Showing 291001 words to 294000 words out of 419207 words

Chapter 98 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1433

dore sosai da ita.
Kwanan mu biyu a lagos wai sai yara sun huta yace kuma yana da abinyi duk da banga yana wani fita ba yana gidan ko wani lokaci makale da yaran shi a jiki.
Al,amarin yaya yana ban mamaki wani lokaci duk da na saba yanzu da irin halaiyan shi don dole na koyi wasu daga cikin halaiyan nasa.
Bai fadawa kowa zancen zuwan mu gida ba haka kuma ga maganan shi na gane nima baison in fadawa kowa zamu zo din.
Jirgin rana mukabi zuwa kano don haka hudu da wani abu muna cikin gidan shi na Kano inda gaba daya fasalin ginan gidan ya canza min ba tsarin farko akayi ba yanzu.
Anyi gyare gyare da dama a gidan an canza fasalin gidan da girman gida ya kara fadi da tsawo sosai ya koma wani aljannan duniya.
Mun samu ma,aikata maza uku da mata biyu dattijuwa da yar karamar matashiyar yarinya duk daga wurin Nasir abokin shi suka fito.
Abinci lafiyaye muka samu sun hada muna a falo muka yadda zango muka dan huta suna gaisawa da Nasir da Aliyu daya dauko mu daga airport wanda mamaki ya cika shi na ganin mu haka tafe babu sani ga iyali mun tara.
Yara kyawawa kamar mutun ya sace su don kyawo daga ba sai an fadama ba tashin turai su AC ta ko ina yana tashi a gidan.
A karshe na mike na shiga daga ciki don gabatar da sallah dake kan mu maria kuma ta kwashi yara zuwa dakin da Aliyu ya nuna muna nasu.
Sai Sultana ce ta makale min don ganin bakon yanayi taki yarda tabi maria tunda ya fita da sunan Sallah basu shigo sai dare dashi da Aliyu suka zauna sukaci abinci naji sun dauko maganan siri na basu wuri.
Da safe suke jin yazo a bakin Aliyu saidai daga haka bai kara masu ba sun dai san dan uwan yazo don yace ya aikeshi Yola zai tafi ya dawo a ranan kuma yake son ya dawo kano.
Uwar tace au yaushe ya sauka garin yace cikin dare suka zo jiya daga haka ya fita baiko tsaya ba da suka gaisa da mahaifin su kuma gaisa yake fada mai zai tafi yola yayan ya aikeshi.
Yana kwance bai fito ba nice dana tashi na fito wurin maria da yaran na duba su daga nan na zauna muka basu abinci.
Abdulsalam ne ya damu da tambayan daddy daddy na kaishi dakin da yake shigan yaron wurin shi yasa ya taso suka fito tare ya zauna dasu nan suna masa shirmay har lokacin a kage nake inji yaimin maganan zuwa gida.
Sai bayan ya karya ya sullace jiki daga yaran ya tafi yai wanka ya fito zuwa lokacin nima na shiga dakina nayi wanka na fito a cikin wata doguwar riga din kin yan chaina.
Rigan har kasa sai gurin hannaye aka budashi hannunwan suka dan sauka shara shara sai gyalen su da nayi rolin din kaina dasu kayan sun kara haskani sosai sun fitar min da shape dina waje.
Ina kara gyara fuskana ya shigo yana fadin kin shirya mu shiga gida mu gaida mutanen gida nace a shirye nake zamu iya zuwa yanzu ai .
Yaran fa nace nasan maria ta shiryasu tun dazun amma yanzu zan fito in duba su ya fita yana waya daga dakin.
Kara duba kaina nayi sosai banda makusa ta ko ina na dauko jakkana na fito tare da jawo kofan dakin na murza key don ban san irin mutanen da zamu zauna dasu ba a lokacin.
Da ganin shiga kasan akwai sirki a cikin lamarina yanzu don ba shigan mu na matan hausawa da muka saba nayi ba saboda sabo tun a can.
Wurin maria da yaran na leka nake fada mata zamu shiga cikin gidan mu ta kula da gida kafin mu dawo ta amsa da yes ma.
Kafin ma in fito na samu har ya fita da yaran suna mota zaune suna jiran fitowa na lokacin tun fitowana ya kura min ido wanda ban san dalilin yin hakan ba nazo na bude motar dake sheki da walkiya baka wuluk na shiga na zauna ya tayar da motar muka dauki hanyar gida sai bin ko ina da kallo nake ina tuna abubuwa da dama duk wuraren da muke bi zuwa islamiya wasu ancanza masu falin gina anyi shaguna wasu kuma an rushe ga baki daya ancaza ginan nasu kano ke nan ta dabo tunbin giwa koda may kazo anfika sukace.
Idona na lumshe a hankali cikin yanayintunanen irin karban da fassaran da hjyn su yaya zatai mun idan mun shiga gidan.
Da farkon shigan mu babu kowa a haraban gidan namu shine tsakiya Abdulsalam da Abdulrahaman suna daga ko wani gefen shi ya safa Sultana a kafadan shi.
Sai ni dake gefen shi tafe da yar hand back dina da nake rataye dashi a kafadana cikin shigata ta alfarma da daukan ido.
Daga part din Amma murja ta fito da gani fita zatayi a lokacin ganin mu kawai tayi tafe da farko bata sheda mu ba sai daga baya ta fara gane yaya ta sake waro ido da kyau tace A ruwa ?
Sai kuma ta juya da gudu tana ihun kiran Amma da mama ga Aruwa ga Aruwa Amma.
Ihun ta ya kara jawo hankalin sauran mutanen gidan lokaci daya hjy maryam ta bude kofa da sauri ta fito kafin kowa ya fito.
A,a sai kuma taja tayi turus ta tsaya tana kallon mu da mamaki tace ikon Allah duk wanda ya fito abinda yake fadi ke nan sai a kallemu cikin mamaki.
Kowa ya kasa karasowa inda muke sai fitowan Amma data fito tana fadin a, a, a lale lale lale marhabin da mutanen turai.
Lokacin na wuce yaya da sarsarfa na isa wurin ta da gudu na rugume ta sai hawaye a lokaci daya suka zobo min.
Itama Amma kukan ta fara hjy maryam ta karsa inda yaja ya tsaya yaran suna make mashi a jiki cikin rashin yarda.
Ikon Allah tana mika hannu zata karbi Sultana ta kara make mahaifin ta sosai alaman bata zuwa ta mikawa su Abdul suma suka yi kamar yadda yarinyar tayi da farko.
Wanan abinda mamaki yake yara har sun kai haka bamu da labari a daidai lokacin da Nafisa ta bude kofan part din su ta fito tana ganin shi da yara taja ta tsaya da mamaki sai kuma ta juya da gudu ta koma ciki tana kiran sunan hjyn su.
Aruwa duk yaran kine wa yan nan diyan murja da farin ciki ya kasa boyuwa a fuskanta tana tambayana.
Na dago kai ina girgiza mata kai nace yaran ki ne ba nawa ba cikin zolaya tace A ruwa yaushe kika haifi yaran nan haka bamu sani ba ?
Amma ta sakeni tana mayar da hankalin ta inda yaya yaja ya tsaya da yaran yana kallon mu yana murmushi.
Na dago kai ina kallon part din mamu da har lokacin banga wanda ya fito ba daga part din a daidai lokacin Fauziya ta bude suka fito da gudun su a cikin murna.
Nima da sauri na karasa na rugumay su ina murnan ganin su mun dade rungumay da juna dasu.
Saudaki kakai miskili sai kuma ta fashe da kuka shidai murmushi yake a fuskan shi yana sauraren ta.
Kafin yace may kuma nayi Amma daga zuwana yanzu ban yarinyar in dauka ka make ya ka hana mutane iya shegen ka umar yayi yawa saidai addua kawai.
Kin zuwa sultana tayi wurin ta a nan ya fara tafiya da yaran yana fadin bari mu shiga wurin mama mu gaisa.
Yaja yaran shi suka nufi hanyar dakin mahaifiyar shi sun rigani shiga don haka ban nan suka fara kwasa dashi.
Yana shiga tana zaune a cikin mamaki takaicin labarin da Nafisa tazo mashi dashi yayi sallama ya shigo falon.
Yana aje yaran saman kujera tare da fadin mama mun samayku lafiya ?
Lafiya ta amsa mai a takaice tare da fadin wa yan nan yaran fa daga ina kazo dasu kuma yaran waye kuma ?
A daidai lokacin da ya kara rungume Sultana a jikin su su Abdul suna haye mai jiki cikin nuna shi din mahaifin su ne.
Saidai hakan bai hana hjy yi mashi wanan tambayan ba ya dago kai a hankali yana fadin jikokin ki ne mama yaranane.
Babawo yaran ka ko may kake fada min haihuwa kayi da wanan yarinyar ko may ?
A daidai lokacin muka shigo part din tare da murja da fauziya da sallaman mu don yana wucewa Amma tace jeki ki gaida sarakuwan ki.
Shine muka nufi part din ina rike da hannun fauziya a makale dani muka shiga part din.
Sallama mukayi yanayin da muka same su a ciki ya nuna muna wani magana sukeyi mai muhinmanci a lokacin.
Har kasa na kai irin gaisuwan al,adan malam bahaushe cikin ladabi nake gaishe ta da mama ina wuni mun samay ku lafiya ya gida ?
Sai daya dago kai ya kalleta tace lafiya tana basarwa mun anzo lafiya ta fada tana kawar da kai gefe.
Lafiya kalau na fada saina koma na zauna a kasa nayi shiru tare da dukar da kai ina wasa da hannun Fauziya.
Falon yayi shiru na dan lokaci sai shi ke dan hira da yaran shi yana tambayan su may suke so.
Hjy dake mai kallon kasa kasa imani da takaici ya kashe ta a lokaci daya don gaba daya ma bata a cikin hayacin ta a lokacin.
Can na dago ina fadin zan shiga in gaida mutanen gida bata tanka mun ba sai shine yace kada ki dade kin san yaran nan ba sake jiki zasuyi ba idan basu ganin ki a kusa.
Ka bata yaran ta ta tafi dasu wurin kakannin su mana bazasu tafi bane idan ban tashi ba yacewa uwar .
Tayi mai wani irin kallo na kaidin tare da kawar da kanta gefe daya kokatin amsan Sultana nayi daga hannun shi akai sa,a yarinyar bataki ba a lokacin ta biyoni muka fice tare muka barsu nan.
Zama yayi har ya gaji batace dashi kalaba karshe ma tayi wani nishi ta fice daga falin zuwa cikin dakin kwanan ta.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:31 - ??5惙5惙5?: BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAMANIN RAHIM IYYAKA NA, ABBUDU WA IYYAKA NASTA, IN, , , , ,


Muna fita har lokacin a tsaye waje muka samu su Amma mama hadiya hjy maryam da sauran yaran gidan kowa na mamakin ganin mu.
Amma har yanzu kina gun bara na gaida mamu nazo mu gaisa maimakon in nufi part din mamu kai tsaye na hjy maryam dake tsaya muka nufa.
Ganin haka tabar gurin itama ta nufo mu part din nata muka gaisa har lokacin wani irin kallo na mamakine karara a indon ta ban tsaya ba don irin kallon kurullan da take min din a lokacin.
Haka na fito dauke da Sultana murja da Fauziya a ko wani gefena muna tafe muna hira murja tana fadin A ruwa ga baki daya kin sauya kamar ba kece ba kin koma kamar balarabiya dake kunyi masifan kyau daga ku har yayan ku.
Wallahi kamar ba kece kika haifi yaran nan ba naku don kamar har yanzu kike budurwa kike.
Murmushi kawai nake mata muka shiga wurin Mamu mun sameta zaune a falo tana ba dan karamin yaron data haifa a bayana abinci.
Da sarsarfa na isa gurin ta na rungume ta a cikin murnan ganin juna tace kada ki karya mu da wanan nauyin naki haka ?
Na daga ina dariya kafin in zauna kasa wurin kafanta ina fadin mun same ku lafiya mamu na dubu yaron da aka haifa a bayana nace mamu wanan yaron naki duk mun fishi kyau dakin nan.
Ta dan kalleni tana fadin gashi ko gwaggona ko yaushe cewa take yana kama da mijin ki sosai duk shi ya biyo.
Dariya na kwashe dashi ina kokarin aje Sultana data makale min a jiki ina fadin haba mamu wanan ina yakai yaya umar kyau ?
Sultana taki zama Fauziya ta dauketa da karfi tana fadin bari a goyata ko zatayi barci anty.
Yau sai gamu ga mutanen turai har da tsaraban bakin fuska da karuwa aka samu bamu sani ba haka ?
Jin muryan mai magana yasa muka juya muna murmushi hjy maryam ce da imani ya cika ta kara biyoni part din mamu.
Ta shigo har cikin falon mamu ta zauna saman kujera muka kara gaisawa tana fadin gaba daya Fatima ta sauya kamar ba ita ba.
Murmushi mamu tayi mata kawai sai murja ke fadin abinda nake fada mata ke nan nima ai ba zakace ita ta haifi yaran nan ba kamar budurwa har yanzu.
Tace ai abu yayi kyau ai haka ake son aure ka auri namijin da zaka karu yan uwanka su karu shine dadin auren wayayyen namiji.
Shiru mukayi ba wanda ya tanka mata tana ta zuba can ta mike tana fadin bari na leka Umar da inga sauran yaran.
Ta mike ta fita tana bacewa murja tace munafuka gulma ya cita ta rasa yadda zatayi har da shigowa ta zauna.
Na kalli murja ina fadin har yanzu halin nata yana nan ne tace may zata fasa saidai Allah ya gyara tunda sun sawa ransu mugun abu kullun.
Yanzu ji abinda take fadi fa watau kin samu wuri yan uwanki zasuci arzikin da kike ci kema ke nan.
Mamu dai bata tanka muna ba sai cewa tayi a nan ke nan zaku wuni yau nace banyi tsamanin hakaba don yanzun ya gama fadin akai yaran gida sun ki sake jikin su.
Zasu sake ai yanzu basu saba damu bane basu sanmu ba shiyasa basu yarda ita wanan gata sun shige sunyi shiru da uwarta ciki kila tayi barcine ta samu baya.
Su mazajen nawa suna gun uwargidan su ta rikesu ke nan mama ai ta bar maki don cewa tayi kece kakarsu a kawosu wurin ki da zamu fito.
Sai mamu tayi murmushi tana fadin hjy ke nan har yanzu dai abin na nan kiyi kokari ki shaye duk wani abinda zata fada akan ku don darajan mijiki a wurin ki ita din uwace kuma a wurin ki.
Yara kuma ko taki ko taso jini ya riga da ya gauraye da ruwa tun farko sun makara.
Mamu kawu fa yana shagone tunda muka shigo naga part din shi a rufe na tambaye ta tace bai dade da fita ba kuka shigo kila baisan da zuwan ku bane ya fita.
Kin shiga wurin gwaggo ta tambayeni da cewa Amma nace yanzu dai zamu shiga daga gun su hjy muke.
Na mike kenan da zuman zuwa gurin Amma sai gashi yayi sallama ya shigo part din na mamu ta amsa mai a cikin mutunci.
Sai daya kai zaune suka fara gaisawa dashi tana mashi yaya hanya da yara ya amsa da lafiya mun samay ku lafiya yaya Addah ta iso kwanaki.
Ta amsa da lafiya tazo tana godiya sosai Allah ya kara arziki mikewa nayi a daidai lokacin ya dago kai yana fadin ina kuma zaki.
Ban shiga wurin Amma ba na bashi amsa ina kokarin gyara gyalen kaina dake sabulewa a lokacin gashina da ya kwanta lub lub a kaina yana baiyana a fili.
Amma kin san yaran nan sun gaji hutu suke so yanzu don haka kizo mu mayar dasu gida su huta hakana.
Ya idan ban shiga gurin Amma mun gaisa ba kasan ban kyauta ba yara ai nan ma gidane su zauna mana su huta a nan.
No ya fada yana mikewa tsaye yanayin shi yana nuna shima a gajiye yake lokacin ko kuma yana cikin wani yanayi mara dadi a lokacin.
Ki shiga ki fito muna mota muna jiran ki Sultana fa ya tambaya tana gun Fauziya ta goyata tayi barci sai yayi shiru ya rigamu fita part din.
A gurguje na shiga wurin Amma din muka gaisa take tambayana yaya kuma taga ban zauna ba na bata fuska ina fadin yaya ya matsa in fito tafi yaran sun gaji wai.
Shi umarun yace haka yana ina mara kunya wa zaiwa iya shege ne yanzu da rashin kunya shi a ina yayi wayau ba a gidan nan ba ?
Yana mota na bata amsa ina hade rai nan na barta na shiga wurin mama hadiye saiga yara sun zo kirana da gudu wai ance in fito mu tafi.
Raina kara batawa Amma ta mike tsaye tana fadin wanan wanan sadauki akwai iya shege dashi kabar yarinya mu ganeta saboda diyan ka zaka takura ma yar mutane.
Amma na biye dani tana masifa a bayana a gurguje na sallami mamu fauziya ta biyoni da yarinyar a bayanta .
Ina sadaukin yakene tana

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login