Showing 267001 words to 270000 words out of 419207 words

Chapter 90 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1388

ko a can ana tsula sanyi gwargwadon yadda Allah ya tanadar wa kashen Africa dashi.
In zaki tuna na fada maki kawu baya fita sosai a irin wanan lokacin yafi zama a gida cikin iyalin shi balle yanzu da jikin nasa sai a hankali jefi jefi yakan leka kasuwa don ya dan motsa jkin sa da yai mai nauyi.
Yau hjy jummai zata fita girki mamu ta karba don girkin gidan a daidai yake tafiya basu hautsana shi ba don dokan hjy jummai ce hakan ko tafiya kayi ka dawo dole sai ka jira idan girka ya zagayo ka karba wanan dokane daga gare ta babu mai tayar dashi kuma a gidan.
Abu ga wanda tsufa ya fara hara a kaidan su karfe shidda ne fita gitkin mai girki a ranan sai dai zuwa biyar zaka iya zuwa kayi aikin daya dace a shiyan maigida kada yamma yayi ba,ayi ba.
Mamu ta dauki abin shara ta nufi sashen nasa a waje ta samay shi zaune yana shan iska duk da sanyi ya fara saukowa a lokacin kowa na haraman natsa kansa guri daya.
Gaida kawu tayi kamar yadda sukanyi idan yana gidan ta wuce zata shiga sashen nasa yace da ita.
Maimuna da zan samu ruwan dumi in jefa kafafuwana a ciki da zan so hakan yanzu dan jimm tayi kafin tace ko a dauko maka waya kakira hjy ta baka don ban son abin fitina ko kadan da saura lokacina yayi ka sani.
Da mamaki ya kalleta yace ruwan ma shi zai zama abin wani kishi a gare ku yanzu ?
Kamar tayi magana sai ta wuce zuwa ciki ta tara ruwan?????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? zafi a roban da suka tanadar mai don yin hakan.
Tana kawo mai yayi godiya wanan yana daga cikin dabian kawu godiya bai bata lokaci ba ya saka kafan nasa kamar yadda yake so don yana jin dadin hakan wani lokaci.
Tun data tunkaro wurin idon ta ya sauka akan roban gasa kafan dake gaban shi lokaci daya kishi ya ziyarci zuciyar ta.
Ta karaso a fusace tana fadin ya naga haka kuma waya rigani zuwa karasa min aikina ?
Kawu da idanun shi suke a lumshe saboda dadin ruwan da yake ji a lokacin kallon ta kawai yake don ya hango masifa a fuskanta lokacin.
Alh tambaya nake waya baka ruwan saurin da nakeyi ke nan yanzu nasan zaka bukaci ruwan a wanan lokaci.
Jummai zan zaunane ina jiran sai lokacin da kika fito ki bani ruwan mai yasa ke baki da tausayine a rayuwan ki ko kadan bani ruwan ma yanzu laifine a gurin ki ?
Amma kasan dai hakkinane yin hakan a wanan lokaci ko ?
Dama abinda take son hadawa ke nan mugun iri marasa asali gaba da baya masu abin kunya tatare a duwawon su.
Wai har wanan masu kashin tsiyan don son kai zaka dauko yar ta ka jefa a cikin iyalina don su bata min zuri,a da kashin tsiya irin tasu dasuka gada.
Wanan ba wani kike zagiba ni kakazo ki zaga dama, idan har wani yana da kashin tsiya a gidan nan to kece gaban masu shi arkin da kike kurin yaran ki nadashi nakine Jummai ?
Da bazarwa sukakai hakan da kike yanga wa mutane maimuna dai da kike zagi ina jininane idan kuma tana da kashin tsiya nima ina dashi ke nan don abu daya ya fitar damu duniya.
Ke har kina da bakin magana sananin kankine bantaba rike arzikin dana rike ba a lokacin auren maimuna a duniyan nan.
Wanan magana daya fada a karshe shiya harzuka zuciyar hjy ga baki daya tace may kake nufi da wanan magana yace kema kin sani ai.
Da can da kika matsamin in kai yaran ki waje ba durkushewa nayi kasa ba ga baki daya sai kama kama muke a gidan nan dan shago gudan dake gareni yana neman subuce muna.
Alh ya isheka haka kai bakaji kunyar fadan wanan maganan ba yanzu wanan hayaniyar da suka soma ya jawo hankalin yan gidan a baki dayan su suka fito.
A daidai lokacin da hjy ke fadi banda arziki ka dauki yar agolan ka ka jefa a zuria ta don kada ta wullakanta .
Kai amma jimmai zuciyar ki na kafiraine Amma ke fadi daga nayan ta wace tsofa ya tasata gaba yanzu tace mutumi na cikin wanan irin halin amma ke kishin ki bai barki kun zauna lafiya ba.
Hajiya fitina ya kawo dama ki duba yanzu karfe nawa tasan ina nan batazo ta ban ruwan dumin nan ba sai lokacin data kwatanci yar uwarta tazo ta ban tazo tana fitina sakarai wace bata kama girman ta ko yaushe.
Amma ita maman fauziya may ya kaita baka ruwan bayan tasan ba haka mukeyi ba inji hjy maryam ta fadi haka .
Wai sai a barshi a zaune da lalura yana jiran sai lokacin dataga dama tazo ta bashi bayan tasan ka,idan yadda kukeyi.
Kai ku rika maganan gaskiya don Allah ai kishi ba hauka bane don ma antaimake ta dama ke bugi sa bugi taikine aikinki a gidan ba fadan gaskiya kikeyi ba sai son kai don a yabe ki.
Hadiye kada ki fada min magana a nan don kawai na fadi gaskiya ai da gangan tai hakan don tasan yana cikin ka,idar mu yin hakan.
A daidai lokacin mamu ta bude kofa ta fito daga dakin dauke da tsitsiya a hannun ta maganan hjy maryam yakai kunnen ta.
Kallon kawu tayi tace na fadama wanan abin zai iya jawo matsala gashi ko ya jawo din.
Kai ni wanan abu ya isheni wallahi yau dai ku sheda na dakatar da jimmai da maryam girki a gidan nan abar mutum daya yai jinya ta har lokacin da Allah yaban lafiya.
Ina wuta su sakashi a lokacin har mamun fada take ita bata yarda ba a lokacin saresarin a sakata gaba da wani kullin ya fadi a tsawace yana mikewa tsaye wanan dokanane haka kuma na yanke a raina da kyat yabi bango zuwa ciki cike da bacin rai a tare dashi.
Amma ce tabi kawu ciki ita da mama hadiye mama hadiye na fadin hakanma yafi wallahi mutum a cikin lalura za a ce sai lokacin da akaga dama za a kula dashi wanan wani rashin imanine haka don Allah.
Wanan abin zaijawa maimuna bakin jini a gurin su kuma shi nake son ku kula maimuna mutum ce mai ruwan ciki sosai.
Hajiya don Allah ku barni dasu idan ba ta baya na fito masu ba nagane so suke su karasani da raina.
Tau gidan kane iyalin kane abindaka yanke daidaine amma a sasauta don Allah Amma ta fada tana fita daga dakin.
Ranan kan zagin tonon asiri da gori mun shashi sosai ga bangaren biyu kowa ya koma sashen shi zuciyar shi cike da bacin rai abinda ya faru.
Hjy maryam da tayi waya tana shedawa yar uwarta abinda ya faru sai yar uwan nata tace daidai ke nan yayi min daidai tunda ana rabaki da shiga sharo ba shanu kinki dainawa ta kashe wayan kawai ta barta dashi a hannu.
Ita gaiyyan aikin yaranta ta shiga kira tana labarta masu saidai tayi neman layin umar ta sheda mai halin da ake ciki saidai bata samu layin shi ba ya manta tunda ya dawo ya canza layi saboda busy da yai mai yawa.
Amma ce tayi wa mamu magana don da ta bijire akan ba zatayi ba saida daddy yakai karanta ta yarda akan zatayi din.

Mun kashi rikici sosai da yaya da farko bai gane abinda nake nufi ba sai daga baya ya fahinci manufata din.
Kai ya girgiza tare da fadin baki da wayau yarinya karamace ke shiya har kikai tunanen hakan.
Banji kyamar merry da idan ta gama ba wankan tsariki takeyi ba sai ke da nasan kina wanka kina kula dashi yadda addini ya tsara zan kyamata ?
Ni lokaci ne banda shi kawai na zama gida saboda course din da mukayo a chaina muke gabatarwa a nan don karuwan na baya mu shiyasa nake kai wani lokaci a waje hakan.
Kunya ya rufeni gabadaya don yana fadi ya bar dakin ya tafi dakin shi abinshi.
Yanzu mai nayi haka na tambayi kaina waini nasan dadin namiji a kusa dani ko may ke nan nayi din.
Tunane nayi sai kawai na danna layin anty Farida a cikin daren nan na kirata kaf na kwashe abinda ya faru na fada mata tare da tambayanta abinda zanyi ?
Tace tawa kice min komai yai daidaita ke nan yanzu tsakanin ku har kin fara kishin mijin ki kuma.
Ba haka bane anty saukowan shi gareni da kuma matsin mahaifiyata daku yasa na yarda makaman yakina dariya ta tuntsure dashi tana fadin yanzu dai ki tashi ki shirya ki samu mijin ki a daki ki san kinyi gyaran da ba zai iya kawar da idon shi a kanki ba.
Godiya nayi mata bayan ta gama min bayanin komai na mike sai bandaki banda wani abin da ta lissafa min inyi don haka na dan zauna a ruwan zafi ina zaune ba a dauki wani lokaci ba naji na kara hadewa kamar ba wanda ya taba shigana.
Na zauna nayi komai kamar yadda ta umurce ni in yi manyatacen rigar baci na saka daga cikin wanda ya dawo min dashi da farko har ina zagin rigar dana dagashi naga harahara din shi yayi yawa sosai.
Zaune na samay shi a dakin shi ya harde kafa kamar mai tunane a lokacin sallamana yasa ya juyo ya kalleni.
Bai iya kawar da fuskan shi gareni ba har na karoso inda yake a hankali na tatare rigan cikin sallo na hauwo gadon jikin shi na dan fada ina fadin yaya har yanzu bakai barci ba ashe ?
Dan ajiyan zuciya ya sauke kafin ya kai hannin shi ya rungumoni da kyau yana fadin mamaki maganan ki nakeyi zarah kayi hakkuri nace ina kai kaina saman kafadan shi na kwanta da kyau.
Wani iska ya furzo daga bakin shi duk cikin sauke ajiyan zuciya ne hakan yace ban san yaya zan maki bayani ki gamsu dani ba.
Hakkuri na sake bashi na hana bayanin da yake son min din a lokacin ta hanyan hura iska a hankali zuwa cikin kunnuwan shi wanan abinda nayi ya jagula muna lissafin komai.
Sai da komai ya lafa a tsakanin mu na yunkura da niyar shiga bandaki da sauri naji ya rikeni sai da gaba ya sake faduwa a zatona wani abin zai sake min da wanan katon kan ihu sosai zan masa.
Amma sai naji yace dani not now ki bari sai dan anjima ka dan zaki iya kewayawa ba a wanan lokaci ba dan kallon shi nayi sai naga ya kawar da fuskan shi kamar bashi yai magana yanzu ba.
Kewayan da banyi ba ke nan sai a cikin dare na falka na samu yayi wanka ya gama sallah yana zaune yana karatu.
Nima wanka nayi daga gurin kewayawan na fito sai dai da yake ban zo da shirin sallah ba don haka na sake kwantawa da alwala a jikina kawai.
Sai asuba ya tayar dani sallah dakina nanufa na sake wanka tare da dauro alwala na fito na dade zaune ban daga ba ina addu,oi wani barci mai dadi ya dinga fisgana daga inda nake zaune dan kwance nakai a kasa gurin da nake zaune.
Shikuma samun kanshi da yayi da rage aiyukan dake gabanshi ya tuno wayan shi akashe yake duk wanan lokacin ya mayar da sim din nashi ya kunna waya.
Ya Umar zaman turaine kawai amma bai yarda ya yarda addinin shi da al,adun malam bahaushe ba don idan ya tashi ya tashi kenan sai kuma wani daren zai zauna bayan ya gama addua ya duba sakoni a laptop din na mayarwa ya mayar wanda baida bukatan amsa ya barshi.
Ranan baisan ya akayi ba sai barci ya dan fisgeshi har yai mafalkin da hajiyan su ina gudu tana bina da sharbeben yuka ga yara ina ja acikin galabaita.
Innalillahi yace lokacin daya mike zaune daga ringinginen da yake kwance din yana mamakin yadda akai barci ya dauke shi da kuma tuna abinda ya gani a mafalkin nasa.
Addua yayi kafin ya mike ya shiga yai wanka ya shirya daya fito saukowa yayi sai jini gidan tsit kamar babu kowa a gidan lokacin .
Haka yasa ya gane banfitoba kamar yadda na saba fitowa inyi aikina da safe dakina ya juya ya kalla yana rufe ya nufi dakin ya tura a hankali ina kwace ina dan juye juye cikin wahala ina dan magana irin na mai mafalki takawa yayi yana kiran sunana ban amsa ba sai ya saurara da kyau yaji ina fadin salma mai nayi maki zaki kashe ni ?
Gaban shi ne ya fadi jin abinda nake fadi da sauri ya bugi filon da kaina ke sama ina kwance a kasa yadda na kwanta a wurin danayi sallah.
Mikewa nayi a wahalce na sauke idona a kanshi yana tsugene daidai saitin fuskana kamar yana min addua a lokacin.
Ki tashi yace yana mikewa tsaye kwanci a wanan lokacin baida kyau kin sani yana toshewa mutum hanyan alherin sa ne.
Dan mika nayi tare da salati ina fadin bansan nayi barci ba a nan saidaya juya yace wanan dabi,ar kine nasani ya kamata ki daina.
Ban fito daga dakin ba sai dana shirya na fito yana zaune a falo na gaida shi da kwana zan nufi kitchen naji yace ga abin karyawa nan na amso muna yana nuna min kwalin daya sayo din.
Dan jakkan kwalin na dauka na nufi danin dashi ina fitarwa a hankali pakege ne a ciki guda uku plates na dauko a kitchen na juye a ciki ina mamakin ko a ina ya sayo shi da wanan safiyan haka ?
Chip's ne sai ganye da sauran tarkace irin abincin su na turawa na juyo ina fadin yaya ga abincin ya mike kamar dama ni yake jira in hada lokacin.
Har muka kareci ba wanda yai magana a cikin mu saidai ina kula da yadda yake tura abincin kamar yana da damuwa a ranshi lokacin.
Yana gamawa ya mike ya barni a gurin na dan dauki lokaci nima cikin damuwan ko may ya samai shi ya canza haka lokaci guda oho ?
Yana zama yaji sako ya shigo mai a waya kamar ya share sai yadai ya dauko wayan yana dubawa Aliyu ne yayo mai text.
Bros ina komai lafiya a wajenka mama tana neman layin ka bata samu akwai matsala a gida daya faru sai dai kabi hukuncin ta a sannu don Allah don ta dau zafi dayawa.
Iya abinda ya rubuta kenan ya dade yana maimaita sakon bai fahinci komai da sakon ke nufi ba iya abinda dai ya fahinta shine .
Akwai abinda ya faru a gidan wanda mahaifiyar su ke son daukan fansa a kaina kila kodai wani abin.
To ko shiyasa yayi wanan mafalkin dayayi da safe yasan dai shi ba gwwnin yin mafalki bane sosai hakan.
Idon shi a lumshe koda na fito yana tunane a ranshi rabuwa da zarah matsala ne gare shi yanzu kamar yadda mama ke nufi abin ya wuce nan yanzu.
Na nufi dayan kujeran zan zauna duk da idon shi suna rufe naji yace zo nan ki zauna yana nuna min gefen shi.
Sai lokacin ya bude idanuwan shi yana kallona na mike a hankali zuwa inda ya nuna min cikin kunya don munyi kusanci sosai da inda ya nuna min in zauna din.
Ta tako a cikin tafiyana kamar na tarwada na zauna a hankali ajiyan zuciya naji ya sauke lokacin dana zauna din hannun shi ya dora sama kafada ya dan karyo kanshi zuwa wuyana yace zarah fada min mafalkin dana samu kina yi dazun dana shiga dakin ki ?
Dagowa nayi na dan kalleshi babu wasa a fuskanshi nace mafalkine kawai dai ba kuma yau ne farkon yin shi duk na kwanta kusan kullun ina wanan mafalkin ko yaushe .
Fada min akan mainene kike mafalkin nace sai nayi shiru na kasa magana yace fada min mana ke nake saurare inji ?
Dama dama sai na kasa fadi yace umhumm dama anty salma ce dai nakan gani tana son wai kasheni.
Tun yaushe kika fara wanan mafalkin ya tambaya kunya naji na kasa magana yace kinga fada min in akwai addu,an da zakiyi sai ki dinga yi don yanayin dama samay ki dazun ya daga min hankali sosai yau.
Dama dai ba wani abu bane sherin mafalkine kawai yaya ganin ta nake wai zata kasheni sai kuma wani lokaci zata jefani a rami.
Nace tun yaushe kika fara tambayan danayi maki ke nan yanzu ai ko ?
Ya fadi yana dagowa daga kafadana tare da tsura min idanuwan shi akaina nace tun lokacin daka fara saduwa dani na karasa a hankali.
Sai naga

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login