Showing 354001 words to 357000 words out of 419207 words

Chapter 119 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1497

kara nauyi.
Ina jinsa ban yi magana ba shima bai jira na bashi amsa ba yace zanso ki hada da kayan yarinyar nan fauziya da maria don an dade ba a sai mata kaya ba tun tafiyan mu gida.
Sai yanzu na gane nufin shi na fita da yaran da yayi dazun don ya sawo masu suturu ne ya fita dasu kasancewa ranan weekend ne.
Zan duba ida na samu lokaci sai mu fita tare dasu na bashi amsa ina gyara kwanciyana.
Nasan halin shi baya daga min kafa idan muna tare ranan ma kokarin lalabata yakeyi sai nace banjin dadin jikina tun rana nake jin marata yana min ciwo.
Shine samun saukina dashi ranan amma idan ba haka ba komai bacin randa yake ciki bai hana shi sauke laluran shi gareni.
Kwana biyu yayi a gidan mu kamar yadda yake a sharia muna zaune bayan karfe biyar sai gashi ya fito yana gyara agogon hannu shi yana fadin zanje wancan gidan.
Ko bai fadi ba nagane gidan merry yake nufi zai tafi lokacin Allah bamu alheri na iya fada a fili na kawar da kai.
Bai shigo gidan mu ba washe gari ga yaran suna tambayana yayi tafiyane nace masu eh baya garine.
Hakan ya dan sa zuciyana kara jin babu dadi da zamana a gida yafi mun wanan zaman nake gani a yanzu da a gida muke zanyi baki koni kaina i fita zuwa unguwa.
Ranan daya dawo duk yadda naso in boye bacin raina kan shere mu dayayi kwana biyu yana gari na kasa boye hakan gareshi.
Don yana magana da kyat nake iya budan baki ina bashi amsa karshema ya sherini kawai ya kama harkokin gaban shi.
Yana zama wayan shi yai kara ya dauka jin ya ambaci mama yasa na dan dago kaina na kalleshi kadan.
Bayan sun gaisa naji yayi shiru yana sauraren wayan kafin ya mike yana fadin idan ta haihu din ai zan bugo makune mama wallahi bata haihu ba sai wanan watan da zai tsaya idan Allah ya kaimu.
Yana fita falon yake fadin haka zuciyana ya ban don auren yarsu hjy ke tambayan idan na haihu badai don kulawa ba kam.
Ya jima bai shigo ciki ba har lokacin dana bar falon zuwa dakina don ban iya kara jimirin zama falin lokacin.
Bayan na gama komai na kwanta zuciyana ba dadi gareni sai faman tunane da nakeyi barkatai a raina kan hjy dashi yadda za a kwashe nan gaba ga zaman mu.
Ni tsorona shine kada hjy ta aura mashi yar uwanshi ta saka ya fita batuna nida yaran don yarsu.
Inzo ina ganin wullakanci don kudirin ta ke nan kawai a kaina yasa ta matsa da sai yayi wanan auren data lakaka mai yanzu.
Duk da banda niyar zuwa wirin shi haka bai hanani shafe jikina da lotion ba da kamshi a jikina kamar yadda na saba yi kullun koda baya gari hakan yanzu ya zama min dabi,ata.
Jin motsin an shigo dakin yasa na dago kai ina kallin wanda ya shigo min dakin.
Shine yana saye da dan three quarter da farar singileti a jikin shi ya nufo bakin gado inda nake kwance yana fadin.
Lafiya kike kikai saurin shiga barci yau lafiyata kalau ina dai son kadaicewa ne kawai na bashi amsa.
Zama yayi bakin gadon yana fadin zancen haihuwan ki mam ke tambayana kokin haihu ban fada masu ba.
Yaya ko ban haihu ba zaku iya yin bukin ku ai tunda sun damu in haihu kuyi bukin .
Murmushi ya danyi yana fadin naki tunanen ke nan kuma don ta tambaya ?
Kuka na fashe dashi ina fadin laifina guda yanzu wurin hjy don ina auren ka yaya da ban auren ka duk wanan kiyayyan da bai kai haka ba tsakani da ita sai dai ya tsaya iya su da mamu.
Zahra me yasa haka kina a wanan halin kike kokarin daga min hanka kan maganan da bashi ba a kullun.
Yaya dole hankalina ya daga da duk wani mai kaunata ina a wanan halin kuma ba,a barni na huta ba sai kokarin akeyi aga durkushewana ko yaushe.
Idan don auren kane ba hannun hjy a cikin sa hakan bai taba damun rayuwana ko kadan don ba,a kaina zata zauna ba idan ta shigo.
Amma kirkiri hjyn ku ke nuna min cewa tafi bukatan zaman ka da yar uwanka dani .
Ni dai rokona gare ka shine kada ka wullakanta ni kana rawan kafa yadda akeson kaimin don samu sabon wuri ni yanzu mai tsohon wuri a wullakantani yadda akeso a ga kayi min.
Magana ta ba karamin dariya taso bashi ba saidai ya daure kamar bai fahinci mai nake nufi ba ga zance na.
Zahra yaushe kika zama hakane wai ban sani ba duk kinbi kin daga hankalin ki a banza kan wani magana da baida tushe can.
Wani rawan kafa kikags inayi kan mace da zaki fara tunhumana kan wata can tun bata shigo ba.
Ke kinfi kowa sanin wanan auren zanyi shine don cika umurni kawai ba don son raina ki koyi hakkuri kina danne fushin ki tunda har kin san da manufa aka sharada min auren nan.
Kuka naci gaba dashi ins sauraren yana fadin wanan halin da kika dauko hakkuri ya kusa karewa a kanshi ina daga maki kafane don halin da kike ciki ba don komai ba.
Idan sakarcin ki ya kaiki kika bada wani kafa da za,a sameki wanan kuma ke kika jiyo don't blamed me yana fadin hakan ya tashin ya fita daga dakin.
Washe gari ina daki naji sako ya shigo min a wayana ban duba ba sai dana gama abunda nakeyi kudine ya turo min masu yawa na sayayyan da zanyi lokacin.
Tambayan kaina nayi ni mai zan saye kuma kayan yarana ma wasu banyi amfani dasu ba.
Koda na fito ya fita kai yaran shi makaranta sai maria me ke gyaran gidan lokacin .
Mun gaisa da ita take fada min sun fita shida yaran ya kaisu makaranta.
Na dauka da yai muna kwana biyu gidan zai koma gidan merry ne kamar yadda yayi a baya sai naga sabanin hakan.
Haka yasa na gane merry bata garin kenan ta koma inda ta fito shima kwana biyu yayi tafiyan da yace zaiyi din.
Mun fita gaba dayan mu zuwa sayayya mun sayo kaya mai yawa kamar ban taba kudin ba daya ban .
Har watan haihuwana ya kama a lokacin ya dawo ya dawo da sati a wani dare na kuda ya kamani muka tafi asibiti abin mamaki sai gashi na kasa haihuwa kuma da kaina.
Saida aka kara yi min aiki ake cire min yaro a cikina wanan dana haifa duk yafi sauran yaran kyau da girman jiki.
Tuni wanan haihuwan ya mantar damu wani zancen kishiya can da muke badakala akai kowa hankalin shi a tashe sai yake ganin kamar zan mutu ne don wahalan da nasha a wanan haihuwan.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
17/11/2021, 07:20 - ??5惙5惙5?: Sai washe gari na dan san a inda nake a hankali na dan bude idanuwana da sukai min nauyi saboda wahala ina karewa dakin da nake kwance a ciki wanda babu motsin komai saina na,uran dakin dake aiki a lokaci.
Sannu a hankali na gane a inda nake kwance dakin asibiti ne kokarin daga hannuna nayi ina shafan cikin jikina sai naji wayau.
Hakan yasa na gane aikin aka sake min wanan karon ma ke nan shike nan ya tabbata ba zan iya haihuwa da kaina ba kenan ko me ?
Turo kofa akayi alaman wani zai shigo dakin ke nan lokacin haka yasa na dan mayar da hankalina ga kofan.
Nurse sai yaya dake bayan ta dauke da yaron a cikin showel ya rugume shi a jikin shi.
Suna kallona nurse din ke fadin thank god ta tashi ma before time din ya cika da sauri yaya ya matso bakin gadon yana min sannu da jiki na amsa mai da kai kawai.
Bayan hakan na dan kara lumshe idanuwa yace bude ido kiga baby din ki zahra namiji kika kara haifo muna wanan karon kuma.
Dan murmushi nayi ina bude idon nake kallon su shida yaron daya karkato min shi yadda zan ganshi da kyau daidai fuskana.
Zahra kinganshi kece ya biyo sak a kyau da fari ba ta inda wanan ya roki har yafi sultana kwaso kamanin ki sosai.
Dan murmushin na sake yi ina rufe idona daga kallon yaron ba tare danayi magana ba.
Nurse din ne ke fafin alluran bai gama sake jikina ba har yanzu su barni har nan da zuwa anjima idan na falka.
Ban kara sanin kaina ba sai goma na dare lokacin na tashi da wani irin matsakaicin yunwa lokaci guda.
Kokarin tashi zaune nakeyi naji muryan maria a kusa dani tana min sannu madam ya jikin nace da sauki maria sannu da kokari ashe kina nan ke nan tace eh oga ya koma gida don yara yace in zauna a nan.
Zaune nakai ina fadin maria yunwa nake ji sosai da sauri tace me zakici madam tea kawai zansha na bata amsa.
Da sauri maria ta tashi ta hada min tea mai kauri ta miko min a inda nake zaune tana kara yi min sannu har lokacin.
Na amsa sai nake fadin ba zan iya sha ba ban wanke bakina ba maria da sauri ta karbi tea din a hannu na ta aje tana kokarin mikar dani tsaya nace ta bari zan iya ai
Saida na wanko bakin na dawo na zauna na dan kurbi ruwan tea ban wani sha sosai na miko mata cup din da sauri ta karba ta aje gefe.
Ban kwanta ba don na gaji da kwanciyan tace madam kina da sa,an haihuwa yaran ki duka masu kyau kamar ku wanan har yaso yafi twins kyau???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? sosai.
Oga yana ta murna sai bugama yan uwan ki waya yakeyi kin haihu murmushi nayi don jin abinda take fadi a raina kuwa cewa nayi wata kila ya gyara halinsa ne yanzu.
Ko kuma ya bugane don asan na haihu don su fara shirin bukin su da suke jiran sai idan na haihu din suyi kamar yadda ya roka a bari har na haihu ayi.
Tabe baki nayi da wanan tunanen yazo min a rai nace maria yaron yana lafiya ko tace lafiya yake sosai madam kullun sai an kawo shi nan ya dan sha dumin jikin ki.
Duk hiran da take min sai dan murmushi kawai nake iya mata a lokacin saboda yanayin jikin da nakeji ba dadi.
Kwana daya na kara aka sallameni daga asibitin bayan sunga na samu lafiya muka koma gida a gida duk wani kula da gidan yana kan maria da fauziya.
Don ni ko falon bana fitowa ina daki ko wani lokaci don yanayin jikin nawa inda muke samun yan barka jefi jefi yan kasan mu da muke hurda dasu can suna shigowa barkan samun karuwan mu.
Ina da sati daya da dawowa asibiti kwatsam saiga Nafisa a garin kamar daga sama don bai fada min zuwan ta ba.
Ban yarda na nuna komai garesu daga shi har ita kawai dai na mata taro yadda ya dace aiwa bako idan yazo kamar babu komai a tsakanin mu dama.
Zuwan ta yasa nake dan fitowa falo yanzu muna zaune muna hira take fada min aida hjyn su suka so zuwa saidai saboda zancen bukin yaya da za, ayi kwanan yasa basu zo tare ba.
Ban yarda na nuna mata ko wani re,action ga maganan ba sai cewa da nayi gaskiya kan dole sai hjy tana kusa zaifi.
Ta kara fadin ai mun dauka zaku zo sai yaya ke fadin sai kin kara jin sauki zaku shigo gaba dayan ku.
Don shinema hjy tace ai in shirya inzo tunda ita ba zata samu zuwan ba kuma nace kin ko kyauta muna aida kikazo don ba wanda ya taba zuwa wurin mu sai yaya Aliyu koshi sau daya yazo kasan nan.
Zaman mu ba wani matsala ina sati biyu cif da haihuwane ranan da dare hjy ta kira yayaa waya tana fadin Nafisa ta iso lafiya ko don naji baka kirani ba sai kuma zancen auren ka yaya najika shiru lokaci yana kara karatowa.
Yace da wuri haka mama tace a fusace a wurin kane yake da wuri kada ka mayar dani wata bi can nina haifaka bakai ka haufeni ba umurni na baka dole kazo don karshen satin nan ne daurin aure.
Don yanzu haka har an fara sha,anin buki kazo ko kada kazo yanzu ya rage naka kuma aure dai ba fashi na fadamaka.
Amma mama har yaushe Zahra ta haihu haihuwan nan kuma fa kinsan aiki akai mata da za, ace na tsira buki yanzu ko suna bamuyi ba na yarin anan suna kawai aka rada mashi.
Fatimar tafi wanan da taketa jiran kane bukatan ka kome na fadama wanan karon ba zan daga wanan ranan ba.
Tana fadin haka ta kashe wayan ta tana huci shima kanshi ya dafe yana fadin innalillahi a fili.
Sharan kiran Amma yayi koda abinda zata taimaka mashi a daga wanan auren har zuwa wani lokaci nan gaba.
Amma na daukan wayan sun gaisa yake fadin Amma kinji fitinan da mama ke shirin jefani kuma a ciki yanzu ta kirani wai daurin aurena karshen wanan satin za,a daura.
Yanzu mai mama take kokarin yi min a rayuwana ya take inyi da yar mutane da nake jinyar ta a nan ?
Amma tace cikin yanayin damuwa muma haka wanan zancen yazo muna dazun nan mahaifin ku yake sheda muna zancen wai ashe bukin ya tashi.
Kayi hakkuri tunda haka shine farin cikin uwarka aure in anyishi a tafarkin Allah ai alherine sadauki.
Indai da zuciya daya sukai wanan hadin Allah yasa hakan shi yafi zama alheri ga rayuwan ku ga baki daya.
Idan kuma bada zuciya daya ake shirin yinsa ba don wani kudiri nasune, Allah ya tarwatsa aniyar su.
Ka kwatar da hankalin ka kai mata biyayya yadda sharia ya tanada muna tsaye gareku da addua akoyaushe insha Allahu sai alheri aruyuwan ku kaida iyalin ka.
Yace yanzu Amma matsalan ai shine yadda zan tunkari Zahra da wanan zancen tana fama da kanta duk a sanadin haifar min yaro datayi.
Kada ka zamo umar din mata mana mai sunan ka da jarumta akasan shi ko a inane kuwa balle kaida matar ka.
Yace Amma na gode don dole yau in fada mata saboda kwana biyu kawai ya rage min ke nan in zo Nigerian.
Amma tace hakana zaka daure ka fada mata Fatima inba ta canza ba zata fahince ka ai yace Amma na gode Allah ya shige muna gaba tace Amin ya kashe wayan.

Saida ya gama duk abinda yakeyi ya shigo dakina ina zaune rugume da Abbana don sunan mahaifina Abubakar ya sakawa yaron.
Muna kiran shi da daddy yayi sallama na dago ina amsa mashi ya tako har zuwa inda muke yana lakatan bakin yaron dake zukan nono hankali kwance.
Fauziyace ta mike da sauri zata bar dakin yake fadin aida kin zauna abinki ba dadewa zanyi ba bata dai tsaya ba ta fice daga dakin kawai.
Zama yayi dab da inda nake zaune yana fadin wanan kamahin fa haka yana kai hannunshi don karban yaron a hannuna.
Murmushi nayi kawai banyi magana ba a lokacin yace zan shiga Nageria zuwa jibi zahra don mama ta kirani dazun da magariban nan nadai yake fada min wai zancen bukin shi ya taso zai tafi Nigeria ayi bukin.
Allah sanya alheri na fadi ina kokarin dauko abu bakin gadona yadda na bashi amsan kai tsaye ya tsaya yana karemun kallo da mamaki a fuskan shi.
Na juyo ina fadin munyi waya da mamu tace zatazo kafin ta koma gida ba wani nuna damuwa a fuskana yadda ya zata nake magana na freely dashi.
Yace har yanzu ashe bata koma gida ba nace ko yanzu ina ganin ba maza ba don ko zata koma ina ga ba,a wanan gida na kawu zata zauna ba don tace gidan da zata koma ana gyaran shi a yanzu haka.
Kara mayar da hankalin shi yayi wurina sosai yana mamakin abindana fada nace eh iyayyen ta wai sun turo an saya mata gida kano tace unguwa dayane dana kawu a nan cikin old GRA ne gidan yake.
Amma ina ganin ko daddy baisan da wanan zance ba balle mama yake tambayana nace wallahi ban sani ba yaya.
Yaji dadin yadda yaga ban nuna damuwana da auren shi ba a yanzu tun bayan dawowana asibiti ban kara tayar da wanan zancen ba muna zaman mu dashi lifiya yana kuma bamu kulawan daya dace mu samu a wurin shi.
Don haka na tatara zancen na watsar a raina bayan zurfin tunanen da nayi tun zuwan merry gidan mu naji kalaman bakin yaya din naba kaina lafiya.

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login