Showing 87001 words to 90000 words out of 419207 words

Chapter 30 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1489

a gidan nan ai ba sai munyi wani abuba zasuyi iya muna haka tunda so suke su rabamu da gidan ko ta halin kaka.
Idan ba haka ba daga bangaza kawai sai wanan irin marin Ahmed yace shike ban mamaki ai
Don ran Alh ya baci sosai yau shike fada min abin ya taba mai zuciya sosai wallahi.
A to ni dai na fada mai abin ya isheni wallahi dan magana kadan sai a kama min yara da duka sai sun kwata ciwo don ha,inci.
Yace ina fatiman take ne ta nuna da hannu tana fadin tana nan daki tun da ta shiga ta kwanta kila barci takeyi.
Kai shima dai yasan bai kyauta ba tunda yarinyar nan dai batayi mai komai ba idan dai ba dama suna hake da ita bace din don hjy bata da dama yanzu haka wani abin ta fada masu wanda zai sa suki yarinyar nan a ransu don halinta ne na sani.
Mamu tace idan ma ta fada masu ai kansu zai kare sheri dai kare ne maishi yaka bi tsakanina da kowa a gidan nan sai fatan alheri.
Gidan dai take son mu bar mata kota halin kaka shine take kokarin daga min hankali dana yayana.
Dan dariya mara sauti yayi yace yanzu kan ai sai dai ita tabar gidan idan batayi hankali ba don kiris ya rage tsakaninta da Alh yanzu.
Itako abinda Umar ya aikata bai isheta tunane ba gaba dayan su basu da tunane nake gani mamu tace abinda nake son ka gane ke nan.
Ace kishi har da yara a ciki yaran ma maza da suka san ciwon kansu haka ai ko kaga akwai aiki a gaba ke nan.
Ta kalli fauziya tana fadin jeki kira masa anty ku kice ga yayan ku nan Ahmed ya zo dubata.
Fauziya ta mike da sauri zuwa dakin mu ta samu ina barci ta shiga tayar dani daga barcin na bude ido take fada min anty yaya Ahmed yazo gaida ke wai inji mamu.
Sai da nan danyi mintu a kwance na dago da kyat daga saman gadon na sauko kasa na dauki dan gyalena dake gefe na yafa a kaina.
Na fito falon yana zaune yana fuskantar dakin dana ke fitowa daga ciki a ranshi ya ke fadin tsarki ya tabbata ga mahaliccin mu Allah daya halita wanan yarinyar.
Yaga na kara cika nayi mai kyau a fuskan shi na kara cika nayi bul bul dani fatan jikina ya goge yanzu yayi kyau sosai ba kamar yadda nazo gatin ba.
Na koma kamar a tabani jini ya fito saboda gogewan da fatana yayi ga zanen lalen da akai min na sallah wanda ya kara kawata kafana da hannuwa ya fito radau dashi.
Ina dago kai muka hada ido dashi nayi saurin kwantar da kaina kasa na karaso kujeran da mamu ke zaune na tsaya daga bayan ta ina gaida shi.
Gaba daya yaga na sauya mai a yadda ya sanni dana zo tunanen shi yana neman kwancewa a cikin dan kankanin lokaci.
Da kyat ya iya saita kanshi ya karba min gaisuwan da nake mashi yace Fatima yanzu Alh ke fada min kasuwa abinda ya faru dazun.
Ba ina fada maku tunda suka zo gatin nan kuyi taka tsamtsan dasu ba na dan bata fuskana nace ban san suna tafe bani Aisha ce ta biyo ni da gudu sai naci karo dashi.
Yace barsu da Allah ai suma suna da kanne mata ko ina dai bai maki ciwo yanzu ko nace kaina dai ke ciwo sai fuskata dayayi min nauyi dazun yanzun kuma naji ya rage dana tashi.
Duk abinda muke mamu tana zaune tana jin mu sai can tace banace kisha magani ba kafin ki kwanta.
Na sha na bata amsa a takaice a daidai lokacin da Ahmed ke dagawa yana fadin zan koma hjy Allah ya tsare gaba adaiyi hakkuri don Allah watarana sai labari insha Allahu.
Tace nagode Ahmed sannu da kokari yace haba ba komai wallahi danaji ne nace ai barin zo in duba ta idan ba matsala.
Yana fadin haka ya fita har yakai kofa ya kira fauziya yana fadin kuzo in baku goron sallah ku ko ban samu shigowa na baku ba yaran suka bishi sai gasu sun dawo da kudi zaikai dubu goma a hannun su suna murna ya bamu don yace su raba har dani.

Sunyi sa, a sun sami tsohon a gida bayan karfe biyar da suka koma gidan akai masu sallama dashi jin sune yace su shigo falon shi da yake zaune.
Ya tare su da fadin ko dai kunyi batan hanya ne don naji kuna garin nan tun kan ayi sallah sai yau kuka tuna da dan tsoho.
A cikin jin kunyar abinda tsohon ya fadi suka karasa shigowa suna neman wuri a nan take ya umurci wani jikanshi da ya shiga ya kawo masu abin motsa baki a cikin gida.
Bayan sun gaisa ne yake tambayan su bayan rabo suka dai dan taba hira sai dai basuci komai daga abinda aka kawo masu din ba.
Can Umar yace cikin girmamawa malam wurin ka muka zo neman taimakon ka don Allah ka shiga cikin wanan maganan don kai kadai ne yanzu muke ganin zaka iya shawo muna kan mahaifin daga fushin da yake yi dani .
Subbahanallahi may ya faru yake fushi dakai kuma daga dawowan ka kasan nan shi ba abin alfahari bane ganin haka.
Bakuji irin dadin da naji ba lokacin da kuka shigo falon nan yanzu kun zamay muna abin alfahari a cikin zuria .
Aliyu yace haka ne malam sai dai yayan mu yayi kuskuren yin aure a can ba tare da sanin iyayyen mu ba shine tashin hankalin dake tsakanin su da Abban mu yanzu.
Nan dai Aliyu din ya kora ma tsohon duk bayanin komai da yadda maganan ta fara har fushin da mahaifan su keyi dashi umar din.
Subbahanallahi tsohon yace yana girgiza kai tare da fadin innalillahi yaya hakan ya faru kaiko abokina da ilimin ka da tarbiyan ka zaka aikata muna hakan.
A sanyaye Umar yace kaddarace malam kasan mutum duka bai wuce kaddaran shi a rayuwan shi.
Malam Nuhu ya jinjina ganshi kafin ya fara karanto masu ayan Allah yana fassara masu ayoyin alkur,ani mai girma wanda yake magana akan hakkin iyayye da sharian aure.
Bayan ya gama masu bayani yaga yadda jikin su yayi laushi sai ya fara nuna ma Umar kuskuren shi na rashin daukan iyayye da muhinmanci dayayi .
Yace yanzu barin ji inda mahaifin naku yake sai dai ita Amamatan wani mataki ta dauka akan wanan magana sai umar yace .
Itama dai ta dauki zafi da farko amma yanzu naga ta sauko sosai ba kamar farko ba kawu ya dauki wayan suka gaisa yake tambayan shi yana ina ne ?
Yace yana kasuwa yanzu zai koma gida yamma tayi yace a dawo lafiya yace dasu barin shiga ciki in fito mu tafi gidan naku ayishi ya kare can.
Sun yi daidai da kawu ya dawo daga kasuwa ya shiga part din mahaifiyar shi suna gaisawa da ita sai ya tura a kira hjy jummai ta samay su a part din Amma don da ita za ai maganan
Suna zaune sai ganin su sukayi sun shigo gaba dayan su har da kanin mahaifin su kawu din malam nuhu.
A cikin girmamawa Amma na fadin ina kafito da wayan nan gardawan a bayan ka yace to gasu nan dai waya sani ko satoni sukayi.
Aka sa dariya banda su a falon su umar suka zube suna gaida mahaufin nasu yayi kamar bai jisu ba.
Ganin haka malam Nuhu yace bakaji yaran na gaida kai bane Sani ashe abinda naji gaskiyane ba karya ba.
Amma kina cikin gidan nan kika bari abubuwa suna gudana haka aure ne dai yaron na ya rigada ya aikata son ranshi sai ayi hakkuri.
Na fada masa ya aikata babban kuskure to amma abin lura a nan shifa yaron nan dan Adam ne shima kuma kowan ku nan yasan dan adam ajizine bai wuce yin kuskure a rayuwa.
Sai lonacin kawu yai magana yace baba indai maganan yaron nan ne na sallama da zancen shi a raina.
Yaje yayi duk abinda yaga dama a duniya tunda har yake ganin shi ya isa mu bamu isa dashi ba sai dai ya sani duniya ta isa da kowa.
Malam Nuhu yayi murmshi gami da gyara zaman shi yace a daiyi hakkuri tunda ya gane kuskuren shi yanzu.
Ubangijin daya hallice mu ma muna masa laifi idan mun rokeshi ya yafe muna don kai zakace ka yafe shi ma, ana yaje yabi duniya ko ?
Kawu Yace baba haka naga ya zabawa ranshi kamar umar yace ni zai tozarta a garin nan a idon jamma,a.
Aure ne fa sani ba wani aikin shedan ya aikata ba a can sai dai matsalan yarinyar a hallul kitabice ita ko shine zafin ku dashi.
Amma duk da haka idan kukai duba da ubangiji bai hana hakan ba sai a sasauto mashi hakana amma kai ka hau mahaifiyar shi ta hau har ke Amamatan kin hau dashi da sauran iyayyen su.
Yaya kuke ganin karshe zaiyi ai sai ya koma can wurin matar tashi da yan uwanta su karbe shi tunda dama haka suke so.
Nan dai tsohon yaci gaba da lurar dasu duka bangaren biyu kuskuren su ya kare da yiwa iyayyen nasu nasihan suyi hakkri an san ya tabaka kuskure sosai.
Bai kyauta ba inda ya tare su yin magana ya umurci umar da ya kara neman yafiyan iyayyen shi .
Idanu shi suna zubar da hawaye ya mike zuwa wurin ko wanen su yana neman yafiyan su.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 22:55 - ??5惙5惙5?: BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM AR, RAHHAMANIN RAHIM, , , , ,

Haka ranan suka kwana rayukan su babu dadi a cikin sa tun dai na uban aikin umar wanda shine ya dauko maganan.
Washe gari haka suka daka sakko zuwa gidan tsoho inda a nan ma suka samu yayi sammako zuwa daurin aure garin zaria.
Haka suka dawo da haushi a zukatan su na rashin samun tsohon a gidan rayukan su har lokacin babu dadi a cikin ta gashi suma hjy jummai duk ta hade dasu tana fushi.
A guje na fito daga part din Amma inda muka gama gardaman littafi da Aisha ta biyo ni aguje ina dariyan kwace littafin a hannun ta.
Ban san da mutane ba tafe mukaci wani uban karo dana gaban sai da ya dan tangaleni danayi baya zan fadi ga zafin da naji kamar zan kare.
Wani tsawa Habbib dake bayan shi ya buga min don shi ko isar shi kallo ban yi ba yana kamani banje kasa ba ya jaye daga gurin.
Cikin wani irin tsawa habbib din ya ke fadin ke wace irin makaciya ce a daidai lokacin da hannun shi ya sauka a fuskana.
Yaci gaba da fadin ke makauniyace baki ganin mutane a tafe ne da zaki fito haka kamar gidan ub, , , , ,
Kai kai kai haba habbib why da zaka mare ta haka da safen nan kan dan wanan abin haba hakan bai dace ba kana saurin dukan kannen ka mata.
Aisha da ta sandare wuri daya don jin zafin marin kamar itace aka mara ta juya da sauri ciki tana fadawa Amma sai ga Amma a fusace ta fito a daidai lokacin da yayan nasa ke masa fada.
Kai mara mutunci mai wanan yar marainiyar Allah tai maka ka mare ta haka da safen nan don radgin imani da tausayi ?
A hasalen ta juya gurina tana fadin mai kikai masa ya mare ki haka A ruwa cikin rawan murya da idanuwa da suka kawo hawaye nace ban san suna tafe ba na bangaji wanan yayan nasu shine ya mare ni.
Amma habibu ka cika mara imani da tausayi wai ma kai ta bangaza ko shiyan kane nan in sani tana tambayan shi cikin tsatsare shi da idanuwa irin na tsofin da ransu ya gama baci sosai.
Yace a a ke ta bangaza ita bata ganine da zata fito a guje ko tsaban rashin kunya da samun wuri ne haka ?
A gidan ka ta samu wuri mara ta ido nace ko nan din gidan ka ne yau zaka san ka mare ta a gidan nan kuwa yace oho ko zaki rama mata ne don dama ance kece ke daure mata gindi tanawa mutane iskancin dataga dama a gida.
Umar da ya gaji da zancen su yace haba ya isa haka Amma ke kuma ki kula idan kina tafiya da yanzu kin fadi kinji ciwo fa ?
Amma na fadin a a haa wanda dai ya isa dakai zan sa ya rama mata tunda kai kana ganin kafi karfin mu sai jin muryan Alh mukayi yana fadin hajiya lafiya kike fada haka da safen nan ?
Gaba daya suka juya wurin da sukaji muryan suna zubewa don gaishe shi Amma na fadin wallahi wanan mai zubin arna ne ya wanke yarinyar nan da mari tunda safen nan.
Subbahanallahi mari kuma yana yi yana kallona da mamaki karara a fuskan shi ya sake mai mai ta mari akan wani dalili ka mari yar mutane haka ?
Ga shafin hannun ka nan radau a fuskan ta har lokacin hawaye yana zubo min a fuskana iskancin naku da kuka koyo har yakai ku dakan min diya a gidana ?
Fada mashi dai don ni ya tsaya yana min iya shegen daya koya a can don shi bai ganin kowa da ta ido a gidan nan sai daukan kan tsiya da girman kai karshe dai nasan wata yarniyar kai ma zaka kwaso dan wanan halin naka sai su.
Haba Amma kin cika mutane da rigima don Allah baki jin daddy yana masa magana ne wai Aliyu yace haka a hasale ta mika mai dakuwa da yatsun hannun ta tana fadin kaci gidan ku a zulunci yarinya ka hana ayi magana.
Don Allah daddy ayi hakkuri nayi masa fada ai, , , , hannu ya daga wa umar din kafin ya fara fadin nayi nadaman tura ku waje karatu a rayuwata don baku koyo alheri ba can.
Na dan gega kawu dake tsaye zan wuce na kalli umar ina fadin ya umar kayi hakkuri don Allah ban san kuna tafe ba ba da gagan na buge ka ba .
Na wuce naji Amma tana fadin kaji ba nace ko kaji yar arziki ka doketa ta baku hakkuri yanzu bakaji kunyar kanka ba don Allah.
Kamar ka ka mari wanan yarinyar aiko baka san inda ta fito ba taci ragowan matsayin ta na ya mace a gurin ka da badon naji dan uwanka na ma fada ba da sai na rama ma wanan yarinyar marin ta wurun nan.
Ya dago jajjayen idon shi yana kallon ta yace ki rama mana udan kin isa ganin daddy ya kallo shi yasa yayi saurin sauke kanshi da sauri Alh yace ina yanzu idan kuna da hankali kun banbance tarbiyan kasan nan da wanda kuka koyo a can to ba agida za ai wanan shashancin ba.
Uwar yarinyar nan bata kasa daku har yau akan zancen wanan babu irin magiyar da batayi min in yi hakkuri ina facale ta gefe.
Amma ku idon ku ya rufe wurin bakin kishi da uwar ku ta cusa maku a zukatan ku kuna maza nasan idan nayi kukan safe akan ku i??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????tako na marance zatayi don Allah ba azzalumin kowa bane.
Amma da taga fadan yai yawa yana so wuce wuri tace ya isa haka ai ya koyi darasi ita ya zalinta amma ta basu hakkuri ko wanan ya ishe su nadama .
Banga abinda yar nan ta tsare maku a gidan nan ba ko bamu san A ruwa ba yau ai mu masu taimakawa rayuwan tane ko tunda tana bukatan taimako.
Hajiya bance wani ya taimaka min cikin rikon yar nan ba tsakani da Allah na dauko ta hannun iyayyen ta don in tallafawa rayuwan ta don haka ba zan lamunci wani iya shege a gidana ba akan kowa.
Yana fadin haka ya kai kasa daga inda yake yana fadin hajiya mun tashi lafiya duk sai sukaji wani iri matsayin mahaifi su da shekarun shi bai hana shi neman albarka a wurin mahaifiyar shi da Allah ya bar masa raye ba.
Duk sai sukaji sun muzanta a gabab mahaifin nasu duk da dai suna iya kokari su wurin ganin sun kwatata abinda suke gani ga iyayyen nasu wurin girmamawa.
Hakan bai isa shesu mamaki sai jin yadda uwar kewa danta fatan alheri da gamawa da duniya lafiya sabanun nasu uwar da suna gaishe ta tana masu zancen su bata wani abin.
Nan mahaifin su ya juya ya wuce bai kara bi ta kan su ba bayan sun gama gaisawa da mahaifiyar shi din ta juya wurin su tana fadin kun gani.
Har yanzu mahaifin ku fushi yake da dan uwan ku kai kuma kazo ka kara dada wani zancen dukan yarinya a kai.
Aliyu yace a dai ba daddy hakkuri

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login