Showing 228001 words to 231000 words out of 419207 words

Chapter 77 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1401

shan wankan larabawa mai take Allah Allahu ya baba asalamulaikum ya, , , ,
Shi nake saure a lokacin ya shagaltar dani saboda dadin wankan da nake ji ina dan kurban lemon dana tsiyayo a cup a hankali idan na kurba in mayar da hankalina ga titi .
Tsaye yake yana karewa yanayi da nake cikina nishadi kallo banda damuwa a tare dani yanzu ko kadan.
Yana mamakin sauyawana da sakewa a dan lokaci kankani duk yaga komai ya sauya daga bangare na.
Wani irin tausayina yaji ya rufe shi lokaci guda yasan yana danne min hakkina da komai amma daidai da rana daya ban taba nuna mashi hakan yana damuna ba ko a fuska.
Na dago ido na dan juya don jin kamar mutum a tsaye bayana sai nayi arba dashi tsaye ya saka suith a jikin shi ash clour yana tsaye ya saka hannayen shi a aljihun wandon shi ya zubo min idanuwan shi.
Dama naji hakan a jikina ana kallona da sauri nakai kasa ina fadin yaya ina kwana.
Mai hali baya barin halinsa kamar bashi bane ya gama tausaya min yanzu dan harara ya galla min tare da fadin .
May kike a nan kuma mutane suna kare maki kallo a haka da kika fito ?
Yana fadin haka yaja guntu tsuki tare da juyawa yabar gurin ya koma ciki cike da takaicin da bai san dalilin yinsa ba.
Bayan shi na galawa harara ina mai takaicin yadda ya tsaya na kare min kallo a fakaice gani kaina babu ko dan kwali lokacin.
Ban bar wurin ba saida na kare shan lemona da kallon wasu yara masu tseren keke a gaban gidan mu.
Na shiga falon bai ciki gurin labulen gaban gidan naje na daga na hango shi yana kokarin shiga motar shi .
Ya hanani tsayawa idanake ganin mutane shi kuma ya fita ya barni kamar manya a gidan ni kadai na fadi a fili.
Ni kadai a cikin gida sai faman mita nake kai kace da wani nake zance a cikin gidan wurin tv dake falon na nufa na kunna.
Ko wani tasha nasu nakai babu abinda sukeyi sai hasko bukin wasan kirisimeti da sukeyi .
Haushi naji ina fadawa saman kujera na kai kwance tare da lumshe idanuwana take zuciyana ta anyana mun shiya dawo da yaya umar kasan nan.
Zubur na mike nakai zaune tare da fadi a fili tabbas abinda ya dawo yi ke nan don matar shi waya sani ma ko shima chocin yake zuwa.
Kai amma ko idan hakane anyu hasarare a gurin nan ya zama dole inbi kwakwafin takon shi in gane ko yana cika sallah shi.
Taya zan gane hakan na tambayi kaina mutumin da kullun yake faman daure min fuska kamar baisan inda na fito ba.
Ta yaya kawu zai dauka harni zan iya gyara mai akidun shi bayan baya son kowama ya rabe shi sai wanan kafirar matar tasa.
Nasan akwai abinda mijin anty farida ke son fada ranan gamay dashi sai kuma yayi shiru bai fada ba koma may ye shiya sani nidai in samu in karasa karatuna in koma gida kawai don ba zan yarda in zauna kasan da bansan kowa ba inta rayuwan kadaici saboda shi.
A ranan nasha mamakin makwabtana don kusan mutum uku suna kwakwasa kofa suna kawo min charismas gift har gida ina godiya ba wani abu bane sai cake da sukayi da sauran irin su sweet da biscuit.
Mamakin hakan nayi sosai a raina don tunda nake dasu ni wani gaisuwan kirki bai taba shiga tsakanina dasu ba ma sai gashi duna buga min gida suna kawo min kyauta har gida don kulawa.
Shiko yaya tun fitan shi ban kara ganin shi ba yau kwana biyu ke nan sai dai dama na kudurta a raina wanan karon idan yace zan tafi can dayan gidan nasa wurin su merry zaisha mamakina don ba zan tafi ba yin bukin shedanci.
Da zaman ya isheni ni kadai a gida na ina jin kamar zan kamu da ciwo don haka na shirya tafiya gidan anty farida in kai masu yawo.
Saidai nayi rashin sa,a sunyi tafiya wata makwabciyarsu yar kasar lebonon ke fada min sai lokacin na tuna amfanin waya ashe dama kiranta nayi inji ko tana gida kafin inzo.
Dama da kafa nake don in motsa jikina haka na tako da kafa na kamo hanya ba gida na nufa ba dayan hanyan nabi da kafa ina kallon gari.
Naji dadin wanan fitan don naga mutane gungu gungu suna wasan ni a layin da kama layin na talakawan garine ko dai wani wurin nishadi.
Haka nayi tabin layin ba tare da nasan takamaimai inda zani ba can naci karo da miji da mata suna tafiya a hanya kamar a mafalki naji suna yaren hausa a tsakanin su.
Sam basuyi zaton zanjisu ba matar tace iko Allah su kuma a haka wai bukin murnan sallah sukeyi haka wai ?
Mijin yace kin san abinda ka yard dashi ko aka haifeka a cikin sa ban san lokacin danace sannun ku da hutawa ba .
Gaba daya lokaci guda suka juyo suna kallona dan dattijon yana kare min kallon mamaki saidai yanayin shigata nasan bana banza bane nayi lokacin.
Na sake fadin ina wuni ku har lokacin da mamakina karara a fuskan su suka amsa min kusan lokaci guda.
Da barka dai yan mata kema kin fito bude ido ke nan ko matar ta tambayeni ?
Eh hjy zaman kadaici ya damay ni na fito kawai inga yanayin bukin su na bata amsa tace ayyah akwai kadaici tundai a irin wanan lokacin da suke zaman gida suna shagulgulan su ta wanan shirmay nasu wai bauta.
Mijin yace kada ki zake da yawa don ita din baki san ko wacece ba Ramla ya fada yana tsareta da ido.
Nace a a ha baba ni din ma musulmace yar uwar ku sunana fatima daga Nigeria nake nazo karatu ne nan kasar tare da yayana gidana yana bayan layin nan kadan.
Kai amma ko nayi murna da haduwa dake yan mata zaman kadaici ba dadi ke gareshi ba tundai a irin wanan kasashen na turawa.
Nayi murmushi saboda jin kalaman matar ganin kamar mijin bai yarda dani ba yasa nace nagode da dan lokacin da kuka bani zan tafi sai watarana idan Allah ya sake hadamu kuma.
Da sauri matar tace haba haba yar uwa tun yanzu aini ina ganin ki kamar naga wata ta gidane wallahi.
Muma daga Kasan ghana muke sai dai shi maigidana dan Nigeria ne don yafi zama a can kowa nasa yana Nigeria sai mahaifiyar shi ce yar kasar ghana.
Ba zaki tafi ba tunda kina ke daya a gidan ki kizo mu zagaya a tare muyi kallo ikon Allah wai kin san al,adun su na gargajiya abin mamakine sosai.
A yadda na fahinta matar tana da son hira sosai da kuma son mutane sai nake tunane duk wanda ke wani kasa haka yake idan yaga dan kasan su wani gari.
Ranan naji dadin wanan fitan don na sake jikina sosai mijin matar ya kaimu wurin cin abincin mai kama data kasan mu kowa yaci abinda ranshi ke so.
Har gida suka dawo dani sai da sukaga shigata gida suka ja motar su suka tafi sai lokacin naji wani irin ba dadi don kamar kada su tafi su barni naji lokacin.
Ina kokarin juyawa mukai ido biyu da yaya umar dake tsaye cikin damuwa a kofan gidan hannayen shi duka biyu suna saye cikin aljihwayan shi na wandon jikin shi.
Dan raza nayi kai kace wani abin tsorone a gabana lokacin yana huci yana cika yana batsewa sai lokacin na saita kaina nace sannu da zuwa yaya kamar kullun .
Ke dakata daga ina kike wa yan nan mutanen kuma su waye su da suka sauke ki ya tambaya cikin daga muryan shi.
Mun fita cikin gari ne na bashi amsa sunan ta anty Ramla mun hadu dasu ne a garin nan.
May kike son zamane Zarah kina son ki zama watsartsane a garin nan komai ?
Naji zafin kalaman watsartsar daya kiramin don haka bansan lokacin da zafin rai yasa nima na daka mai tsawa ba kamar yadda yai min.
Nace kai yaya ya isheka haka nayi maka kama da mara tarbiyane a shiga ko kaga wani abin Allah waddarai a tare dani.
Ka sani koda bani gaban iyayyen mu nasan abinda nake don ba tarbiyan banza sukai min ba ban kuma taso naga ana abin asha ba a gidan mu balle inzo nan in koya a garin mutane.
Yaya kake son inyi da rayuwata yaya ka daukoni kazo dani kasan mutane ka watsar dani ba kulawa ba komai nima fa mutumce yaya da dole ina bukatan wani a tare dani.
Banki duk yadda kace min ba ina kokarin ganin na bi duk wani dokan ka na tsare shi yanzu kuma zakace kada in fita in ga mutanen arziki.
Na sani da sunan aure muka bar gida amma kaida bakinka yaya kace kada in sake in nunawa wani a kasan nan akwai aure tsakanina dakai.
Duk da nasan hakan ba gaskiya bane ina kokarin nunawa kowa kai yayanane najini karatu ka kawo ni yi kasan nan kamar yadda kake son in nuna din.
Ko zanyi iskancin da kake zato inayi din da mata da mijin ta zanyi yaya ?
Ido rufe nake magana duk cikin bacin rai yasa bansan ya karaso inda nake ba sai jin saukan mari biyu masu kyau naji a fuskana.
Dafe fuskan nayi yayin da nake duke na kasa dagowa sai can na iya dagowa na kalle shi yana tsaye yana huci akaina.
A hankali na ja kafana na tura kofan zuwa ciki ban tsaya a falo ba na hausama inda dakunan kwanan mu suke.
A hankali na tura kofan na shiga na mayar na kulle nasa sakata gadona fada na nemi farin ciki da nishadi dana dawo dashi na rasa a lokaci daya.
Rutse idona nayi a hankali na furta mamu wayyo Amma wayyo ni manjona da wani irin karfi.
A daidai lokacin da yake rufo gidan yaji wanan karan dana sake lokaci guda daga kai yayi ya kalli kofan zama yayi saman kujera tare da kokarin sasauta tie din wuyan shi.
Ya mayar da kanshi saman kujera tare da runtse idanuwan shi wayyo mamuna don Allah kizo ki kwace ni a hannun wanan azzalumin kafin ya kasheni.
Abinda ya shiga kunnen shi ke nan, kai ya girgiza ya ya kara runtse idanuwan shi zancen kanin shi Aliyu ya tuna yaya matse zai iya sa ta dauki matakin da bai dace dakuba.
Ba wai ina nufin tursasaka akan iyalin ka bane a a ya kamata ka rage wasu abubuwan da kake mata itama fa yace kamar kowa.
Why ba doki wanan yarinyar yaya akayi har nakai hannuna a jikin ta ya dade zaune yana tunane barkatai.
Kafin ya mike ya hausama tun a matakalan yake jin sautin kukana a kunnuwa shi wanda yake jin zuciyan shi na kara tabuwa da baci a lokaci daya.
Har ya tura kofan shi zai shiga yaji na kara fadin wayyo mamu na zai kasheni zai kasheni a garin mutane sai ya dauka waya nake a lokacin.
Fasa Shiga yayi dakin nasa ya nufo nawa dakin ya tura kofan ya jishi a rufe gam.
Ya tura ya tura yana rufe juyawa yayi ya koma inda ya fito har lokaci yana jin wani iri a ranshi ba dadi.
Da kyat na iya tashi nayi sallah isha,i ban tsaya cire kayan jikina ba ranan haka na fada kan gado tun ina tunane har barci ya dauke ni gurin ban sani ba.
Washe garima haka na falka da bakin rai yinin ranan ban fita daga daki ba ina daki ko falo banyi gigin lekawa ba.
Komai ban saka a bakina tun safe har ukuna rana ban fito ba bandamu da sanin ko yana gidan ko ya fita ba lokacin tunda zuwan shi ko zaman shi gidan sai yaga dama ko yazo yin wani abin da yake sirine gare shi zai shafe lokaci yana dakin yana aiki da laptop din shi.
Kadan kadan yake dago kai ya kalli hanyar benen kamar may kallon wani abu ba komai yake kallo ba sai fitowa a lokacin tun safe yake zaune a falon sallah ne kawai ya tayar dashi yana idarwa ya dawo ya sake zama gurin.
Jin shiru ban sauko ba har lokacin yasa shiikewa yahau benen kofa ta ya nufa ya tura har lokacin a rufe kofan yake.
Nocking ya fara yi tun yana yi a hankali har ya fara duka da karfi yana kiran sunna na ina jin shi naki budewa.
Ko dagawa banyi a inda nake ba ya kara kiran sunana da karfi yana fadin ki bude kofan nan ko in karya in shigo dakin nan in saba maki nan ma ba amsa sai shiru.
Hankali shi ne ya tashi sosai yana ganin kamar wani abu ya samay nine don marin da yai min din.
Tun yana fadin zarah zarah har ya koma fadin Fatima nace ki bude kofan nan karna karya shi.
Jin shiru ba amsa zuciyar shi ta fara kaduwa da fargaba a lokaci daya.
Ya koma yin magana cikin marairaice murya yana fadin kiyi hakkuri zarah ki bude kofan ba dukan ki zanyi ba .
Ina jin shi na kasa tashi saboda yanayin da nake jin kaina na yunwa da kukan dana sha kaina da jikina gaba daya ina jin su kamar ba nawa ba.
Muryan shi na kara ji cikin wata marainiyar murya yana fadin zarah don Allah ki bude kofan nan ko hankalina zai kwanta kinsan amana kike a gareni kasan nan.
Nasan nayi maki ba daidai ba don Allah ki bude kofan nan hankalina a tashe yake da rashin fitowan ki daga dakin nan.
A hankali jiki ba karfi na dago daga kwance tare da sauko da kafafuwa daga saman gadon da nake kwance.
Jikina ba karfi don yunwan daya ci karfina a lokacin ga kaina kamar zai fashe don ciwon da yake min.
A hakali na bude kofan tare da murda marikan kofan jin ana kokarin bude kofan har ya juya yana shawara a ranshi yakira security din unguwar suzo su balle kofan sai gashi yaji ana bude kofan.
Ya juyo yana kallon kofan da na riga dana bude a lokacin ina kokarin komawa sama gado in kwanta.
Turo kofan yayi da karfi tare da fadowa cikin dakin daidai lokacin dana kai saman gadon ina kokarin zama a bakin gadon.
Wani irin kallo yakewa yanayin daya riskeni a ciki don na gala baita sosai bakina duk ya bushe tun rigan dake jikina lokacin da abin ya faru shine saye min har wanan lokacin.
Ga kaina babu dan kwali gashina dana tufke ya dan barbaje saman kaina har ya zubo saman goshina.
Take yaji wani tausayina ya kamashi ya iso inda nake da sauri yana fadin zarah kina son ki kashe kanki ne kija min magana a garin mutane ko may ?
Sai kuma ya juya zuwa waje da sauri ya dan dauki lokaci har na kai kwance sai gashi ya dawo dauke da kofi yana tururi da ruwan tea a ciki.
Zuwa yayi har kaina ya tsaya yana fadin ki tashi ki sha wanan tea din hanji ya warware.
Kamar badani yake magana na kyale shi ya ja tsuki yana fadin idan baki tashi ba zan dura maki shi ta karfin tsiya yanzun nan wallahi.
Jin hakan nayi kokarin tashi zaune saidai na kasa da taimakon shi na samu na dan zauna a hankali karban kofin nayi jannuna sai rawa yake na dan kai bakina.
Zafi da dacin shayin naji lokaci guda na sauke kofin ba shiri da sauri ki sha mana ya fada cikin tsatsareni da idanuwan shi.
Kisha nace ko in kira ai maki allura yanzun nan tunda haka kike so jin hakan yasa na kara daga kofin ina kokarin kaiwa a baki na.
Na kama kurbawa da dan sauri don ban son alluran danaji ya ambata min yasa na daure ina dan sha badan ina so ba.
Wayar shi ta dauki ruri ya ciro yana kallon wanda ke kiranshi hakan yasa ya dauke kai a gareni ya mayar da hankalin shi gun wayan .
Merry naji ya ambata daya daga waya yana fadin Ina nan mana ina zanje ban fada maki ba wani irin amai ne yazo min lokaci guda na sako shi har wandon jikin shi zuwa kafan shi sai daya taba.
Haka yasa ya fita zancen wayan yana fadin subbahanallahi kinga zaki halaka kanki ko a banza.
Wai wai nake fadi cikin jin ciwon da cikina keyi a bangaren merry tana sauraren abinda ke faruwa sai magana takeyi a wayan shiko hankalin shi yana gare ni.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:20 - ??5惙5惙5?: ALHAMDU-LLILAHI RABIL ALAMIN, , , , ,

Duk kokarin danayi na dagawa kada aman ya kai gare shi hakan bai samu ba don aman ya rigada ya zubo min daga cikin

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login