Showing 168001 words to 171000 words out of 419207 words

Chapter 57 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1417

daura zataji idan zai yuyu.
Kowan su tunane yake a ranshi ta yaya zasu iya boyewa mahaifiyar su wanan maganan mai muhinmanci a garesu haka duk da sun san idan taji ma daga bayan ba,a hutaba.
Sun dan gama tataunawan yace zasu iya tafiya Allah ya kaimu gobe bayan ya mika masu kaya a cikin ledoji dinkaku da zasu saka a ranan.
Haka suka mike suka fice daga falon jikin kowan su babu karfi sai tarin bakin ciki da takaicin dake cin ransu lokacin.
Har sun nufi hanyar part din mahaifiyar su umar ya dakatar dasu yana fadin ina son ku sani yiwa mahaifin mu biyayya ya zama wajibi a gare mu .
Mudin muna son haske a rayuwan mu ya kamata kowan mu yabi umurnin mahaifin namu don mu gama lafiya dashi kamar yadda yake so har ya nuna muna jin dadin shi a fili haka kan yardan namu.
Don haka zuwa gurin mama a wanan lokacin yana nufin rushe farin cikin mahaifin mu ne don babu yadda za yi mu shiga wurin mama yanzu bata fahinci komai ba gare mu.
Don haka ina shawartan ku da ku daure mu kyale mama har sai komai ya kammala kamar yadda daddy ke so damu daga baya koma may zai faru sai ya faru mundai nuna ma daddy mu masu biyayya ne a gare shi .
Ajiyan zuciya Aliyu ya sauke da tun fara maganan ya kasa furta komai sai lokacin yace nima hakan nake gani don ba komai yasa zan hakkura da hakan da daddy ke so sai do goben mu don muma zamu so diyan mu suyi muna biyayya a gare mu wata rana don tarihi yakan maimaita kanshi akan mutum.
Kayi tunane Aliyu abinda na dade ina faman tunane ke nan a raina yasa nake nuna yarda na, babu gardama ga mahaifin mu don mu rabu lafiya dashi.
Ya dafa kafadan habbib dake cika yana batsewa tsaye gefe daya hannayen shi daye cikin aljihun wandan shi yace be cool bros komai zai zama sauki da yardan Allah.
Kai kawai habbib ya iya kada mai ya juya zuwa hanyar fita gidan hankali a tashe daga haka sukai sallama kowan su ya bar gidan.
Hjy jummai ta aje masu abinci tana jiran shigowan su har goma na dare bataga shigowan su ba yasa ta kira layin Aliyu don shi keda saukin samu a cikin su sai dai waysn tasa a kashe take haka yasa ta gwada na habbib shima hakan.
Tayi tunanen kiran umar sai dai tasan tunda yakai wanan lokacin bai shigo ba tasan ba zai shigo din bane don baikai karfe tara ma a gidan shi.
Haka taita gwada layukan nasu baya shiga dole ta hakkura da rashin samun su din ta kwata da tunanen ina suka shiga haka basu fada mata ba don tasan komai under control din ta sukeyin shi.
Ba zasu iya yin wani abu kai tsaye ba indan suna garin kai koma basu garin hakan kamar ya zamo masu jiki sai sun sanar da ita dan dama umar da ya fara girma ya fara yarda wanan akidar tasu na yan dakin nata.
Don haka ne wanan damuwan nata a ranan yai yawa rashin jin yaran nata ko washe gari haka ta aje abinci ba wanda ya shigo daga cikin su dan dama Aliyu ya dan leko a gurguje daukan abu salma ta ganshi yace tace yana zuwa suna wani aiki ne yasa bai samu lokacin shigowa ba.
Taje ta fadawa uwar tasu kafin ta fito ya fita yabar gidan bata samu ganin shi ba ya wuce ko da saurin shi.
Karfe biyu daidai A massalacin dake unguwan an tashi daga sallah jumma,a aka sanar da daurin auren wanda ranan mafi yawan bakine suka halarci masalacin daga cikin su harda su baffa da sukazo daga misau a ciki da sauran abokan daddy da suka samu labari a kuraren lokaci.
Wanda hakan yaba mutane mamaki da dama hjy jummai da bata san abinda akeyi ba tana can tana sheka barcin ta a dakin ta ta saka wayan ta a silent don tana son ta huta haka yasa kira da yawa na masu son cinta tara yai ta shigo mata bata sani ba.
Hjy maryam data tsuncin labarin daga sama shiganta uku wurinta tana samun tana barci ga tsegumin haka yana cinta dole ta hakkura har ta tashi taji kwam.
Sai bayan anci an sude kanen ta da suka zo a fusace don jin yaya harkan ya faru basu da labari su bayan ko jiya da yamma suna tare da ita bata fada masu ba.
Ta daiyi masu korafin ya kira yara ba tare da ya sanar da ita zasu zo ba bata kuma san dalilinn shi nayin hakan ba ya kyale yaran a cikin damuwa .
Cikin barci taji bugun kofa a tashin hankali ta farka a razane tana kallon kofan tare da fadin wai waye ne don Allah ke damuna.
Turo kofan sukayi suka shigo kallon yanayin fuskan su kawai ya nuna ba lafiya ba a rude take tambayan su lafiya ta gansu haka hankali tashe ?
Kallon juna sukayi tare da samun wuri suka zauna ba wanda ya iya magana a cikin su kara tambaya ta maimaita masu may ke faruwane wai na ganku haka kamar a rude ?
Anty Alh yayi maki bayani ko a rikice tace wani Alh bayani akan mau kuma don Allah ku fada min abinda ke faruwa kun barni a duhu ?
Kara kallon juna sukayi sai babba daga cikin su tace bai maki bayanin kan auren yaran nan da aka daura yau ba bayan sallah jumma,a harda na salma aciki ?
A rude take fadi tana nuna kanta tana fadin yarana harda salma wace salma wai kuke magana ne ?
Salma dai nake dasu babawo yau an daura masu aure yanzun nan ma har gida ya fara cika da jamma,a.
Ta sake nuna kanta tana fadin ni ni Amina ni din nan Alh zaiwa sheri a idon, , , bata iya karasawa ba sai ta tafisu ta fadi a sumay.
Ihu suka saka suna kiran sunan ta ina bataji tayi suman gaskiya a lokacin don bata san wanda ke kanta ba.
Hjy maryam dake jiran taji kwam sai ganin yan uwanta tayi maza suna shigowa wurin ta da kwandunan goro da minti dasu chewing gun.
Tana kallon su da mamaki ta karaso falon tana fadin yaya kune tafe ashe ai wanan kwandunan ba a nan za a kawo suba don na yan shiyan hajiyace kayan .
Yayan su babba yace wanan na nan shiyan ne don kayan daurin auren ikilima ne da sadakinta yanzu aka bamu don karramawa mu shigo maki dasu nan.
Ikilima kuma yaya ta tambaya da sauri cikin tsure su da ido tana kallon su eh yanzu aka daura masu aure harda ita ciki ai.
Yau da safen nan yaje ya fada muna muma haka mukaji zancen daga sama wallahi shiyasa bamu tsaya neman ki ba don ba lokaci kamar yadda yai muna bayani din.
Ni ni Alh zaiwa haka ya tozartani a idon duniya maina aje yanzu na auren ikilima har nawa ikilima take ne wai da zai daura mata aure ban sani ba.
Sai kuma ta fashe da kuka mai ban tausayi a lokaci guda suka shiga bata hakkuri a wurin.
Sallah na idar naji ina bukatan kwanciya a kasan don yanayin jikina dake min ciwo a lokacin yasa na dan kwanta in huta.
Na soma barci naji murya kamar na baffa na suna gaisawa da mamu zubur na mike zaune ina kokarin tashi naji mamu na fadin yaya ashe kun iso ko ?
Yace eh maimuna mun shigo makare yasa muka wuce wurin daura auren baki daya don mota ya dan bamu matsala a hanya ne .
An daura yanzu alhamdullahi Alh yayi kokari har yara goma maza biyar mata biyar sai addua ake masa a gurin taron.
Tsaye nake na kasa karasowa gurin don jin maganan da sukeyi sai dai gaba ya fara faduwa ganin har da baban Atika a cikin falon da sauran fuskokin da ban iya shedawa a lokacin.
Baffa yana fadin banda abinda zancewa Alh sai godiya don har surukin namu an kirashi mun gaisa yanzu yaron kirki kamili mai mutunci baban su Atika ke fadi.
Huce na ke wanda ban san daga in yake zo min ba kafin na fara kuka in kai kasa a wurin jin faduwa na ya jawo hankalin su a inda nake suna fadin subahanallahi ku kamata.
Da sauri mamu ta isa gurin da mama suwaiba da ban san zuwan ta gidan ba suna fadin yaya haka kuma wani irin mika nayi na sake ihu mai karfi daya gigita kowa a falon take gurin ya rude.
Baffa yace subbahanallahi wanan matsalan ya taso ke nan na yatinyar nan wai dama haka abubuwan nan suke damun fatima ne yanzu ?
Wasu abubuwa kuma yaya mamu data gigice take tambaya tare da fadin bata da matsalan komai dama yau dai ne na fara ganin haka a gare ta ai.
Wanan matsalan ko a misau ya taso mata haka akasha fama da ita ranan har dare ana abu daya da yarinyar nan a gurin.
Mamu tace tau walllahi bata taba yin haka a nan ba gaskiya tunda tazo garin nan sai yau din nan na fara ganin haka gare ta.
Murde ni ake ana wani irin lankwasa ni da juyani guri daya sai mai kallona ya dauka bazan iya more jikina ba kuma a rayuna.
Fita tayi da sauri zuwa part din Amma suna zazaune ana mayarda yadda abubuwa suka tafi kamar yadda kawu da yan uwan shi suka tsara komai sai ganin mamu hankali tashe sukayi tana fadin gwaggo kizo ki duba sayadi halin da take ciki.
Gaba daya su mama hadiye suka mike suna tambaya ta kasa fada masu komai don hankalin ta dake tashe a lokacin.
Suna shiga falon mamu kowa ya tsaya da mamakin yana kallon ikon Allah abinda ke faruwa a falon lokacin salati Amma ta fara tana tafa hannayen ta a cikkn mamaki tana fadin.
Yar nan dama tana tare da mutantanin nan ne haka ba a sani ba sai yau ranan auren ta suka taka haka a kanta ?
Kowa na tsaye yana kallon ikon Allah shigowan kawu sani ya ce kawu balarabe ya kai su baffa masauki suci abinci kafin su juya.
Waya ya dauko yayi kiran wani layi baifi mintina ba wani mutum ya shigo saye da jallabiya fara a jikin shi .
Tunda ya tun karo inda nake wa yan nan abubuwan ya kura min ido har lokacin daya tsugunna daidai inda nake din kwance yace assalamu alaikum idan musulmine su amsa min muyi magana.
Sai shiru ba magana kusan biyu suka zagayo suna nasu sallon sai can akaiwa malam din sallama kamar ba muryana ba.
Ya amsa tare da fadin may ke tafe daku mai zaisa kuzo mata yau ranan farin ciki a gare ta kuma zumunci ya kawo yaran mu wurin ta don su nuna mata farin ciki.
Yace amma ai ba haka ya kamata ku nuna farin cikin ku ba gare ta ko yace kasan yaran zamani ba jin magana sukeyi ba sai dai nima nazo ne don in fadakar daku akan wanan baiwar Allah.
Tana tare da makiya a ko ina mun dade a tare da ita bama yarda wani ya cutawa rayuwan ta da can munsata rashin ji sosai da wasu abubuwa na yarinta.
Sai dai yanzu zan fada maku duk lokacin da kuka ganmu ku sani wani abin cutarwa ne yake harinta zamu taka duk wanda ya nufeta da sheri komai kankantan shi.
Dan murmushi malamin yayi yace Allah ne kadai ya isa ya kare bawan shi ga komai sai yayi dariyan manya tare da fadin ka manta Allah na sanadin sa ta ko ina a cikin wanan sanadin muna daga ckin kaddaran ta .
To idan ku musulmine don Allah ku bar boyar Allah nan ta zauna lafiya kunga yanzu tana gap da shiga sabon rayuwa ne .
Ya tare malam da fadin saboda hakan ne muke yawan biyanta wanan lokacin domin sihirin da ake kokarin aikowa gare ta .
Da kyat dai bayan sun gama kwasa da malam tare da jin abubuwa daga bakin su suka fita kaina tun lokacin na kwanta wani barci mai nauyi ban kara sanin inda kaina yake ba saida Amma har mamu suna kaina ranan.

Zan iya cewa ranan mama hadiye da yaranta ne suka kwana cikin farin ciki a gidan bayan su ko wani part a ciki tashin hankali suke.
Part din hjy jummai ke asibiti da ita inda yaranta gaba dayan su suna asibitin sun zagaye ta cikin tashin hankali fuskan kowan su babu walwala a cikin sa ranan.
Sai shaga da fice suke a dakin zuwa office din likita uwa ke nan mai yafi uwa dadi a duniya.
Alh sani ma da yan uwan shi da farko sun dauki abin kamar wasa sai da sukaje suka iske halin da take ciki ne suka gaskanta girman maganan nata.
Zagi da diban albarka ga auren an shashi ga bakin yan uwan hjy jummai ranan duk wanda yazo da irin abinda ake fada saida wani baba a gare su da kawun su suka tsawata masu aka koma yi a boye.
Kawun yace may kuke nufi da zagin bawan Allah nan da kukeyi dashi da yayan shi zaku hanashi yin iko da abinsa ne ?
Wani irin mulki da nuna isa ne jummai batayi a gidan Alh sani ba har mutane na ganin ta koma miji shi ya koma mata sai yau da yafito ya nunawa duniya ya isa da gidan sa yanzu shine zaku zageshi.
A lokacin da yar uwarku take nata mulkin da nuna isa may yasa baku zage ta ba sai shi dayayi abinsa bisa kan ka,ida zaku saka shi gaba da zagi haka ?
May ye laifin Alh sani cikin yiwa yaran sa gata dayayi wanda ku duk nan baku sanda hakan ba sai gaba.
Ya fiku hange da tunanen nesa don yasan abinda yakeyi lokacin da dan ku ya dauko maku maidan buje may ye nan baku fada ba ga hakan ?
Sai yanzu da yake son nunawa duniya shidin mutum ne wanda ya isa da iyalin shi kuke kokarin hurewa yar uwan ku kunne ?
Shiru sukayi har su Aliyun su uku dake tsaye daga gefen gadon suna jin batacin da sukewa mahaifin su da sunan son yar uwarsu gare su.
Ya juya wurin su Aliyu yana fadin kunyi daidai don ku ba mata bane ubangiji Allah yai maku albarka ya kawo haske ga lamarin ku yaba abinda zaku kula da iyalan ku ta hanyar halal ya baku zuria dayyaba masu albarka.
Idon ko wanin su yayi ja don tashin hankali da fitina tsohon yace kunyi daidai kun nunawa duniya iyayye suna gaba da komai wayewan ido ba shine sanin duniya ba bin iyayye shine alheri.
Sannan ku idan kun san ba zaku taushe yar uwarku ba na rokeku Allah ku bar kysantan ta a wanan halin sai idan komai ya lafa.
Yana mai hade hannaye shi guri daya yake wanan maganan tare da bin kowa dake dakin da ido cikin bacin rai da kunan zuciya.

Ban garen hjy maryam ma yan uwa sai da suka taru suka taushe ta da kyat aka ciwo kanta ta hakkura tabar kukan da takeyi.
Ikilima ma kusan halin da nake ciki itama ta kwana ranan don su ko mijin ma ba wanda ya sani don koda suka tambaya akace masu sunan mijin dai nata Abubakar .
Ba wanda yasan wani Abubakar ne don Alh baya cikin hankalin shi ranan ba wanda yaga fuskan shi balle a zauna maganan.

A ranan su baffa suka koma bayan sun kara ganawa da Alh ya sanar dasu ba zamu kai lokacin daya diba na shagalin bukin da mata zasuyi ba don mijina yace yana da aikin yi can zai koma da wuri.
Don haka masu zuwa zasu iya zuwa gobe ko jibi za ai yinin bukin gaba daya a huta tunda komai da za a tanada dama an gama shiryawa.
Da wanan bayanin suka koma gida bayan ya kara bin su da alherin dayace angone da kansa yace a basu su kara namai a motar su.
Kowansu ya koma misau ciki da farin ciki da al,ajabin karamcin irin na Alh sani a zukatan su har suka kai suna hiran irin hayan wanan mutumin.
Mamu da su mama hadiye sunje asibiti duba hjy a cikin daren ta barmu da Amma dake zaune damu a part din yayin da ni ban san inda kaina yake ba saboda narcin da nakeyi.
Ba wani tarbon arzikin da suka samu don yan uwan hjy ne maza da mata tab a dakin gaida ita sukayi inda bayan hakan ba wanda ya kara bi ta kansu kuma.
Sun dan tsaya sukayi masu

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login