Showing 327001 words to 330000 words out of 419207 words

Chapter 110 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1467

yana raye.
Duk magana ya tashi ke kenan a cikin zagin kaddaran da ya sameta don kawai mahaifiyar ta tana kasan su .
A laila ba mamaki yarinya wuyan ki ya isa yanka a gidan nan ni kike kokarin yiwa kashedi akan uwar ki ko mai a gidan nan.
Ai ba tafiya zakice kakar taki tayi ba kice tana wurin yawon dandin da suka shigoyi dama a kasan nan.
Allah sarki hjy gara da yau kika fadi manufan ki kowa yaji a gidan nan mamu tace sai dai saukin abin asalin kowa a tafin hannun kowa yake yanzu.
Amma dai kin san mun san mahaifin ki su suka fara budewa karuwai gidan clubs a garin nan a fili yana yawo da betil da mata da rana suna shan giya suna rawan yawon siyasan NPN duk da tsufan shi ko kin manta da hakan duk da ban sani ba kunne ya girmi kaka ai.
Wani irin kukan kura hjy tayi mamu ta mike tsaye nan fitina ya murtuke sosai a tsakanin su tana fadi tana fadi duk suka rikita gida mamu na fadin na gaji kullun ina daga maki kafa baki daukan girman ki.
Aliyu ne ya samu wanan fitinan a gidan ya juya ya fita rai bace in auren yarki yayi dubu da babawo ya mutu a gidan nan .
Mamu tace sai me don kin kashe auren danki naki nakima ai baki damu da yamutu ba balle na wani hjy wani girma da kimar da nake baki duk ya kare a gidan nan daga yanzu yadda baki kaunana da jinina haka nima ban kaunar ki har cikin raina.
Kawu da yaji hayaniyar yayi yawa ya fito basu daina ba yace wace ta kara tankawa a wurin a bakin auren ta fadan malam bashe a gidan shi hakan yasa kowa taja kafanta ta koma part din ta cikin kunan rai.
Nikan har cikin raina banji dadin hakan daya faru tsakanin su ba don nasan abu zai kara rikicewa a tsakanin mu ke nan.
Saidai kuma naji dadin amsa mamu sosai don ta rama cin fuskan da hjy ke mata tana ganin bata san nata zancen ba na fada.
Ashe yaya baya garin anyi haka da kwana biyu ya dawo tun yana can Aliyu ya buga mai waya yana sheda mai cikin bacin rai.
Koda ya dawo bai nuna yasan komai a kan zancen ba sai hjy ce ta fito mai da zancen karin auren shi yace ban shirya aure yanzu na fada maki mama.
Zaman Fatima a gidan nan da daddy ya zaunar da ita nake son ta koma don ban fahinci may hakan yake nufi ba don.
Kai dakata kaji idan itace autar mata babawo ka gama zama da wanan yarinyar diyar marasa tarbiya diyar wa yanda basu da mutunci.
Mikewa yayi ya bar part din ba tare da ya tsaya sauraren ta ba sai da dare ya kira mamu a waya.
Yace ina son Fatima zata koma dakinta cikin jikin ta yana girma zamu koma tare wanan karon.
A,a umar ya kamata ku hakkura hakana da kai da ita kasan mahaifiyar ka har yanzu tana kan bakanta ga zancen nan zaifi don Allah idan haka yafi zama alheri a gare ku Allah ya tabbatar muna da hakan.
Nagode yace ya kashe wayan shi ina zaune ina jin yadda sukayi dashi a wayan .
Kaina na dukar lokacin da take aje wayan naji tace kai bawan Allah nan shima yana cikin wani hali wallahi.
Wanan al,amari yakai min inda yakai wallahi tun farkon wanan hadin abindana guduwa ke nan don halin hjy sai ita.
Al,amarin sai addua wallahi naji ta fara jero addua,a tanayi sai kuma tace ni yaran ma suke ban tausayi kullun idan sun shigo nakan shiga wani hali wallahi.
Ni idan ma auren zatayi mai tayi masa kowa ya huta tunda ba,a kan ki zata shigo ta zauna ba kowa da halin sa ake zama dashi ai.
Washe gari ina barcina sa goma zuwa shadaya dake min dadi a yanzu naji mamu tana tayar dani wai kawu suna neman ta a falo ga yaranan zaune falo.
Nafito ina tunane kan me kuma su kawu suke neman mamu fitinan gidan nan dai baya karewa wallahi.
Mamu tana zuwa falon Amma ta samu falon a cike yake kawu balarabe yace ina ita Fatiman take tace ina daki tabashi amsa.
Ka barta tukun sai idan an fara magana a kirata zai fi kawu yace a dai kirani kusa yanzu zaifi dole mamu ta fita ta kirani muka dawo tare da ita falon Amma din.
Lokacin da na shiga nayi mamakin ganin mutanen da aka tara a falon na samu wuri kusa da Amma na zauna na fara gaida su.
Wanda naji kawu balarabe ya kira da liman ai muna addu,a kafin mu fara abinda ya kawo mu ko ?
Sai mutumin yayi addua ya kara da fadin duk abinda za,a tatauna ya zama alheri a garemu baki daya suka amsa da amin.
Kawu balarabe ya kalli yaya yace jiya ina gida Faruq ya sameni da wani zance akan matar shi wanda ni duk dadewan nan basan da wanan zancen ba gaskiya.
Yanzu dai gashi muji daga bakin shi don kowa yaji wanan maganan dayazo min dashi shiyasa na taraku a nan gaba dayan mu don samun mafita ga zancen.
Yaya dake kasa gefe shida habbib ya gyara zama ya fara da sallama yace akan zancen matanane Fatima da daddy ya aura min har mukai haihuwa uku da ita gana hudu a cikin ta yanzu.
Don muna zaune daddy ya kirani ga waya muna zuwa ya bada umurnin itata koma dakin mahaifiyar ta ni kuma mama ta rikeni da yayana tun wanan lokacin ban kara jin wani magana a kan zancen ba.
Yanzu ina son matana ta koma dakin ta don ina son mu tafi tare saboda cikin jikinta da ke girma ba zanso barin ta nan ta haihu bana nan ba.
Hjy bata bari yakai zancen ba ta bude baki tace karana ke nan kakai wurin iyayyen ka ko ?
Hjy kiyi shiru nan ai yanzu ba karan ki ya kawo ba inhar kina da laifi zancen Alh dai muke son jin manufarshi nayin wanan hukuncin daya yanke ?
Kawu ya dago kai yana sallama kafin ya fara fadin lalai nayi hakan ne kan a zauna lafiya don banyi wanan abin da wani manufa a raina ba sai don karin zumuncin dake tsakani na da yan uwana koda bayan bana raye ne.
Sai kuma wanan yaron da ya dauko muna yar ahalulkitabi a matsayin mata yazo min da ita na duba gaban sa hakan ba zai haifar mashi da alfanu ba a rayuwan shi nan gaba
Liman yace haka Allah yace ayi Alh hakkun kayi gaskiya sai kawu yace ashe ni ban sani ba ita hjy yin hakan har wanan lokacin bai mata dadi ba.
Kai balarabe da mustapha ga baba nan zaune da ranshi tsohon yana jingine da sandan shi baiyi magana ba har lokaci kai kawai ya kada masu.
Ba zabi da baki na basu ba takarda na watsa da sunayen yarana mata da nake da niyar basu a lokacin diyan ya uwana.
Koba haka akayi shi a falin nan ba ya sake tambayan su suka amsa da hakane.
Yace daga baya jimmai ta tuma ta kafe bata yarda da auren shi umar ba da yarinyar nan tun kafin in basu takarda saida na kafa sharadin idan jummai tayi korafi akan auren nan a bakin auren ta.
Subbahanallahi liman ya furta kawu yace kwarai anan falon na fade shi gaban kowa jin haka jimmai ta yarda da hakan ta amince.
Saidai ashe bansan da manufa ta amincewa hakan ba azuciyanta na dauka daga ta fahinci abinda na hango nayi wanan hadin daga baya.
Saidai ashe ita a wurin ta ta dauki wanan abin gaba tsakanin ta da maimuna gata nan.
Yakai bayan yaron nan ya wuce da mayarshi ashe ta kafa mai sharadin banza kan idan yaje ya sako muna yar mutane da akai min alfarma aka dubi mutuncina akabamu.
Ita mai diya mace da aka cuta tana karama sosai a lokacin a???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?ka ba danta batayi koraglfin haka ba sai jummai ne zata kasa hakkuri ta rugumi kaddara har yakai yaran nan sun haifi diya uku acan batare da sanin mu ba anan .
Kullun na kira saidai suce suna lafiya yana zuwa kasan nan ya koma ba tare da ita ba duk bai fada muna sun samu karuwa a tsakanin su ba .
Ashe duk gudun mahaifiyar shi taji wanan yakw boye muna hakan koda suka dawo hakkurin hakan kawai ya bamu a lokacin nayi fada sosai dashi daga baya na fahinci abinda yake nufi da hakan.
Sun dawo gida fitinan mahaifiyar shi kan yarinyar nan sai karuwa yakeyi bata bar masa mata ta zauna lafiya ba haka kuma bata bar kishiyan ta sun zauna gidan nan lafiya ba.
Har takai ta kwashi yan uwan ta zuwa gidan yaran nan tayi tataki kan ta shirya zata aurowa danta mata da take bukatan shi da ita a duniyan nan.
Ba wani ya fada mun ba ya ciro wayan shi yana laluben yace kai balarabe shedane tare tsohuwar mu ta kiramu ta nuna muna video nan da yarinyar nan murja ta dauko na cin mutuncin da sukaje sukayi a gidan wai sunzo duban dakin da zasu saka yarsu.
Wanan dalilin yasa na kira yaran nace kowa ya dauki dan shi a zauna lafiya duk da na fada mata kafar yarinyar a gidan umar gashi fitan ta gidan nan nawa har abada ke nan.
Naga alaman ta amince da hakan kuma a zuciyar ta tunda zaman yarinyar nan gidan nan ba wani sauyi da suka samu kullun fitinane da uwar yar nan.
Har yau ban taba kiran su da sunan maimuna takawo min karan jimmai ba gata zaune amma ita a kullun cikin korafi take anmata dai an mata a gidan nan.
Kawun hjy ya nisa a lokacin yace jummai amma baki biyo halin mu ba wallahi tir da Allah waddai da wanan halin naki.
Keda kanki zaki hana rayuwan danki zaman lafiya don wani kudirin ki na baza can da kika sa azuciyar ki gareki wai farau kishiya jummai ?
Kawu da kubar wanan zancen don yarinyar nan ba zata koma gidan umar ba har abada shine abinda na yanke akan maganan nan mamu tace.
Kowa na falon ya kallo ta don jin abinda ta fada tace kwarai kawu hakkurina ya kare a kan hjy tunda kan auren nan yakai har hjy ta kira min da mahaifiyata da yar yawon duniya.
Subbahanallahi hjy da girman kike wanan furcin ga yar uwan ki ya kasance hakan gaskiya ne ai ba fade yakamata ki mataba illa shiryuwan Allah gareta.
Kawu balarabe yace a ina wanan zancen ya fito haka mara dadin ji kuma ?
Liman ne ya katse su da fadin salamu alaikum suka amsa masa yace da farko wanan al,amarin baiyi dadin ji ba ace babban gida irin na Alh mutumin da duk unguwan nan yaro da babba ake ganin mutuncin sa yau ace a halin sa ne ke wanan irin rikicin kamar gidan da babu adini a cikin sa.
Alh kaima kana da naka laifin a wani bangare a ina ka taba jin iyayyen sun samu ikon kwatar yarsu a hannun mijin ta ?
Wanan sai idan shi mai auren ya bude bakinsa yace bayayin auren ya fasa wanan ba sauran abin yi sai a raba auren.
Yanzu duk mu bar wanan zancen tunda ga ma,auratan a zaune gaban mu ya juya ya kalli yaya yace Umar Faruq kazo tafiya da matar kane a yanzu ?
Cikin ladabi yaya yace abinda nake so ke nan idan hakan zai samu a yanzu.
Amma idan zai tafi da ita sai an bani dama ya karbi nawa bukatan auren yar wurin sabuwa da nake son yayi.
Da sauri kawunta yace bukatan auren diyar sabuwa jummai kina da hankali kuwa a rayuwan ki son kan ki har yakaiki ki halaka kan ki da kan ki yaro suna zaman lafiya da matar shi zaki dauko zancen yar sabuwa da basu da tarbiya ki jefa a cikin ahali ki ?
Kawun nata yai mata tas a wurin yayan ta yana taya shi dole taja bakin ta tayi shiru don babu hanyar yin magana a wurin gareta kuma.
Yace ka dauki matarka ka tafi wanan magana ya kare a wurin nan yanzu don haka idan ka shirya daukan matar ka ka dauketa ku tafi.
Mamu tace ta bishi kuma a haka kawu ku tuna fa ba daku zata zauna ba dasu ne hjy kuma ba fasa abin nan zatayi ba ga yarinyar nan tana fadin haka ta fashe da kuka.
Jikin kowa a falon sanyi yayi a lokacin ganin mamu na kuka nima na fashe da kukan lokaci guda falin yayi tsit ana sauraren sautin kukan namu.
Kawun hjy yace kuyi hakkuri ansan an cuta maku ana makan cutarwa din don wanan bata da alaman fasa halinta tunda ta kulla da sabuwa.
Yanzu ai ga yarinyar nan a zaune itace ke zaman aure ba wani ba yana da kyau muji ra,ayin ta idan zata bi mijin ta su tafi a yanzu din.
Da sauri yaya ya dago kai kalli kawun hjy da idanuwan shi da suka kada sukai ja a cikin natsuwa yana fadin malam kada kuyi haka yanzu a lokacin nan da suke jin zafi da ciwo a zuciyar su don furcin mahaifiyar dataji kuma.
Kawun hjy yace umar ka kwantar da hankalin ka ba zabi bane hakan hakkintane itama za a bata don muji ra,ayinta a kanka yanzu.
Ya juyo gareni yace Fatima kiyi hakkuri ki daina kukan nan kiyayya a filin Allah da tozarci haka baida dadi ko kadan .
Fatima kindai ji hukuncin da muka yanke a gaban ki yanzu shin zaki bi mijin kine ku tafi koko wani shawara kika yanke a zuciyar ki ?
Kaina a duke ban dago ba sai hawaye nake yi ina tunane a zuciyana ra,ayin uwata da take kokarin kwato min yancina a gurin hjy zanbi koko tausayin mijina da yayana da suka koma kamar marayu zan bi yanzu.
Jin malam ya kara kiran sunana yana fadin Fatima ke muke saurare muji ra,ayin ki yasa na dago kai a hankali na kalli inda malam din yake a daidai wurin kuma yaya Umar din shima yake zaune a kasa.
Karab idanuwa na suka sarke a nasa ni yake kallo da jajayen idon sa da suka kade ko kiftasu bayayi a lokacin bashi kadai ba duk wanda ke falon a lokacin ido ya zuba min don jin me zan fada.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
17/11/2021, 07:16 - ??5惙5惙5?: Na sake dukar da kaina a kasa ina dan sheshekan kuka kowa a wurin ya zuba min ido suna saurarena a lokacin.
Azuciyana sai faman tunane nake ba zan yarda in bi yaya a wanan lokacin ba don kwatar wa uwata martsnbata a gurin hjy dake ganin don abin hannun danta mamu ta zuga kawo ya cusa ni gareshi a nata tunanen ke nan ita.
Kowa yasa tsakanina da mahaifiyata akwai shakuwa da yawa wanda har mutane ke ganin bata kawaici a kaina irin da akewa dan fari don shakuwane sosai da aminci a tsakani na da mahaifiya ta.
Don shi kanshi yaya idan muna waya wani lokaci da mamu ya kance min shike nan kun koma aminai dake da mahaifiyar ki don na lura a cikin ki babu wanda take so kamar ki.
Nakan ce mai kasan banda Amma mamu bata da wani wanda suka shaku a baya yanzu ko Amma girma ya kamata dole wani shawaran dani zatayi shi.
Sannan ina tuna da namiji ba dan goyo bane in watsawa uwata kasa a ido yanzu a gaban jama,a yazo uwarshi ta tursasa shi yai auren da take so da wani ido zan kalli mahaifiya ta daga baya.
Kai Allah waddan naka ya lalace kan yar nan duk kabi ka susuce kanka a banza kamar itace autar mata a duniya.
Na rasa mai kagani a wurin yarinyar nan ka juye a lokaci haka babawo har suna daukan kansu su wata tsiyace yanzu muryan hjy ce kewa yaya fada a wurin lokacin.
Wanan ai da gani sun gama da kaine don bayin kai sake bane wanan abin don anga wurin cin banza an mayar da kai shanuwar tatsa.
Kawun hjy yace jummai wanan wani irin kalamai ga danki kike furta wanan magana nan haka a gaban kowa babu dadin ji.
Kawu bari na fada mai gaskiya don Allah idan ba an gama dashi ba zai zaunar damu a nan haka kan wanan diyar makaskanta har ana son a fada min magana akanta.
Don kawai suna kurin sun rabani dashi zaiyi kokarin ya kunyatani a gaban jama, a haka yasa ai min dariya nan gaba kan bijire min da yayi.
Tana aje maganan ta lokacin zuciyana ya gama tafasa da kalaman ta mai daci a garemu tana ganin don abinnhannun shi yasa nake zaune tare dashi ke nan ko

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login