Showing 288001 words to 291000 words out of 419207 words

Chapter 97 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1430

rike yana dan matsawa a hankali zuciyar shi cike da kunci a lokacin shi kadai yasan irin yanayin da yake ji a lokacin.
Likitace ta shigo tare da wasu nurse a bayan ta shigowan shi yasa ya daga daga yadda yake zaune tare dani.
Dubani tayi tare da yan tambayoyi tana rubutu kafin tace dani in mike zaune zan iya ko da sauri yaya yaso magana ta tare shi da hannu.
Da taimakon nurse din na samu na daga, daga kwace har lokacin jikin nawa akwai dan tsami kadan tace in sauka daga sama gadon na sauka a hankali.
Tare da dan umurtana in taka da tsoro na fara dan takawa sai najini wasai dani ba yadda nake tsanmani ba.
Shi kanshi yaya yayi mamakin hakan wanda hakan yasa shi dan murmusawa yayi yana mai jin dadu har cikin ranshi.
Likitan tace zasu sallame ni zuwa safe idan sunga yadda jikin nawa ya kara sauki suka fita bayan ta umarceni da in zauna kada in kwanta kuma.
Daga inda nake zaune ya koma bakin gadon ya zauna ya tsura min ido a hankali ya kira sunana bayan ya sauke wani nauyayyen ajiyan zuciya yace Zahra.
Na dago kai a hankali na kalle shi cikin yanayin ciwo da nauyin jiki yace kin san may kika haifa min ?
Kaina girgiza mai a hankali alaman a,a yace cikin daga yan yatsun hannu shi biyu yara biyu maza kika haifa Zahra.
A zatona wasa yake min sai na dan murmusa kawai shigowan su Ramla da mijin ta yasa muka katse maganan mu.
Da murnan su na gani zaune suka shigo suna muna ba,a yanzu kan hankalin shi zai kwanta tunda yaga na farfado ban mutu ba.
Sai dan murmushi yake sakewa kawai a fuskan shi sun dade wurina kafin su fita tare dashi zuwa ganin babeis din.
Washe gari aka sallamay ni daga asibitin kamar yadda likitan ta fada a zatona gidan su Ramla zamu nufa sai naga an dauki hanyar wata unguwana daban wanda ke unguwar sarauniyar kasan england.
Daga gidajen zaka iya hango gine ginen masarautan daga can nesa kadan gidane wanda ya amsa sunan gida ko a can maigirma gidan yakai abin kallo.
An ma gidan kwaliya irin na al,adan turawa da furanni masu launi kalan fari da pink gwanin ban sha,awa.
A hankali nake takawa bayan na fito daga cikin motan ina karewa gidan kallo da mamakin nan kuma inane aka kawoni kuma ?.
Daidai shiga gidan an yi rubutu da flowers wellcome to new world dan dagowa nayi na kalli yaya dake rike da hannuna zuwa cikin gidan.
Mamaki bai gama kasheni ba saida naga photo na dashi sai na yan yaran kamar ayi magana mu fito fili.
Wani dadine ya kamani har kasan zuciyana wanda ba zan iya musultashi ba a lokacin da taimakon anty Ramla ne ta kaini har dakin da yake mallakina bin dakin nayi da kallo ina mamaki wanda har ban iya boyewa a lokacin.
Rayuwa ke nan Ramla tace min idan baka mutu ba ba,a gama hallitan ka ba mijin ki ba karamin so yake maki ba Zahra.
Yanzune lokacin da zaki kara zage damtse ki kara kama mijin ki a hannun ki.
Kada ki bari haihuwa ya rageki da komai ga mijin ki son shi dana yaran ki zaki auna ki kara akan komai a rayuwan ki.
Tsabta ya ganki yanzu zarah idan da kinayi yanzu ki kara ninkin baninki samada wanda kike dashi a baya.
Mun kai wani lokaci tana ban shawara kafin mijin ta yace tafito su wuce zuwa gida nan suka tafi suka barmu daga mu sai mu yaran a gefena na juya na kalle su ina mamakin wai a cikin cikina suka fito dukkan su.
Shine ya shigo dakin bayan ya dawo daga masu rakiya daga kofa ya tsaya yana kare muna kallo.
Dago kai nayi na dan kalleshi daga inda nake kishingide ya tako zuwa bakin gadon ya zauna a hankali tare da riko hannayena yace zahra may zance dake ne wai.
Sai ya dan rugumoni zuwa jikin shi yana fadin kin gama min komai a rayuwana ko haka kika barni da yaran nan biyu na godewa Allah a rayuwana.
Zai kara magana nayi saurin rufe mashi baki da hannuna ina fadin please yaya don Allah ka bar wanan zancen don Allah.
Ajiyan zuciya ya sauke mun dauki lokaci a hakan kafin dayan yaron ya motsa yayi saurin sake ni ya juya gare shi da sauri yana fadin ko nono yake so ne Zahra.
Yana kallona yake magana dan langabe kai nayi nace mai yaya yaya zanyi yanzu ?
Kokari bude gaban rigana ya shiga yi ya fitar da nono ya juya ya dauko yaron da kanshi ya kama yaron saida yasha nonon ina runtse idanuwa yaron yana ja.
Kulawa sosai dagani har yaran muke samu daga gare shi bai bari in yi komai har yaran shike masu komai da kanshi.
Jina shiru an koma school Anty farida ta shiga neman layin wayana tazo gidana yafi a kirga karshe wasu turawa ta samu a ciki suke fada mata munbar gidan.
Luckly ta kira layina ya shiga ina zaune ya tasani a gaba ina cin abinci saiga kira ya shigo min na dauka tace Fatima ina kika shige haka tsawon wanan lokaci haka ?
Naje gidan ki ban samayki ba sai wasu na samu a gidan sukace basu san ki ba.
Nace cikin cool voice anty na mun canza gidane kuma na haihu tace kin haihu ban sani ba fatima yaushe kika haihu nace two weeks ago.
Amma baki da kirki fatima ina garin nan baki sanar dani kin haihu ba yanzu kuna inane gani nan zuwa.
Kallon yaya nayi yana jin duk abinda muke fada sunan unguwan da kwatancen gidan yai mata bayan ya karbi wayan a hannu na.
Zuwanta yai min dadi sosai don itace ta samo min wata bakar fata mace saidai yar ghanace da zata dan zauna tare dani.
Hakan ba karamin dadi yai muna ba taban kulawa sosai tankar yar uwatace ta jini da ita da Ramla banda abinda zance dasu.
Don sun min karamci sosai a rayuwana wanda bazan iya godiyan baki a garesu ba saidai addu, a.
Ban san da zancen zuwan wani daga kwatsam naga Addah na sun shigo gidan tare dashi saida naji wani iri a rayuwana.
Don kamar a mafalki naga Addah tana shigowa maimakon inyi murnan ganin ta sai kawai na fashe da kuka yana tsaye yana kallon mu.
Tausayi na bashi don yasan kukan da nakeyi bana komai bane saina farin ciki ganin na gids yau a idona.
Sosai naji dadin zuwan Addah na don dagani har shi mun kara samun hutu sosai da zuwan ta ga maria mai kula da wasu abubuwa a gidan ga Addah.
Haka ya bashi daman fara fita wurin aiki nima hakana na fara zuwa makaranta daukan darasi anyi bukin suna irin namu na nan hausa.
Inda duk gaiyan na Ramla ne da Anty Farida mundai dan cika gidan inda yaran sukaci sunaye Abdulrahaman da Abdulsalam.
Zabin sunayen da mahaifinsu yai masu ke nan kuma dashi sukazo duk sunan da yaro yaci dashi yazo duniya.
Ina jin dadin zama sosai da Addah wace take yar uwa a gurin mahaifina ba karamin karama min dangina naga yayi ba ga hakan.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:31 - ??5惙5惙5?: BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHAHIM MALIK YUMMUDEEN, , , , ,

A cikin amincin Allah yarana suke wani irin girma zakace kamar wani abin girma ake basu lokacin.
Kula sosai suke samu daga mahaifinsu da Addah da maria nawa dasu nono kawai idan na dawo in dan basu su sha sai kuma idan zasu kwanta in kara masu.
Bazakace wai nice ma na haifesu ba idan ba an fadama ba don uban ya fini kula da yaran don hakane ma sukafi shakuwa dashi fiye dani.
Don idan yana gida gaba daya shine mai masu komai ko Addah dake zaune damu lokacin tana hutawane saidai abinda ba,a rasa ba.
Na murje na zama kamar wata queen dani wayewa sosai ya zo min duk da haka ban yarda na bar al,aduna ba.
Ina bisa umurnin shi da dokan shi karatu yana tafiya a yadda yake so don akwaini da kokari sosai a fanin karatuna.
Yarana suna da shekara daya da wata bakwai na fahinci ina dauke da wani cikin duk da yaran suna saman kafarsu har an fara kaisu daycare suna dan daukan darasi.
Hankalina ya tashi sosai akan cikin dana gane ina dauke dashi lokacin yaya bai gari yayi tafiya sati uku.
Nasha wahalan cikin sosai wanan karon ba kamar cikin farko da aka ban sadakan shi ba wanan amai da kasala da yan ciwarwuka yake sakar min.
Har abin yaso ya shafi karatuna ga shi yanzu muna matakin karshe in zama likitan mata da matsalolin su don shi yaya ya zaba min.
Haka ya dawo ya sameni a cikin wani hali bai huta ba duk da naje asibitin bai yarda da zuwa naba ya daukeni muka garzaya asibitin.
Bayan yan gwaje gwaje aka tabbatar mai da ciki ke jikina na sati bakwai shi kanshi yayi mamakin hakan.
Ganin yadda na tayar da hankalina dole ya rufe nasa ya shiga aikin lalashina kan na kwatar da hankalina wanan ba komai bane ai, kuka kan nayishi sosai a lokacin.
Dole na hakkura na maida hankalina ga karatuna Addah kuma tana kara min karfin gwiwa da ban musalai iri iri wanda hakan ya kara kwantar min da hankalina.
Daga baya na fahinci kamar yaya ya shirya da matar shi don yawan zuwan zuwa America da yakeyi lokacin .
Ko kuma yana garin zaice min ba zai kwana a gidan mu ba zai tafi wancan gida nasa ya kwana.
Ban taba tambayan shi ko nuna mashi bacin raina ba kan hakan kuma ban taba mashi maganan ko sun shirya da matarshine.
Shima kuma tunda nasan ba mutum bane mai yawan magana ko fadar sirin shi da damuwan shi hakan yai masa dadi.
Muna waya sosai da mamu da kawu dasu Amma inda wani lokaci sukan tambayeni waiku har yanzu dai shiru saidai kawai in masu dariya in wayece zancen akan karatu nakeyi ai.
Amma kanyi fada sosai tace karatu zai hanaku aje iyali idan suna waya da Amma mutum yana kusa zaisha dariya sosai a lokacin.
Zuwana England zuwa yaya Nigeria uku bai taba zuwa dani nima ban saka raina ba tunda yace sai na kare karatuna zan tafi gida ban san dalilin shi na fadin hakan ba.
Haihuwana na biyu ma CS akai min aka cire yarinyar a cikina wanan karon kusan ince namafi wancan karon na haihuwan yan biyuna wahala.
Saukin abin Addah tana tare damu don taso komawa gida saboda kewan gida dakan addabi mutum a can.
Da kyat yaya ya lalasheta ta yarda don cikin dake jikina a lokacin da haka har Addah ta zauna damu na sheka biyu da wasu watani a kasan kafin ta dawo gida don hankalin ta ya koma gida ga baki daya lokacin.
Haka rayuwa yaita gudana al,umurah mai kyau da mara kyau suna faru suna wucewa kuma har dai lokacin abindana sani ba kauna tsakani da sarakuwana.
Don a gaba zasuyi waya zata tambayi merry da yar ta bata taba tambayana ba halin da nake ciki.
Shekaran dana kare karatuna a shekaran ne kamar yadda yai min alkawari wata rana kwatsam yaya ya dawo dags tafiya yazo min da maganan zuwa gida.
Ba karamin farin cikin jin hakan nayi ba ban kuma kawo fargaban yadda zamu kwashe idan muje ba a raina ko kadan.
Tun a ranan daya fada min zancen tafiyan tyn wanan ranan na soma shirin zuwa gida duk na fita naga wani abinda ya ban sha,awa zan sayowa kannena da mamu da sauran mutanen gida.
Duk wanan shirin bai san inayin shi ba a bangarena Allah Allah nakeyi watan dayace zamu tafi ya kama kawai in ga kaina a gida cikin yan uwana.
Wani tafiya daya dawo muna zaune naji yace zan baki kudi kuyi sayayan abinda kike bukata wanda zamu tafi dashi gida.
Na dago ina fadin sai dai idan kara masu zanyi don ni tsaraba ban san yadda ma zan dauke shi ba daga nan don tun ranan daka fada min na fara shirina.
Wanan kuma naki ne ki tafi ki sayo wanda nace da kudina azo a hada kayan wuri daya a tura ta ruwa su wuce dashi kafin mu tashi don akwai kayan da nake son za a wuce min dashi a cikin satin nan .
Ba halin inyi mussu dashi dole na karbi kudin daya bani na fita da zuman sayo wani abinda zan kara dashi.
A wanan fitan ne muka hade da wanan matar mai sallon don nayi zuwa barkatai bamu haduwa da ita wai ashe ta tafi libiya ne duk dadewan nan bata nan.
Itace ta shedani don ni ban ganeta ba tunda an dade wanan lokacin ta bukaci in bata address dina da layin wayana kan tana son magana dani wanda bai yuyuwa a nan.
Mukai musayan layi da ita mun rabo nayo sayayya sosai kudin daya bani kamar ban taba ba .
Kwana biyu da haduwan mu da ita sai gata a gidan mu taro sosai nayi mata na karramata.
Bayan mun dan taba hirane take tambayana ko ina da yan uwa dake zaune a libiya nace mata gaskiya ni ban san kowa ba a can.
Tace ban taba jin labarin ina da yan uwa a kasan ba na girgiza mata kai da a,a tayi shiru can ta zaro wayan ta daga cikin jakkan hannun ta ta dan taba sai ta miko min na karba.
Sak da wace ke cikin hoton kamar mu daya kusan kuma shekarun mu daya da mai shi saidai zata dan girmay mun.
Ajiyan zuciya na sauke nace lalai muna da kama sosai tace shiyasa ta matsa min da tambaya tace inje gaba in duba akwai wasu photuna na family din su.
Kallo nake cikin nazari sosai don kamannin yan cikin photon da nake gani da mu sosai.
Tace a Nigeria kowa naki yake nace eh kowa nawa yana nan kasan tayi shiru can nace saidai mamata nakan ji ana fadin babbarta ba yar Nigeria bace ita kuma tun da ta tafi ta barta a zanin goyo har yau basu kara ganin juna da ita ba.
Da sauri tace min ko zaki bani photon maman naki ingani don Allah ?
Na neme photo mamu na nuna mata a wayana wanda nayi zoming ta tsurawa photon ido sosai sai ga hawaye yana fita daga idon ta.
Kallon mamaki nake mata tace wanan yar yarmu ce data bari a Nigeria ko tantama ba zanyi ba yar uwar muce wanan.
Yar uwarku na tambaya ina mamaki tace kwarai wanan kamar haka ba zai tafi a banza ba saida dalilina jini mai karfi
Ko zaki iya kira min mahaifiyar taki a waya yanzu muyi magana nace zan gwada in gani ko layin ta zai shiga.
Sai akai rashin sa,a layin yaki shiga haka yasa na bata layin mamu akan zata kirata suji idan itace.
Ta tafi ta barni cikin halin damuwa da tunane tare da fargaba cike a zuciyata sai bayan tafiyan tane yaya ya dawo gidan nake labarta mai zuwan matar.
A ina kika hadu da ita ya tambaye yana kallona a cikin mamaki nace a shagon ta mukaje gyaran kai da anty Ramla ranan tun ina da cikin su Abdulrahaman na bashi amsa.
Duk wanan dadewan baku hadu ba sai yanzun kuma na bashi amsa da eh sai shekaran jiya muka hadu a shago wurin sayayyan danaje.
Shiru yayi na dan lokaci yana nazari yace gashi kuma jibine tafiyan mu banda lokaci da sai mu ziyarce ta in karajin wani bayani a gurin ta.
Yanzu sai idan Allah ya dawo damu lafiya zamu neme ta Allah ya kaimu kawai na iya furta mashi lokacin don yanayi sai ina jin shi wani iri.
Komai da zamu tafi dashi ya tura gida ta jirgin ruwa sai wanda mukafi bukata da zamu tafi dashi tare damu.

NIGERIA LAGOS, , ,

Karfe bakwai na safe muka sauka Nigeria ta birnin ikko jirgin mu ya sauka nayi mamakin ganin wai yaya yana da gida a garin.
Maria ta biyo don dama kudi taje nema a can kuma ta samu yaya na bata hakkin ta yadda ya kamata.
Wanan yasa tace ba zamu barta ba a can dama tana son zuwa taga gida daga nan hakan yasa mukazo tare da ita kan sai munje kano tare taga wuri zata dawo ta tafi gida.
Ina jin dadin zama da maria sosai don bata da matsalan komai ta ko ina don hakane zaman namu ya

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login