankalun don sun samu labarin abinda mai wankin mu ya fada tun suna gida.
Kawu ne yakw fadin in kwantar da hankalina tunda har Allah yasa mi sanin gane wani abu mara kyau yana shirin faruwa da yaran naji a jikina kuma har hakan ya faru .
Sai in godewa Allah in dage dayin addua don addua itace takobin mumuni Allah ya kara tsarewa insha Allahu Allah zaibawa yaya lafiya ya tashi da yardan ubanginji.
Wanan kamar kina nunawa ubangiji rashin godiyane yau da ace wanan abin ya zama sanadin rasa umar fa ?
Ashe ba zaki zamo mai tawakkali ga jarabawan ubangijin ki ba fatima ?
Jin kalamin kawu yasa na dago kai ina kallin shi tare da kokarin share hawayen dake zubo min a lokacin.
Bayan kawu ya mike don shiga yaga dan nasa ya rage wurin dani da mamu sai Amma dake lazumi tana sauraren mu .
A hankali nace mamu yaran basu damun ki ko a can don nasan su da fitina idan basu ganin dayan mu tare dasu.
Saida mamu ta sauke ajiyan zuciya take fadin basu fitinan komai tunda ga sadiya nan da maria suna gani yau daine ita yar fitinan ta matsa da kiran mummy mummy ina jin maria tana lalashin ta itama kanta maria ai abin ya bugeta sosai don bata a cikin dadin rai duk yinin yau din.
Sai lokacin Amma data shafa addua take fadin yo ina zataji dadi wanda kake tare dashi yana a cikin wani hali haka mara kyau.
Mamu n fada maku ni zuciyana tafi karkata gun merry din nan don yarta da yaya ya karbe a hannun ta yanzu.
Kada kice haka sayadi don zato zunubine koda ya zama gaskiya don haka ki daina wanan zargin.
Sai ya kasance ita bata ma san da wanan zancen ba sai wani ya taka sawunta yai wanan aikin .
Abin ne da kama ai dole yar nan tayi zargin hakan don biri yai kama da mutum gashi an nemeta an rasa a garin nan tun jiya.
Wata kila tsoron taji kamar yadda habbib ya fada ai ana kan bincike dai insha Allahu gaskiya zata baiyana komai daren dadewa.
Fatan mu dai Allah ya tayar da kafadan shi ya bashi lafiya yasa hakan ya zamo mashi kaffara a yanzu.
To Amin Amma ta fada tana kawar da kai tare da fadin ni dama auren sadauki da kafiran nan bai taba kwanta min a rai ba sai ace ranon yar nan daine kawai ya kaishi ga auren ta .
Amma wanan ai ba macen nunawa tsara bane a fage don banga wani abinda yaja shi gareta ba.
Aurene gwaggo Allah ya kaddaro akwai aure a tsakanin su da rabon yar nan da kika fada yanzu.
Idan ba wani abuba ai sai ya bata yar ta karata can da ita ta bar dan nan ya zauna lafiya Ammake fadan hakan.
Amma wai kin san sai da wanan matar ta saka aka kwace wa yaya komai a can da farko kamar zasu rabo dashi sai gasu kuma sun kara dinkewa daga bayan nan.
Ke yar nan ki bar wanan zancen aka kwace mashi dukiya kuma yake zaune tare da ita ?
Kwarai Amma don kawai kara aurena da yayi daga bayan nan taimakon yaya guda shine tun farko sunyi alkawari a rubuce cewa ga addinin shi ya yarde mashi ya kara aure .
Kuma ta amince da hakan saidai lokacin da tasan da zancen aurena dashi ta kaishi kara kotu dole kotu ga al,adansu nacan ta raba dukiyan sa biyu ta bata rabi.
Bata san da yana dabaran turo arzikin shi gida ba daga bayan nan kuma da ta sani ta biyo shi har kasan nan da jidali wai a cewan ta tare da ita suka samu arziki don me zai munafunce ta yayi hakan ba tare da sanin ta ba.
Rikincin gangan ke nan wanan ta zama Sarka mai rikucin gangan arziki nasa sun hada karfi ne tare da ita ?
Gwaggo kin san su ga al,adan su ai haka abin yake na miji baida halin yin wani abin ba tare da sanin matar shi ba irin namu na nan.
Yau ina mahaukaciyar uwar shi tazo taji wace tafita famkama da abin danta ita da da anyi zance zatace ni uwar maza ne masu arziki kuma ?
Yoni wanan jahilci ko hauka za a kirawa jimmai yau dai idan umar ya fadi ya mutu ke A ruwa kin fita kaso a cikin abinda ya bari shine kawai bakin ciki da hassadan jummai dama dake.
Amma ni ban taba tunanen irin wanan ba a rayuwana idan za a barmin shi yafi a bar min tarin arzikin da hjy ke hange.
Affa ke kika san wanan Aruwa rikicin jummai ai ba sai da dalili ba abin ya zake mata a jiki don ita bata bar kowa ba.
Duk da wanan abinda ya sameta baisa jummai yin nadama ba don dazun nan kuna ciki wurin yaron nan take fadin wai dama ana son ya tafi a mamaye abinda ya tara.
Har abin yaso zama masu fada da hadiye shine dalilin dana tura hadiye gida dazun .
Don ba zamu taru anan ana sayar da hali ba mutane suna tafiya damu a baki.
Kai halin hjy sai ita duk da bawan Allah nan yana cikin wanan halin bautan ubagiji zukatan mutane baya a kwance take wanan furcin.
Mamu ne ke fadin wanan magana tana kada kai taci gaba da fadin wa take zargin ya aikata hakan yanzu gareshi ?
Na nisa tare da fadin ni zancen hjy bai taba damuna a yanzu matar da taje neman wace zata kifar da mutuncina a gidan yaya don kawai kiyayya irin nata.
Mai kuma zatayi ko ta fada a kaina yanzu inji zafin shi a kwance take amma zuciyar ta na cike da sheri.
Kawai lamarin hjy sai addua a gareta idan tana da rabon shiryuwa Allah ya gyara halin ta.
Na dauka wanan abin da ta sameta a yanzu zai sa ta yin nadama sai gashi har yanzu zuciyar hjy bai saduda ba ga yawan aikata sheri gana tare da ita .
Kafin wanan abin ya faru na fito da safe na samu mama asabe waje tana kuka nake tambayan ta.
Da farko bata so fada min ba saidana matsa da nuna mata damuwa na take fada min ita ta gaji da halin hjy.
Don duk dawainiyar da take da ita bata ganin haka wai jiya don tace a kiran in duba ta take fadin ta fahinci akwai makircin da muke kokarin kulla mata nida ita.
Don taga yadda take shige mun idan na shigo tana wani yabona to ta sani duk kilibibin da nake kallona kawai take don ta gane nufinmu a kanta.
So nake kawai na karasa nakasata sai nace mata haba hjy wanan wani irin magana ne yarinyar nan fa itace fa silar samuwan saukin ki a yanzu.
Sai cewa tayi dani koda banzo ba idan Allah ya nufa zata warke ne ta tsani ki ta tsani duk wani ahalin ki jin hakan da nayi nace .
Wa,iyazu billahi hjy mai yai zafi hakan uwar jikokin kine fa kike aibantawa hakan.
Nice shedaniya kike nufi da kike kore min shedan komai to bari kiji indai a kan wanan yarinyar da tayi sanadiyar barina dakin aurena kike kokarin karata a gaba ki sani bani bake asabe.
Dama nasan ba don Allah kike min abinda kike min ba don wani manufa takine kawai don da ba zaki goyi bayan yarinyar nan ba haka alhalin kin san irin kuntata min da sukeyi da ita da uwarta.
Mama asabe ta kare da fadin yanzu FFatima ya dace duk irin kokarin da nake da hjy tace min wai ba don Allah nake kulata ba .
Don haka ni na gaji wallahi tafiyata zanyi ba zan iya wanan abin ba gaskiya jiya sai abinda hjy ta manta bata fada min ba.
Nace mama don Allah kiyi hakkuri kada kice zaki tafi don yaranta yadda suka daukeki bazasu ji dadin hakan ba idan kin tafi.
Hjy halinta sai ita wallahi ya kamata ace iyanzu kin saba da wanan halin nata ita da kanta zata dawo ta nemeki ai .
Tunda ba zata iya yiwa kanta wani laluran ba dole sai an taimaka mata bamu rufe baki ba mukaji muryan ta tana kiran mama asaben.
Amma tace ke ki duba min wanan abin mamakin don Allah wai mutum na kokari da kai kake masa wanan bala,in haka don wani dalilin naka can.
Ganin su kawu sun mike daga inda muke iya hangen su a zaune suna magana sunyi cikin dakin da yaya yake kwance da sauri.
Saurin mikewa mukayi lokaci guda don bamu san abunda yake faruwa ba a dakin suka mike zuwa dakin nasa.
Kusan nice a gaba wurin shiga dakin a tsartsaye na samu su kawu suna gaida yaya din da yake kwance yana bin kowa da idanuwan shi.
Sai dai duk gaisuwan da suke mashi bai amsa ba sai binsu yake da idanuwan shi kamar wanda bai karkare farfadowa ba a lokacin.
Zuwan mu kusa dashi yayi daidai da karasowan su hjy gurin hjy tana ririke a hannun yan uwanta.
Ganin su yasa muka dan tsaya a bayansu kada sai gaidashi da jiki sukeyi mai ina gefe tare da mamu da Amma sai hamdala nake ga ubangijin talikai daya rufa muna asiri yaya ya samu lafiya.
Ganin ba za,a sarara ba a lokacin yasa na karasa bakin gadon na fara fadin yaya sannu ya jikin ?
Sai lokacin ya dan juya kanshi yana kura min ido kafin yayi kokarin budan bakin shi yana son yin magana.
Sai dai ya kasa sai kuma ya lumshe idanuwan shi a hankali ganin hakan da yayi ne wani kuka ya kubce min lokaci guda.
Bani kadai ba kusan matan dake dakin hawaye suke a lokacin Amma na fadin saudaki sannu ya jikin kuma tana share hawaye .
Jin muryan Amma din yasa ya kara bude idanun shi a hankali yana kallon mu ya kara dago ido ya kalleni a karo na biyu.
Kuka nake yayin da iyayyen mu maza ke fada dani akan in daina kukan sai ya dan saki dan murmushi kadan ya lumshe idanuwan shi.
Muryan likitan shine ya shigo yana fadin haba a rage yawa a dakin don ba,a son a dameshi da yawa hakan zai iya kara jefa shi cikin wani damuwa.
Jin yadda nake kuka yasa likitan dago

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login