Showing 348001 words to 351000 words out of 419207 words

Chapter 117 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1421

ruwa da abinci ta kawo min gabana wai inci.
Dago kai nayi na kalleta sai lokacin na dan sake murmushi kada yarinyar ta daga hankalin ta akaina.
Ruwan na dauka na dan kwankwada na aje kofin ina lumshe idanuwana tare da bin kujera na kwanta har lokacin na kasa aje magana daya a kan zancen da yau salma take fada min din na tabbacin zancen karin auren yaya din.
Bayan kwana biyu ya sauka kasan bai samu zuwa wurin mu sai washe gari da yamma ya shigo gidan hakan kuma ya bani tabbacin gane merry tana kasan ke nan.
Ya shigo gidan daidai yaran na gidan sun dawo da murna suka tare shi sultana ta sheko zuwa dakina tanayi min albishir din dawowan daddy nasu nace naji kawai.
Ya gama da yaran a falo har lokacin ban fito zuwa taron shi ba ina dakina kwance na lumshe idona.
Can naji ya murda kofana ya shigo daga kofa ya tsaya yana kare min kallo ni kuma har lokacin ban dogo kai na kalleshi ba.
Sai da naji motsin shi zuwa inda nake kwance na dan bude idanuwana da sauri nace sannu da zuwa a kasalance ya bini da kallon yadda na tare shi yana mamakina a ranshi.
Bai amsa min gaisuwan ba yace meya sameki ko baki da lafiyane kuma yana tambayana tare da kokarin taba jikina yaji.
Lafiyata kalau na bashi amsa kawai ina kokarin tashi zaune ya hanya na kara fadi.
Tambayan ki nake kina kin bani amsa meke damun ki ne na ganki haka kamar mara lafiya ?
Lafiyata kalau sai dai idan za a lakaka min ciwon dai a yanzu kallon mamaki ya bini dashi yana fadin wani irin magana ne wanan kuma kike fada min.
Ai ba,a damu dani ba tunda ana ganina banda galihu tunda mahaifina baya raye kamar na kowa dole azo nan a yardani kamar banza.
You are very stupid da wanan magana da kike min zahra daga dawowana zaki tareni da wani shirmen magana taki mara dadi haka.
Ya mike ya fita a fusace ya bar dakin rai bace bai sake shigowa ba nima ban fita ba ina dakina kwance a lokacin ban leko falon ba.
Yayi wanka yana cikin shirin shi da alama fita zaiyi a lokacin fuskan shi a daure yace ni zan tafi merry na gari nazo duba kune dama.
Ban tanka mashi ba ya juya ya fita abinshi ya bar dakin cikin tafiyan shi mai kama da kasaita sai daya dan jima naji tashin motar shi a lokaci.
Haka na kwana ina hadiyan zuciya dagani sai yarana da maria a gidan don ko washe gari bai shigo gidan ba sai da dare lokacin har yara sunyi barci ya shigo gidan.
Ban san ma shigowan shi gidan ba don haka na wuni akwance sai maria ne ranan take komai a gidan don a zaton ta banda lafiyane ni.
Kofana ya murda yaji ta a rufe ya fara kiran sunana ina jin shi ban amsa mashi ba ya kara cewa dani ki bude kofa nace cikin tsawa jin tsoron shi da nake har yanzu yasa na mike na bude kofan lokacin.
Wanan wani hali kuma kika dauko na kule kofa da key banyi magana ba na juya in koma bakin gado naji ya rikeni yana fadin.
Wai wanan wani hali kika daukone hakane zahra ban fa gane maki ba zahra tun dawowana garin nan.
Ka tambayi yar uwanka da kake boye min auren ta don a yaudareni ne aka turoni nan aka barni da yara ai da ka sani baka turoni nan ba don ba zan tareka da komai ga auren ka ba.
Hakan baiyi ba sai da kazo ka watsar damu kamar mu ba mutane bane a nan ka shigo garin nan yaya baka damu ka fara zuwa nan kaga lafiyan mu ba sai ka tsaya wurin merry da yarta.
Zama yayi bakin gado yana murmushi yace har an samu wanda ya kwarmata maki wanan zancen tun daga Nigeria har nan duk taka tsam,tsam da nake kada kiji ?
Ban tanka shi ba don haushin da nake ji a raina a kwana kin nan yasa na kyaleshi kawai bayi magana ba.
Karamin filon dake gefen shi ya jawo ya rugume a jikin shi yai shiru har wani lokaci na bashi baya yana zaune sai ajiyan zuciyana yakeji daga inda yake zaune.
Bai taba tunanen ina da zafin kishi haka ba don ban taba nuna mai kwatankwacin halin dana nuna mai ba wanan karon.
Sai ya danganta abinda harda laluran cikin dake jikina ya hademin jin zafin don ace zuciya sai mace mai tsohon ciki dama.
Baiso inji wanan zancen ba a yanzu sai idan na haihu shi da kansa zaimin bayani yadda zamu fahinci juna don shi kanshi auren biyayya ga mahaifiyar shi zaiyi yanzu bawai don so ko kaunar auren ba.
Sai gashi wani da bai sani ba ya bata mashi tsarin shi ya kwaramata min zancen a lokacin dabai so hakaba gareni.
Yanzu kallon mayaudari nake mashi wanda ke shirin ha,intana ko cin amana nakenan na dauke shi.
Can naji ya gyara kwanciyar shi still dai dakin shiru yayi ba wanda ya iya magana a cikin mu a hankali kuma yaji sheshekan kukan da ya fara zo min a lokacin.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
17/11/2021, 07:18 - ??5惙5惙5?: A hankali na sauka daga kan gadon na wuce bathroom nayi alwala na fito har lokacin bai falka daga dan barcin daya samu?????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? ya dauke shi ba don ya kwana da tunane a ranshi.
Mata biyu ke nan bai iya da halin su ba inaga kuma ya kara na uku yanzu wace ba bakin arzikin dayaji yabon ta a gurin su.
Ya bar gidan merry data zo bukin yar uwanta tun yana Nigeria ta ishe shi da kira saida ya dawo akan dole da fitina da komai sai da yazo wurinta karshe ma kuma suka kare da fitina don yanzu yar tsarguwa ya rigada ya shiga tsakanin su ko.
Komai yai mata sai taga rashin kyautawan shi gare ta zatace don ya aure illiterated din yar uwan shi yake kokarin wullakanta ta yanzu.
Har ya kai ga fada mata wanan din data raina tafita da komai yanzu gareshi don tasan kimar shi da darajan shi tare dana yan uwan shi.
Ran merry ya baci da wanan kalamin nasa sosai tace dama an fada mata su musulmai basu da tabbas ai gashi ko ya fara nuna mata hakan.
Saida sukayi tsiya tsiya dashi yabar mata gidan rai a bace ya nufo wanan gidan namu .
Sai gashi yazo ya samu wani fitinan dake shirin taso mashi kuma wanda yake ganin zaifi na merry idan bai dauki mataki a kan hakan ba.
Ashe gaskiyane da akace mace ba abin yabo bane sai idan an mata kishiya bata tada hankalin ta ba za a yabeta.
Ina abin tayar da hankali akan wanan auren da yake shirin yi yanzu yarinyar da sau daya ma ya ganta kuma a duhu don samun su tayi zasu tafi bayan sun gama ganawa da mahaifin ta da mama ta tursasa mai yaje ko ta saba mai .
Hakan yasa dole ya shirya shi da Nasir da Aliyu suka tafi akai magana suka bada komai.
Allah ya gani zaima mamane biyayyan haihuwa kawai don ya gane auren shine salama a gare shi don a zauna lafiya.
Ina za,a hada zahra da sauran matan shi don dai kawai halin mata da basu raina abin kishi har may wanan mai zubin mayunwatar daya gani zata ja da zarah ne ?
Koda ya aure ta baiji zai iya zuwa da ita ko ina ba bayan Nigeria shiyasa tun farko ya fadawa mahaifiyar shi wanan magana akan ta sani ba zai fita da yarinyar ko ina ba idan ta yarda zata zauna a Nigeria shike nan .
Suka yarda da wanan sharadin nasa don su bukatan su kawai ace anyi wanan auren su shiga cikin rigar arzikin su suma a dama dasu kawai.
Nan hjy ta kawo zancen Fauziya da taji mun tafi da ita daga baya tana fadin zakace ba zaka iya kai yar yaruwata inda kake ba.
Amma ka iya daukan diyan maimun har biyu don ka inganta masu nasu rayuwan suci gaba wanan ba maganan da zai yuyu bane yadda kakai wanan yar matsiyatan itama ya zama dole ka kai wanan din can .
Habibb yace ki gyara zancen k mamai don yanzu sun wuce akirasu ahalin tsiya kamar yadda kuke kira masu a baya.
Don kowa yaga arziki yanzu a tare dasu har sun zartamu don shi wanda uwar maman twinces ke aure ake sa ran shugabancin kasan nan gaba.
Saida na bincika naji komai nasu a kasan ita kanta uwar wata babban ma,aikaciyace a kasan basu da alfaharine kawai yasa baku san wanan ba yanzu haka idan kin shiga kinyi saching din sunan shi zakiga komai masu in deteils.
Arzikin su na banza da wofi tunda danashi suka fara karya a gidan nan kowa kuma ya sani in badon arzikin nasa da sukabi ba ina zata taba ganin uwar nata nan a tauye.
Kai barin fadama ba wani abinda zaka fada min wa yan nan mutanen su burgeni a duniyan nan na tsane su kamar yadda na tsani ranan mutuwata.
Amma mama uwar diyan shine fa bai dace kina aibanta masa mata da take matsayin uwar garken gidan sa ba haka a gaban shi.
Tace ko zaka rama mashine marata ido da bai san inda duniya ya dosa ba uwar garken sheri da ba,ayi hakan tsakani da Allah ba tun farko.
Da kyat ya samu barci ya dauke shi lokacin saboda tunanen irin abubuwan da suke faruwa dashi duk sabodani wanda kuma a karshe sai baiga laifin nuna kishi na din ba gareshi don ta haka maza ke gane irin son da mace ke masu ai saidai kishin idan yai yawa cutane wani lokaci don ya gani ga mahaifiyar su wanda zafin kishin ta yasa yanzu bata sanin abinda ya dace da ita na daidai.
Shine gabanin asuba ya samu barcin yayi gaba dashi har na tashi nayi sallah bai sani ba yana kwance ya dukule a wuri daya kamar yadda yara ke kwanciya idan suna barshi ya dan dora hannu yayi filo dashi.
A hankali na bar dakin har lokacin bai falkaba da alaman bai dade da fara barcin nasa ba don nasan ba kasafai sallah asuba yake wuce shi ba tundai wanan unguwan da musulmai keda yawa har jam,i yake zuwa wani lokaci don akwai mosque da sarauniya ta gina don musulmai.
Ban wani dade da fita a dakin ba ya falka a razane yana furta subbahanallahi yaya akai haka ya faru dashi baiji karan alarm ba ya tashi.
Kallon inda nake kwance yayi bana dakin a zaton shi ina bayi ne lokacin sai da ya saurara yaji bana cikin bayi tashi yayi ya koma dakin shi bathroom ya nufa don dauro alawa.
Maria na samu a kitchen tana aikin hadawa yara abincin tana ganina ta shiga gaidani da kwana na amsa mata cikin sakin fuska tare da tambayan ta mai take girka masu ne ?
Tace madam burgur ne nake tosting don ko sunje da abincin basa ci har su dawo dan murmushi nayi don tunawa da baya wai yau nice har rayuwa ya nuna min nawa diyan cikina sun fara daukan darasi a duniya.
Maria tace in koma kawai in kwanta zata gama komai a cikin lokaci nace ta barshi in karasa sai in dora abinda zamuyi breakfast dashi.
Daki ta nufa don yiwa yara wanka da shiyasu naci gaba da aikina a kitchen din hankali kwance.
Saidai aikin nake don ya rage min zafin danake ji a raina baiwai a cikin dadin zuciya nake ba lokacin.
Ni kaina nayi mamakin kare aikin abin karyawan danayi da wuri koda na fito falo na samu yaran suna fitowa daya bayan daya dakatar dasu nayi sai sun karya tunda maria tace min basucin abincin da ake dan saka masu a jakka suje dashi naji hankalina bai kwanta da hakan ba sam.
A daidai lokacin yaya ya fito a cikin shirin shi na da ya saka kwarjin shi ya kara fitowa sosai yana rike da labcoarth din shi sagale a haban hannun shi.
Morning dad yaran ke fadi daya bayan daya daga inda suke zaune saman dining table din ina basu abinci.
A hankali na dago kaina dan kalleshi tare da fadin ina kwana yaya kun tashi lafiya ya ban amsa yana shafan kan Abdulsamad dayakai inda yake tsaye.
Nice ke fadin suyi sauri su shirya kada su makara bus ya wucesu sai naji yaya na fadin ni zan kaisu yau ina da abinda zanyi can.
Suka shirya ya fice dasu gidan bayan ya zauna shima ya karya kummalo a lokacin ya fice da yaran.
Na dan dade a zaune wurin da suka barni kafin in mike in shaga daga ciki wanka nayi na shirya na kara kwanciya don nima ban samu barcin kirki a daren jiya din ba.
Ina tsaka da barci ya shigo dakin ya dan dade tsaye saman kaina yana kare min kallon yadda na dan koma don na dan fada ga cikin jikina da alama ban nisa sosai da haihuwa yanzu yace a ranshi.
Ke zahra yace daga inda yake tsaye yaga ban motsaba haka yasa ya dan bubuga min kafa na bude idanuna dake tattare da barci a lokacin.
Kallon shi nayi a cikin dakewa nake mashi sannu da dawowa lokacin na mayar da kaina saman filon da nake kwance.
Yayi karfin halin hade fushin shi a kaina yace ki tashi asibiti nake so muje a dubaki, da sauri na bude idona nace a dubani banda lafiya ne halan.
Yace ina son a duba ki don nasan bakije asibiti ba tunda kika dawo kasan nan ?
Nace ni lafiya ta kalau banjin komai balle inje asibiti wani dube dube yanzu kuma .
Kin dai ji abinda nace maki ban son raini hankali ana maki magana kina share mutum kamar wace bata san ciwon kanta ba.
Dole na tashi ba don naso ba na shiga bandaki na kewaya na fito na sameshi a falo yana jiran fitowa na.
Tunda muka dauki hanya ba wanda yai ma dan uwa magana a cikin mu har muka shiga haraban asibitin .
Katina ya bika suka dauko file dina sai can aka kirani wanan karon ma likitan mace ce muka sama asibitin ta karbemu kamar ta san mu da farko.
Bayan dan dube dube tana rubutu take fadin in rage yawan tunane kada yai min yawa ya shafi abinda ke cikina in dinga samun isashen barci ina yi sosai lokaci lokaci.
Mukai mata sallama ta fada min lokacin haihuwa na muka bar office din don zuwa sayen magani.
Muna cikin tafiya kamar yadda mukazo din na ba wanda yai magana a cikin mu sai naji yaja tsuki yana fadin.
Haka kawai don sakarci mutum yajawa kansa ciwo a banza kiyiwa mutane hasara kallon shi nayi nace injawa mutane ko in jawa kaina.
Tunda yanzu ba batun mu kakeyi ba kana zukin sabuwar amaryan da kake shirin daukowa inma wani abu ya sameni aikaina najawa ba wani ba.
Eh ai kinsan lokacin dana aure ki nayi rawan kafa sosai ba dole yanzu itama wanan din in mata rawan kafa kan zan shiga inda ban taba shiga ba.
Kashi ga mana yaya meye sabo a wurin da zai dameni ga wace tayi rayuwa lagos kowa ya sani ba abune boyayye ba idon ta ya bude da mazan lagos .
Karki soma aiban ta min mata don ba zan lamunci hakan ba ga kowa kowa ya zauna a matsayin sa.
Raina ya kara baci da wanan magana bace basai ka fada min yar uwaka bace don nasan dama nice bare a cikin ku ai.
Zaki iya fadan komai yanzu lokacine zai nuna kasan idan muna da rayuwa daga haka yai shiru bai kara magana ba nima na juya na bashi baya na bar zancen.
Muna shiga gida dakina na wuce ban tsaya falo ba ko gaisuwan da maria ke min sama sama na amsa mata shi.
Shigowa yayi dakin dauke da ledan maganin da muka sayo yana miko min amsa nayi ba tare dana yarda na kalleshi ba.
Zuwa yanzu ma dariya nake bashi don daukan abinda nakeyi a shirme yake kallon shi niko iyakar gaskiyana nake masa hakan.
Ban kara fitowa falon ba sai bayan magariba na fito don yunwan da nake ji a lokacin.
Yara na falo suna assingment tare da fauziya nake tambayan ta ko sun biya karatun da take koya masu saboda ban son su rasa karatun addini tare dasu don zaman mu a kasan turai da mukeyi babu daman kaisu samun karatun addini din.
Sun biya a gurin yaya dazun da yamma kafin ya fita ta bani amsa daga hakan na wuce zuwa dining don jin ambatan sunan shi da tayi.

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login