Showing 57001 words to 60000 words out of 419207 words

Chapter 20 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1510

wallahi.
Na gaji da korafin mahaifin ku a kaina ko yaushe ya debo zugan shi a kan ku wurina yake sauke haushin shi.
May kake son ka zamane babawo kana ko da tausayin mu a zuciyar ka, baza kayi kokarin sauke hakkin mu dake wuyan ka ba sai bayan mun mutu ko may ?
Subbahanallahi mama may yai zafi haka harda wanan maganan in sha Allahu cikin wanan shekaran zan zo gida da yardan Allah kamar yadda na fada maki da farko.
Ka dai ji abindana fada ma kuma gaskiyar magana ta kenan na fada ma yaya kake son inyi da surutun mutane a kanku ne ?
Ko jiya jiyan nan sai da muka kwasa da Alh kan zancen ku har yake fadin don kana takaman kana turo muna da abin duniya kake ganin ka fita hakkin mu ko may ?
Har yake fadin da goyon bayana kake komai don nice na daure ma gindi kake haka may ye a cikin zuwa gida ka gane mu idan kai baka son ganin mu.
Mu iyayyen kane muna son ganin ka a rayuwan mu tunda muna raye bamu mutuba idan kuma dayan mu ya mutu sai kazo gausuwa idan ka samu lokacin hakan .
Jikin shi yayi sanyi yake fadin Allah ya huci zuciyar ki mama insha Allahu zanzo kamar yadda na fada a dai dan kara hakkuri don Allah sai yaji kit ta kashe wayan.
Hakan ya tabbatar mai da ta katse layin ke nan kuma tana cikin fushi dashi abinda bata faye yi dasu ba ke nan indai ta fara yai mata alkawarin makudan kudi yanzu zata aje zancen da take fitina akai.
Sai dai yau an samu akasin hakan don ya lura mahaifiyar tasu ta hau sosai dashi duk maganan da yake merry ta tsura mai ido daga inda take zaune.
Don fahintar da tayi yana cikin wani yanayi kan maganan da yake a wayan saboda yanayinsa daya canza a lokaci daya.
Idan akwai abinda taki ninin ji shine taji ya ambaci zuwa gida yanzu hankalinta zai tashi su dinga rikici har sai taga ya janye tafiyan da yayi niyar yi din.
Duk da itama kasanta ne na haihuwa amma bata son abinda ta danganta ta da Nigetia a yanzu saboda son mijin ta da takeyi .
Don tasan ba abu kadan zai iya faruwa a tsakanin su ba idan har ya taka mahaifan shi yaje kano tasan sai yadda Allah yayi da al,amarin su ita kam.
Don kafinta samu kanshi ta aure ba karamin yaki tasha kan haka ya faruba sai data hada da gargajiyan su nan ta samu ta ciwo kanshi ya yarda ya aure ta.
Wanda tasan ba wani ahalin shi da yasan da zaman shi da ita don aure da sukayi snyi shine a can daga su sai abokan arzikin su.
Ba damuwanta bane sai wani nasa yasan da ita ita dai burin ta ta samu kan mijin ta akoda yaushe ta kuma samu yadda take so din.
Ko ita ta shiga tashin hankali lokacin da iyayyen ta suka samu labarin auren ta da dan kabilan hausawa kuma musulmi wanda abin gori ne da kyama a gurin su balle shi da tasan addinin su bai yarde masu da hakan ba kasafai.
Wanan dalili ne yasa bata kaunan abinda zai sa yace zai je gida don tana ganin zuwan shi wurin iyayyen shi komai zai iya faruwa da auren su din.
Kasancewan ta itama yar kasan Nigeria kuma daga yakin jos mahaifinta ya fito mahaifiyar ta ce yar kudu ko zo in kashe ka bata ji da hausa haka ma ita merry bata jin hausa sai dan gaisuwa da sauran kalama mai saukin haddacewa.
Dan dama mahaifinta yana danji koshi ba sosai ba yafi bada amanna ga yaren da yafito daga ciki bai yi rayuwan shi a gida nigeria ba.
Duk rayuwan su a kasan turai sukayi shi acan ya hadu da mahaifiyar merry din sukai aure wanda wanan dalilin yasa da merry ta hadu da Umar tana jin daga Nigeria ya fito suka kulla abotan daya zama aure a gare su.
Yanzun haka da ake maganan nan tana dauke da cikin umar din wanda suke expecting din haihuwan ta ban da wata shidda masu zuwa.
Kallon shi da yaga tananyi ne yace da ita is my mum tana magana akan rashin zuwana gida da banyi duk dadewan nan.
And kin san gaskiya ke ma don kin kusa zama uwa very soon kin san irin feeling din dake tsakanin da da uwarshi a yanzu.
Tunda ya fara magana ta kura mai ido babu ko kiftawa har ya gama sai lokacin tace may kake nufi da maganan ka Omar ?
Yace kin sani zan tafi inga mahaifa very soon don nima rashin zuwana gare su yana damuna sometimes ina jin kewan su ina son ganin su.
Ina son inga Family dina da, , , hannu ta daga mai tana fadin is eenough Omar ma,ana dai kana nufin gida zaka ka barni nan ke nan ?
Yace yes haka nake nufi zanje gida in duba su in kwana biyu a tare dasu su gane ni nima in gansu in yaso daga baya munyi settle da mahaifina zan dawo gare ki da baby mu.
Mikewa tayi tana fadin wanan ba zai taba yuyuwa ba Omar banki ba in kace mu tafi tare wanan zan dan yarda dashi.
Da kuma sharadin idan munje zamu sauka a gurin iyayyena ba a garin ku ba har sai idan iyayyen ka sunyi acepting dina a matsayin daughter inlaw din su.
Wani kallo ya watsa mata kafin shima ya fara magana a hasale yana fadin kada ki manta da alkawrin mu kafin muyi aure na fada maki koni waye kika yarda.
Don haka idan kina son muci gaba da zama a cikin salama dake ki bari in fuskanci iyayyena ta ruwan sanyi bada garaje ba kamar yadda kike nufi din yanzu a kaina.
Ganin da gaske yake idan akwai abinda ta ki a wayi gari su rabu da umar din ta don haka dole ta kyale shi a lokacin don tasan muhinmancin alkawari sosai.
Ya juya ya barta wurin sha waran da kawai ya yanke shine zai tafi Nigeria cikin hakan kuma zai sanar dasu zancen auren nasa inyaso ayi wace za, ayi tsakanin shi da mahaifan nasa.
Da wanan tunane ya kwana a ransa na yadda zai kalli ifon mahaifin shi da wanan laifin dayayi masu yasan cewa mahaifin shi mutum ne mai ra,ayi akan addinin sa sosai.
Uwa uba irin tarbiyan daya basu tunda farko bai sako yaro wani kasa sai ja haddace alkurni da dan taba wasu litttafan addini.
Shikan shi yakanyi mamakin yadda ta samu kansa dumu dumu da auren Merry koda kuwa ace itama din yar addinin shi ce ya kamata ace iyayyen shi sun san da auren su tun farko.
Sai dai kaddara ta riga fata don Merry ta zama wani bangare na rayuwan shi yanzu zama suke a tsakanin su na so da kaunan junan su sosai.
Yasan merry ba yarinya bace ko zai girmay mata da kadan ne a wurin shekaru sai dai hakan ba illa bane idan akwai so da kaunan juna.
Auren shi da merry yanzu shekara hudu ke nan sai bana tayi ra,ayin haihuwa don a ganin ta ya kamata su zama iyayye a lokacin.
A karshe dai daya gaji da tunanen sa sai yaga bai kyautawa merry sa ba a yadda suke akwai fahinta mai karfi a tsakanin su sai dai bai san dalilin ta na rashin son zuwa gidan shi ba.
Gashi ita tana zuwa wurin nata iyayyen sun shirya da sukaga bata sake akidar taba na christanci dama su shine damuwan su.
Haka dai yai ta sake sake a zuciyar shi har barci barawo ya sace shi ranan washe gari bayan ya gama abinda yake yaga har lokacin baiga merry ba yasan fushi take akan maganan su ke nan.
Ya shiga daya dakin da take a ciki don idan tayi fushi haka sukeyi ko shi idan yayi fushi da ita.
Tana kwance fuskan ta yana kallon daken din dakin ya shigo har inda take a kwace din yana fadin kin dai san condition din da kike a ciki da kikai wanan kwanciyan yanzu.
Ta dago ido tana kallon shi yana tsaye ya harde hannayen shi a saman kirjin shi yace ko ba zaki gyara bane in gyara maki.
Sai lokacin ta gyara tana fuskantar shi ya samu wuri ya zauna a gefeb gadon yana fadin ban san may yasa kike son yanke alakata da iyayyena da yan uwana ba.
Ke baki tunanen lokaci yayi da zan fuskace su akan matsalan auren mu da basu san nayi ba don unborn baby din mu dake zuwa ?
Ko kina son baby mu yazo ya samay mu a wanan halin na rashin wani nasa daga bangaren mahaifan shi ne ?
Kai ta girgiza don jin abinda ya fada wanda tasan gaskiya ya fada ta bude baki da kyar tace a a ba haka nake nufi ba dear.
Ina dai tunanen kamar in ka tafi ba zaka dawo gare mu bane kuma idan suka san da zaman mu a wani matsayi zasu karbe mu can.
Yayi murmushi yace ina son ki gane idan naje gida nasan zamu sasanta da iyayyena akan abinda muka dade muna boyewa gare su nasan surely zasu fahince ni.
Don aure nayi ba zaman banza nake dake ba and nasan halin iyayyena duk abinda nake so suma zasu so abin nan.
So zama haka a cikin duhu ba zai yuyu akan mu ba, idan naje nasan babu wani dogon matsalan da zamu samu a gare su matukar na zauna nayi masu magana ta fahinta akanki.
Sai lokacin mery ta danji sanyi a ranta taga zuwan nashi yana da amfani gare su matuka ta tace yanzu na gane na fahince ka amma kabi sannu kada kazo kaje a samu wani matsala kuma ya biyo baya.
Yace kada ki damu da wanan ni nasan yadda zan fito masu da zancen ba tare da an samu matsalan komai ba.
Da haka dai ya ciwo kan merry din har take ta faman taya shi shirin tafiya gida da zaiyi ba tare da an samu matsalan komai ba a tsakanin su don kawai unborn baby din su ya samu saki a wirin dangin mahaifan shi shima.

Ni dai ina ganin yan part din hjy jummai sai shirye shirye sukeyi gashi an bude dayan bangaren da babu kowa a cikin sa sai dai lokaci lokaci akan bude wurin a gyara shi.
Ko idan anyi baki a sauke su a gurin sai naga duk wanan kwanakin ana ta yan gyare gyare a wurin hakan dana gani baisa na mayar da hankalina in san abinda akeyi ba a gidan harkan gabana kawai nakeyi.
Mun dawo daga islamiya ban shiga part din mu ba na bi ta baya don in kwashe shanyin uniform din mu danayi a baya sai nake jin murysn hjy jummai a wanan part din.
Nayi abinda zanyi har na bar gurin bata fito ba bayan na shigo ne na samu mamu a zaune tana waya don haka na shige ba tare da na gaishe ta ba bayan sallama.
Ina kokarin shiga bayi don in dauro alwalan magariba idan nayi sallah in zaman gugan kayan makarantar namu naji mamu ta kwala min kira.
Da sauri na fito daga dakina ina amsawa na fito falon na samay ta har lokacin tana rike da waya a hannun ta.
Nuna min wurin da yaran da suka dawo suka bata tayi da hannu nasan bata son kazanta don haka na gane may take nufi na juya zuwa dauko tsintsiya da packer don in dan tattara wurin.
A lokacin naji abinda take fadi a wayan tana fadin ko sun dawo gidan nan ina ruwa na dasu hajara ?
Idan mutum yace yanayi dani in yi idan kuma naga su maza sun dauki akidar uwarsu sai in share su tunda ba zaman su nake a gidan ba.
Banji may na cikin wayan ke fadi ba sai naji tace gobe fa gobe goben nan idan dai ba sun fasa bane baki ga yadda mahaifan ke ta rawan kafa ba mu dai iyakan mu ido ai.
Suwa zasu zo gobe naji mamu na magana na rambayi kaina da kaina da yake ba abinda ya shafeni bane na kwashe na fita daga falon.
Ina zaune ima zaune ina guga bayan magariba mamu ta fito daga daki na san ta sallamay sallah ne a lokacin don tana saye da hijjab din sallah ta har lokacin tace.
Sayadi kije part din gwagona ki karbo min kankara idan suna dashi nace to ina kokarin dagawa daga wurin gugan take fadin don Allah kada ki tsays hira dasu Aisha ki barni ina jiran ki.
Nace ba ma zan tsaya ba mamu fon ban gama gugana ba gashi dare yayi na fito ne naga ana shiga da wasu kaya part din har Alh kanshi yana gurin a lokacin .
Ko da na dawo still suna cikin part din fon daga can part din mu mutum zai iys hango abinda akeyi na raya a raina idan na shiga zan tambayi mamu .
Sai dai ina shiga na samu ta kara tayar da sallah haka yasa ban samu tambayan ta ba komai.
Washegari Jumma a ce tunda muka dawo nake kwance ina barci don ranan ba islamiya ga gajiya na kwaso yass na kwanta in huta.
Can cikin barcina naji gida ya rude da hayaniya sosai sama sama nake tsinkayo muryoyin mutanen gidan har da Amma.
Gyara kwanciya na nayi don nasan bai wuce wani fitina suka samu a gidan don su basu raina abin fitina gidan nan.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
16/11/2021, 22:48 - ??5惙5惙5?: YA, HAYYU YA , KAIYYUMU BIN RAHAMATIKA YA ASTAGIS, , , , , , , , ,


Daga manyan gidan har zuwa yaran gidan gaba dayan su murnan zuwan bakin su sukeyi har Amma kanta saida ta fito lokacin da ake fadin gasu nan sun iso gasu nan.
Wanan hayaniyar ya hanani komawa barci na mike na fito falon mu babu kowa a cikin sa na nufi hanyar fita waje.
A daidai lokacin da Amma ke fadin banga angona a cikin ku ba don shi na fito taro saboda shine yasan da zama na yakan kirani jefi jefi mu gaisa dashi.
Kallo juna sukayi sai habbib ya daure fuska shi kuma dayan yace kai wanan tsohuwar da rigima kike dama muma ai bake muka zo gani ba dama.
Ta dan tabe baki tana fadin daga fadin gaskiya sai bakar magana ka dawo ke nan baka ko huta ba ka shiga halin naka.
Yace ai amsa na baki don ba wanda ya gyato ki nan maman mu da daddy muka zo gani sai yan kannen mu gasu nan sun tare mu.
Aikin banza tace tana tabe baki ta juya wurin habbib tana fadin kai kuma abinda ka kara koyowa ke nan a kasan rashin fara, a, ?
Ya dan gyara tsayi tare da fadin ohh wanan tsohuwar halin ki dai yana nan ashe ?
Dan murmushi ta sake tare da fadin kai da alaman zamu shirya wanan karon don da gani kafi wanan mai askin arnan da shiryuwa.
Kai Amma ki bar wurin nan ki bari mu gaisa da iyayyen mu don Allah tace ai yanzu ko ba sai ka kore ni ba marata ido.
Ba dai naga saukan ku lafiya ba yace wanda dai kika zo taro bai zo ba sai ki shirya ki samay shi can idan kin so ganin sa.
Hjy jummai dake ta bata fuska kan ba,an da suka tsaya yi da tsohuwan ta mayar da kallon ta gun habbib cikin nuna kulawa tare da fadin .
Ku shiga daga ciki ku zauna kafin ku isa sassanku sai lokacin su mamu suka shiga gaida su da zuwa wanda sun sha jinin su tun kalamin Aliyu din dayace mahaifan su suka zo gani ba wani va sai yan uwansu.
Ke nan su basu damu da tsayin su a gurin ba ke nan sai iyayyen su duk da haka abinka ga kawaici sai basu nuna jin zafin hakan ba a fuskan su.
Sai lokaci su mamu suka samu gaisawa dasu inda suka amsa ba yabo ba fallasa a fuskan su ko wani kula da su, su nuna su din matan mahaifinsu ne kuma uwayen kannen su basuyi ba.
Ni dai ganin Amma ta juya zata wuce nayi sauri kafin ta ganni ta sa inyi gaisuwan dole na bar wurin inda na samu kanne na a falon mu.
Hjy jummai ta kalli yayan nata cikin so da kauna ta nuna ma su mamu kuma itafa ce da gida tace ai sai ku shige daga ciki ku huta.
Daga baya ku gaisa da daddy da kyau ba mussu yaran suka fara shiga part din ta a can ta fara gabatar masu da

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login