Showing 69001 words to 72000 words out of 419207 words

Chapter 24 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1431

umma manjo ba lafiya may ya samay ta tace daga kafan nan nata daine sai ga abin kuma yana ci gaba .
Ban iya sauraren abinda take fadi ba na fara hawaye sai naji mamu ta karbe wayan a hannuna tana fadin hajiya ashe yar nan nada layin ku ?
Nan suka shiga gaisawa a tsakanin su inda mamu ke fadin ashe jikin babba kuma ya motsa banjin abinda take fadi a lokacin sai mannewan da nayi a jikin mamu don inji may suke fadi a lokacin.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 22:50 - ??5惙5惙5?: :BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHHIM AU,ZU BIKKALAMAT, TAMMA,AT MIN SHHARIN MA, HALAQ, , , , , ,


Tun wanan maganan hankalina ya tashi sosai da jin zancen da nayi na ciwon kakata manjo ran???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?an ko abinci ban iya ci ba dan dama ruwan da nake sha.
Da asuba ban fito yin sahur ba kuma ba barci nakeyi ba raina ke min sake sake a kan ciwon manjo ganin ban fito ba yasa mamu shigowa dakin.
A kwance ta samay ni na lafe sai dai tasan ba barci nakeyi ba lokacin mamu tace haba sayadi sai kace ba musulma ba in banda abinki ai ciwo ba mutuwa bane.
Kuma kowa dole ya tausayawa hin da babba take ciki a garin nan ida ma mutuwa tayi wani ba zai iya tarewa wani mutuwa ba ai.
Don Allah ki tashi kina tayar min da hankali nima da wanan halin da kikeyi kukan ki kara sakani cikin wani hali yake banda natsuwa da zan nemawa babba mafita.
Abinda zuwa islamiya naki ya koya maki ke nan idan bawa ya shiga wani hali maimakon addu,a aita mashi kuka.
Ki tashi kije ga abinci can a falo kici kada lokaci ya kure ki fara wanke bakin ki kafin ki fito kai kawai na iya gyada mata na tashi jiki ba kwari zuwa bayi don ita har ta fita dakin ko ta koma falo.
Dana fito kasa cin abincin nayi na tasa shi a gaba ina kallo sai daga can mamu ta farga da bancin abincin tace bazaki ci abinci ba sai lokaci ya shige ko.
Cikin muryan kuka nace mamu Allah ban iya cin komai a yanzu na koshi wani irin kallo ta watso min wanda nasan kallon warning ne gareni .
Da sauri na mika hannu na dauki spoon din na fara dan cakulan abincin a hankali cibi daya da kyat na kaisa a bakina ina ji kamar guba ta bani don halin da nake ciki a lokacin.
Dubana mamu tayi tace ashe ba zaki wa kakarki addua ba idan da mutuwa tayi ko kin rasa wani daga cikin mu sai kuka.
Da kyat na iya bude baki da muryan kuka don a lokacin ji nake dai Manjo ta mutu ko don yadda naji maman Atika nawa mamu dogon bayanin da banji ba.
Mamu ban iya ci na koshi sai ta miko min kofin tea mai zafi danaga ta hads tun zamana ta aje gefen ta na karba babu mussu na kafa kai na zuka kadan na aje kofin.
Don banga amfanin cin wani abuba a lokacin masoyiya ta tana can cikin wani halin ciwo da ban san iyakar shi ba.
Maimakon inyi magana sai na fada jikin mamu ina kuka gwaunin ban tausayi ina fadin mamu banda kowa daga Allah sai ku bayan ke da manjo na .
Kai ki daina fadar haka sayadi ina kika baro Alh da Amma da suke nuna maki kauna na sahihi in Allah ya yarda ba abinda zai samu babba ina jiran gari ya waye ne in samu su gwago da maganan inji yadda za a yi.
Wanan kuka haka kina sare min gwiwa da shine sanan Alh ba zaiji dadin wanan kalamin naki ba bayan kokarin shi da yakeyi a kanki yana gwadawa duniya ke yarshi ce ta cikin shi.
Nayi alkwari muddin ina raye sayi ba zan taba barin kiyi maraicin mahaifi ba zan baki duk wani kulawan daya dace duk wata uwa ta gari ta baiwa yarta.
Ina rokan Allah ya haskaki a idon zurin an ku baki daya amma fa sak idan kin taimaka min haka zai samu gareki.
Duk da nasan kina da tarbiya sai dai ki kara kula yanzu da da ba daya bane a gare ki saboda haka ki kawar da idon ki aurin kula samari don nasan ko baki kulasu ba su zasu kula ki
Ki fita batun duk wani da namiji ki mayar da hankalin ki wurin karatun ki sosai don da kin gama ki samu gurbin shiga jami, a.
Don Allah ki kiyaye ki kare mutuncin ki ga kowa da idon shi ke a kan mu aga yadda zamu kwashe nan gaba da rayuwan mu a gaban ki yaya take fadin haukanta a kan yaran ta .
Ta manta Allah ke yi ba mutum mu tasan abinda gobe zai haifa ga namu yayan ba don haka fatima kiwa Allah ki natsu akan tarbiyan dana doraku akai.
Dagowa nayi da sauri na kalleta da mamaki don jin kiran sunana da tayi a karo na farko ke nan da naji ta ambaci sunana na yanka a bakinta .
Insha Allahu wataran sai labari da yardan Allah sai kin zama abin kwatance a idon jamma,a koda kuwa bana raye .
Allah yai maku albarka ya kare min ku daga duk wani abin ki, ya azurta min ku da ilimi mai amfani ya baku mazajen aure masu albarka da sanin ya kamata.
Da kyat ta kai maganan don muryan ta da ya juye zuwa na kuka Allah kadai yasan abinda mamu ke ji a zuciyar ta akan mu.
Gashi ba wasu dangin mahaifiya ke gare ta ba tun da mahaifiyar ta suka rabo da mahaifinta ta koma kasan su basu kara jin labarin ta ba har yau.
Nasiha mai ratsa jiki mamu tayi min wanda ya kara min karfin gwiwa da sanin matsayina yanzu a duniya wanda ya zama dole inyi taushi ko don kwanciyar hankalin mahaifiyata mai son ganin farin cikina itama a duniya.

Ban kwanta ba sai da nayi sallah na samu batci mai nauyi ya dauke ni can cikin barci na nake jin muryan kawo na mijin mamu yana fadin ina ita sayadi din.
Tana ciki tana barci nasan sai yanzu ta samu barci a yadda ta kwanta a jiya yace tayar min da ita .
Itama matar da ta fadi wanan bata kyauta ba bata ganin fatima yarinya ce kamar da zata sanar mata da wanan magana sanin yadda suka shaku da kakan nata.
Barcin data samu ne yanzu don nasan ta kwana tana kuka jiya yace kin gani ba wanan ai ba sakon yaro bane wasu haka suke basu da tunane.
Mamu ta shigo ta tayar dani na samay shi tsaye a falo yana jiran fitowa na daga daki na fito na dan rusuna ina fadin kawu ina kwana ?
Ya amsa min fuskanshi ba yabo ba fallasa yace har yanzu kukan kike yi fatima ?
Haba fatima ai ciwo ba mutuwa bane daina damuwa insha Allahu zata samu lafiya abubuwa ne sukai min yawa yasa na shagala da zancen kakanki a raina.
Murya Amma ne ke shigowa part din mu wanda zance duk zuwa na gidan baifi sau biyu ba data shigo part din sai kuma wanan karon.
Tana shigowa tace ashe kana nan yanzu maimuna ke fada min yar nan she kakanata jikin ya motsa kuma a can.
Ta juya wurina tana fadin haba A ruwa kiyi hakkuri ki daina kuka ciwo bawai an rabo bane gaba daya daurowa yake idan Allah ya saka ma bawa lalura sai addua yanzu.
Hawaye masu zafi suka zubo min wanda ban iya bambance na maynene ba ko na ciwon manjo ko kuma na irin so da kaunan da ake nuna min a gidan kawuna tsakan shi da mamu da Amma.
Wanda ada ba debe tsamanin samun irin wanan kulan na mahaifa a gareni sai wurin mahaifiyar uba da take kulani ita kadai wanda kesa nake ganin banda kowa a duniya sai ita.
Tashi ki shiga ki kwanta abinki tunda akwai barci a idon ki kawu ke fadi na mike tsam na nufi dakin kwanan namu.
Barin wurin keda wuya baji mamu na magana kasa kasa sun dan dade a wurin suna tataunawa wanda ban sa may suke magana a kai ba lokacin can dai har na daina jin su ko don barcin daya dauke nine lokacin.

Amma da ta fito daga part din mu tana komawa ta samu Aliyu da umar a falon ta sun shigo gaida ita basu samay ta ba.
Tana shiga ta gansu a zaune kowa hankalin shi yana ga wayan shi ba maima wani magana a cikin su.
Da sallama a bakinta ta shigo part din kamar yadda tsofi keyi a duk inda zasu shiga wuri koba kowa sai sunyi sallama a guri.
Dago kai sukayi suna amsa mata sallaman ga baki dayan su Aliyu yace ji wanan tsohuwar ke da baki da kafa ina kika je da safen nan haka ?
Tace bari kaidai yar nan A ruwa ce aka bugo wanan wayan wai kakarta mahaifiyar ubanta bata da lafiya.
Waye kuma keda wanan sunan banzan wai a ruwa ke yanzu har kina da kafan shiga makwabta a hakan.
Kaji ja,iri sai ana maganan kwarai ya jefo shirmay yar nan mana yar gurin maimuna na dake gidan nan.
Ba wanda ya amsa masu daga ciki ita kan taci gaba da fadin wallahi abin akwai tausayi yar kaka wace take gani taji sanyi yanzu kuma ance kafa ba lafiya gara ni ai tashine aiki a wurina yanzu.
Haba Amma ko gausawa bamuyi ba kin damay mu da zance wata wace bamu da hadi da ita a wurin mu.
Dan nan kana da imani a ranka kuwa Amma ta tambaya cikin mamaki da bata fuskanta.
Yanzun kai ko tausaya mata bakayi a matsayinta na tsohuwa balle ace yarta jinku ce ita aiko don yar uwanku ka tausaya mata da addinin ka.
Ke kowa fa ba irin ki bane sarkin tausayi haka kawai kina kokarin lika muna yarinya a jiki don kawai wani alaka can.
Haba please kasan may kake fadi aiko don zamanta a gidan nan ko yar aiki ce zamu tausaya mata balle yar maimuna ce fa yarinyar.
Ku daina irin wanan maganan please ya karasa yana maida fuskan shi a wayan shi sai Amma tace.
Fada mashi dai dan albarka shiya nake kara son ka saudaki don ka biyo ni sak wurin fadin gaskiya da tausayin mai bukatan a tausaya mai.
Ni da banda tausayi sai kisa a rufeni ki daina ganina a duniyar nan ga baki daya .
Wai ba abinda habbib ya karato ke nan ba Amma matar tana ina ne sai ya duba ta ido Aliyu ya zaro waje da sauri yana fadin wani habbib din zaije aikin kalar dangi.
Dakuwa ta nuna mashi da hannu tana fadin kaci gidan ku yaro ana baka kana roko idan baiyi ba abu na kudi sai wasu suyi.
Ke ma dai kinsan habbib bai wanan aikin don bai fara duba kowa ba a kasan nan balle ya fara da tarkacen ki.
Wai wanan dan may ka dauki duniya ne kadai bi duniya a sannu don Allah bani fatan haka a cikin zurian dana haifa.
Rashin imani da tausayin mabukaci ba wanda yana cikin abinda ke kai mutum Aljanna idan an dace anyj wurin daya dace din.
Amma don Allah dai ki barshi zanyi magana da habib din ansan abin daya dace a kai tace sannu dan albarka yadda kake da zuciyar nan ubangiji ya tausaya maka ya jibanci al,amuran daka sa a gaba duniya da lahira yasa maka albarka ga zurian ka ya baka mata tagari mai irin zuciyar ka.
Yace Amin amma na gode Aliyu zaiyi magana ya daga mai hannu yana fadin please please ka barta hakana kana sa kaina yana ciwo wallahi .
Yana fadin haka ya gyara ishishirewa saman kujera yana dafe kanshi da hannun shi daya mikewa Aliyu yayi yana fadin ke dama ba a zuwa maki abin arziki ni kinga tafiyana .
Lokacin ya cire hannu a goshin shi yana fadin jinan kada ka fara ka tari habib da wanan magana yace naji bros ya fice.
Ban san yaya akayi ba sai kawai naji ranan mamu na magana wai za a dauko manjo a dubata a nan kano ranan murna a wurina ba,a magana ina Allah Allah gari ya waye in bude ido inga manjo don ance Addah ce zata zo da ita.
Washe gari basu iso ba sai bayan la,asar Ahmed aka tura ya dauko su tasha daga shagon su ko gida baizo da ita ba don yanayin daya ganta ya wuce asibitin da akai bucking da ita daga can .
Sai zuwa yayi yake fadin abinda ya faru a can mamu ta samay su bata fada min halin da ake ciki ba don kar hankalina ya tashi.
Azumi yana damuna gashi na gama girkina mamu ta fita ban san inda taje ba sai shirun yayi min yawa na yanke shawaran muje part din Amma kafin lokacin shan ruwa yayi.
Muna shiga ban kula da mutum a falon ba na nufi inda Amma take ina zhwa na kwanta saman jikin ta ina fadin Amma zumi ga mamu ta fita tundzun bata dawo ba.
Idan ta dawo wani abin zatai maki na gyara kwanciya saman jikinta nace wallahi Amma yau akwai azumi sosai.
Ta dan turani tana fadin ke dallah ja can raguwar banza da kike hawan jikina an fada maki ni ban azumin ne halan ?
Muryan namiji naji a hankali kamar yana rada nayi saurin juyawa wurin yana zaune yana waya jikin shi saye da yadin shadda mai laushi da maiko brown color saj walkiya takeyi.
Tun ganin da nake mai da yazo wanan karon na ganshi a cikin kayan mu na gargajiya sai na rasa da kayan mu dana turawan da yake sakawa wani yafi mashi kyau a lokacin.
A hankali na mayar da kaina baya ban kara kallln shi ba abinda naji yana fadi da harshen turancine ya dan girgizani.
Mace mai suna merry yake waya da ita sai dai wayan nasa kalaman rarashine ne yake mata inda yake fadin tayi hakkuri ya karasa abinda yazo yi.
Sai kuma ya tsaya dan saurarenta can naji ya fadi a dan tsawace kada ta soma ta biyo shi nan ko ranta ya baci saurin juyowa nayi na dan kalle shi yadda yake magana a hasale kamar mai fada da dan shi.
Nace a raina shegu sun gama watsewan su a turai sai da suka gaji suka dawo gida kilama abokiyar shashancin shi ce ta matsu ta kirashi yanzu.
Bankai karashen tunane ba naji muryan shi yana fadin Amma zan je masallaci lokacin sallah ya kusa tace a dawo lafiya dan albarka.
Yana fita naja tsuki ina fadin kamar na Allah da sauri amma ta juyo tana fadin wa nace wanan jikan naki mana Amma.
Yanzu fa ya gama waya da mace a gaban ki kuma baki masa fadan haka ba tace lah ha,ila ha, illah yanzu yar nan ki rasa wanda zakiwa sheri sai dan nan ?
Sherin may kuma amma inji abu da kunne na kice min sheri da wata merry arniya fa yake waya a gaban ki dan gwara takai min a kai tana fadin lalai yar nan kin iya sheri.
Na mike ina fadin don na fada maki gaskiya shine zaki dangware ni bari ki gani idan na sake zuwa wurin ki duk abinda kikaga dama ki mun.
Na mike tana kirana naki koda juyowa yan kanne dake a takure rashin sanin inda mahaifiyad mu ta tafi suka biyo ni a baya.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 22:50 - ??5惙5惙5?: BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM, LA, ILLAHA ILLA, ANTA SUBBAHANAK INNI KUNTUM MINAL ZALUMIN, , , , , , , , , ,



Mamu bata shigo ba sai bayan shan ruwa koda ta shigo bata wani tsaya ba sallah tayi tare da umurtana in biyo ta kitchen.
Sai nake mamakin mai kuma zamu hadda da daren nan bayan mun kammala abincin ranan da zamuci har asuba.
Kuloli ta jawa ta miko min in wanke bayan na wanke ne naga tana ta faman zuba abinci a cikin kulan tare da fadin in zuba ruwan zafi a flask.
Muna gama hadawa Ahmed ya sallama mata tare da shigowa falon namu ina zaune takure saman one seater na dunkule kafafuna a saman kujeran na takure a wuri daya kaman mai jin sanyi.
Shigowan shi bai sa na canza zaman da nayi ba kamar wace ke a cikin damuwa ina ganin shi daga inda nake zaune na gaida shi.
Naji mamu na fadin ka iso ashe yace banje nisa nan muka sha ruwa da Alh a falon shi don kada mu makara.
Bata wani tsaya ba ta kallo inda nake zaune tana fadin ku tufe part din nan idan nafita in na dawo zan buga maku.
Na amsa da to kawai suka fita ya karbi kayan abincin ina mamaki a raina ko may suka samu

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login