Showing 171001 words to 174000 words out of 419207 words

Chapter 58 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1404

Allah ya sauwaka suka fito daga dakin a haraban asubiti suka hadu da yaran sun fito sallah isha,i suka tsaya suna masu yaya jiki.
Sukan sun amsa masu a cikin kulawa da nuna su nasune tare da tambayan ya akaji da taron jamma, a kuma dan dama habbib wanda tunda ya gaisa dasu ya koma daga baya kadan ya tsaya yana dakilan wayan shi.
A hankali kamar baya sauraren su har suka gama gaisawa suka tafi Aliyu ne ya fara magana gaskiya maimunan nan tafi mun hjy maryam mamace dai kawai bata son a fada.
Diba yanzu duk irin halin da ake ciki saida matar nan ta tako kafanta asibitin nan kai ma da ganin ta kasa akwai damuwa a tare da ita wallahi.
Humm ka manta mutumiyar mama ne sosai har dinki mama take muna tare da muna yara takance batayiwa bros kaya ba tare da hussainar shi ba.
Sai lokacin ya dan saki murmushi a gefen fuskan shi yana fadin daddy da mama sun raba wanan tagwaicin yanzu maimuna sarakuwanace can you imagine wai yau nine da auren yar maimuna ta cikin ta fa ?
Wata kanwar hjy ce ta katse masu dan hiran rahan da sukeyi ta fito tana fadin wai a kawowa hjy ruwa masu zafi daga gida yanzu.
Likita yace idan ruwan hannunta sun kare ta dan watsa ruwa ko jiki zai kara sake mata dan haka ne su Aliyu da habbib suka nufi hanyar gidan a wurin packing din motocine suka samu su mamu da motar mama hadiye yaki tashi suna fama da ita dole suka tsaya suka duba masu motar kusan a tare suka iso gidan.
Sai a lokacin suka tuna da babu kowa a part din sai kuma suka rasa yadda zasuyi dole gurin mamu suka nufa ta samasu shi da sauri tare da bada babban ktele din ta akai don bukata haka suka wuce suna zancen a mota.
Koda suka dawo sun samu hjy a zaune ana jiran dawowan su suna zuwa aka juye mata ta watsa sai data fito ne tana zaune ana zancen dora wani ruwan zafin ta kyala idon ta ga kytele din mamu tayi saurin gane shi don sunyi sababin don may aka sayo mata shi lokacin haihuwan twis da tayi a asibiti tace don may Alh zai saiwa maimuna electric ita kadai a lokacin.
Sai ga shi yanzu ktelee din yai mata rana itama bata damu da halin da take ciki ba ta lailayo ashar tana fadi ubanwa ya kawo wanan electric din nan, nan ?
Wani electric kike magana wanan ai su Aliyu suka zo dashi da aka bukaci ruwan zafi fada take sosai kannen ta suna bata hakkuri a daidai lokacin suka shigo dakin tako hausu da sababi tana fadin don may suka dauko mata kayan makiyiyar ta.
Tsayawa sukayi suna kallon ta da mamaki don basu san aka abinda takewa fadan ba haka sai daga baya suka fahinci abinda takewa fadan .
Bayani sukai mata tace da ba kowa a gidan ba sai kuje wani gun ba ku karbo min Ammani ko kayan maryam ba zanyi amfani dashi ba balle na maimuna.
Haba mama matan nan fa har rawan jiki take da sauri ta sa ruwa na don a kawo maki kuma har asibitin nan take wurin gaida ke.
A zabure tace makira algunguma tazo ganin halin da nake ciki ko don ta gani ko na kusa mutuwa ko yaya ance mata na fadi kasa warwas shine ta kwaso kafa tazo gani.
Aiko do wanan yarinyar bazan mutu yanzu ba don kawai inga bayan ta gobe dole ne babawo ya sake mata shegiyar yarta don duk bala,in da za ayi dole ne auren salma dana babawo ya mutu a goben nan.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:12 - ??5惙5惙5?: YAHHAYU YA KAIYUMU BI RAHAMATILLAHI YA ASTAGIS


Dakin yai shiru ana sauraren ta kafin ta dago kai tace dawani sakaran mara hankali ya samu yaba salma shi don sai mara hankali zaiyarda da aure yata ba tare da sanina ba wanan wani dan iskan nemawai ?
Kowa ya kasa fada mata sai habbib ne yaja dogon numfashi kafin yace ba wani bane fa mama Ahmad ne yaron daddy.
Tayi saurin fadin wa iye tare da sakin wani uwar ashar kafin tace Ahmad, Ahmad dai almajirin mu kowa ?
Yace almajiri kuma mama Ahmad ai ya wuce a kirasa almajiri kuma yanzu.
Mikewa tayi tsaye lokaci daya tana fadin yanzu na gane kuskurena na auren Alh don wallahi Alh ya nuna baya kaunana ko kadan.
Amma zai gane kuren shi nayin hakan gare ni na fahinci nema yake ya tozartani a idon duniya kai yama gama tozartani din yanzu.
Saidai wallahi yayi karya don wanan auren basu dauro ba kamar an warware shi angama a wurina.
Haba mama ki kwantar da hankalin ki don Allah har ki samu lafiya mu yanzu lafiyan ki shine a gaban mu umar da tun shigowa shi kamar baya dakin yai magana cikin zafin rai ga mahaifiyar tasu a laron farko tunda ta tashi tana haukanta yana zaune yana dakilan wayan shi.
Cikin wani tsawa tace rufa min baki don na fuskanci baka son laifin mahaifin ku a fakaice idan ayi magana ka wani nuna damuwanka a kanshi duk zaku gane kuren ku na yarda da wanan bakin hadin da kuka bari akai maku.
Zaiyi magana habbib ya daga mai hannu tare da fadin bros mu tafi idan yin biyayyan data koya muna muyiwa mahaifin mu ya zama laifi a gare mu yanzu.
Yana fadin haka ya juya yabar dakin cikin zafin rai Aliyu bai tsayaba ya mara masa baya umar suka bari zaune ranshi inyai dubu ranan duk a bace suke mai.
Katashi kabi su kaima don banga abinda kake muna a nan ba tunda bakin ku daya da mahaifin ku na sani.
Umar ya sake dago kai ya dan kalleta kamar zaiyi magana sai kuma ya mike ya kalli yan uwanta dake tsaye cirko cirko suna kallon yace mama zan tafi sai da safen ku ya juya wuri ta yace Allah ya baki lafiya mama daga haka ya fice dakin shima.
Yana fita ta fashe da wani irin kuka Asma,u ta kalleta tace haba yaya bai kamata ki fito masu ta wanan hanyan ba gaskiya.
Ki tuna yaran nan suna maki matukar biyayya duk inda kika dorasu basu ketare wurin yanzu suwa mahaifin su bore a fili kike so may ye laifin yaran nan cikin maganan nan don Allah ?
Asma,u barni naji da abinda ke damuna Alh rayuwata yake nema tace koma dai may ye anty munsan irin halinda kike ciki don dukkan mu nan muna jin zafi amma yaran nan yadda kikai masu ne bai dace ba.
Tun dafa aka kawo ki nan bansa wanin su yasha ko ruwa da dadi ba yaya kike son suyi da ransu bafa don Allah ya dora mu akansu yace muyi masu yadda mukaga dama da rayuwan su ba.
Sai ki bisu a sannu tunda suma baki san kudiri su ba gagawa fa motar shedan ne anty.
Ta jefawa Asmau wani harara tare da fadin ke kika damu da hakan yanzu ban tausayin su tunda da sukazo nuna min sukayi basu san komai ba ai.
Asmau na jin hakan ta mike tana kallon agogon wayan ta tana fadin dare yayi anty mu zamu gida saidai da safe mu sake shigowa Allah ya baki lafiya.
Babu wanda ya tankata cikin su uku dake dakin ta mike ta fita abinta tana fita dayan????? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? 
tace ita asamau dama haka take a kan yara bata son ran daya baci.
Mikewa hjy jummai tayi tana fadin ni yanzu zaman may nake a nan yashe ga aiki nan ja a gabana ai banga zaman asibiti ba tunda naji sauki.
Ki dai bari zuwa safe sai a kara ganin yadda bp din naki yake kinga sai a neme sallama wirin likita zaifi.
Da kyat ta yarda da shawaran su sai zuwa safe zataga likita ya sallamay ta takoma gida da safe tunkan likita ya bata sallama ta salami kanta tana idar da sallah din.
Ita ta buga gida maigadi maigadi da bai dade da dawowa daga masalci ba ya bude masu kofa ta shigo da jidalin ta tana fadin.
Ina munafukan banza da wofin gidan nan ban mutu ba na taso do a hada baki aga bayana maiganin bayana sai Allah.
Yanzun za,a fara wasan tsakanina daku tunda haka kuke so duk wani tsohon banzan gidan nan da baiba da shawaran alheri na daina shayin maishi daga yau din nan.
Jin hakan da mama hadiye tayi yasa ta bude kofan part din su ta fito tana fadin tsofin banza na gwale kin barsu Amina .
Indai wanan ne ba a son ki ba a son ki din Amma dake zaune a kaina tun kare sallah na tana ban baki taji muryan mama hadiye tafito tace.
Hadiya idan nina haife ki ban yafe ki kara tankawa duk haukan da jummai zatayi a gidan nan ba.
Haka yasa mama hadiye komawa badon taso ba don ta shirya su cashe juna ranan da hjyn a gidan.
Kawu da bai dade dawowa daga masalaci ba yana dakin shi sama sallaya yana karatu yaji wanan hayaniyar nata zai fito ne yaji abinda Amma tacewa mama hadiye haka yasa ya koma bai fito ba.
Nan aka barta tana ta zage zage ita da yan uwanta a tsakar gida ba wanda ma ya bude part din shi ya kula da abinda takeyi kowa nasa ya ishe shi a gidan.
Ta kare da fadin duk uban daya daura aure diyan ta shi zai koma ya warware shi don ba wanda ya haifa mata diyan balle yai masu auren dole don an raina ta.
Alh dake daki ranshi ya gama baci yana son fitowa kalamin mahaifiyar shi ya hana ya fito sai mamakin irin kalamin da take sake mai shida yan uwanshi harda mahaifiyar su.
Hakana ya daure ya kyale ta saida ta shiga part din ta ita da yan uwanta ya tashi yai wanka ya shirya ya fara shiga wurin hjy maryam dake tare da yaran ta da wasu tsofi gudu biyu yan uwanta da suka kwana suna tausanta.
Sun gaisa dashi a ciki mutunci inda hjy maryam dataci kuka har ta gode tana zaune a kasan kafet ta dukar da kai.
Zai fita yace babba gobe idan Allah ya kaimu ne yaran nan zasu tare a dakunan nasu da naso sai satin sama ayi buki amma yanzu saboda wasu dalili an fasa haka gobe ne tarewan nasu.
Wani kuka hjy maryam ta sake maicin rai tana fadin ita bata aje komai ba bataba wani ajiya ba zai sa mata buki bata shirya yinsa ba.
Ya kalleta yai murmushi tare da fadin ina dai nine mahaifin wanan yaran ni kuma nasa bukina to ku barni da dabarana ku gani.
Tsohuwa guda tace Alh mu damuwan mu shine yarinyar nan tace bata san wanda aka daura ma yar nan aure dashi ba shine damuwan nata.
Yace babba wanan ba matsala bane don ni nasan wanda na zabawa diyana da kaina kuma haka tsarina yake idan an kaita zaku sanshi ai.
Allah ya kyauta matar tace yace amin ya fice abinshi ya barsu ta sake barkewa da wani kuka daga ita har ikilima din.
Part din mamu ya shiga ya samaysu falo zaune tare da Amma ya dan sake fuska saidai hakan bai boye mashi damuwan dake tare dashi ba har lokacin.
Kasa ya zube yana gaida mahaifiyar tasa ta amsa itama cikin yanayin damuwa a tare da ita take tambayan shi yaya gajiyan jamma,a yace Alhamdullahi.
Ya dago yana fadin hajiya gobe in Allah ya kaimu yaran nan zasu tare a dakunan su don na gama shirin komai saboda umar yace yana son zaikoma nan da jibi bakin aikinsa.
Haka yasa na mayar da tarewan nasu gobe idan Allah ya kaimu don haka nake son idan da wani shiri a bangaren mata sai ai min lissafi na bada komai ayi yadda ya dace din.
Tace gobe goben nan aiko dai kamar yayi kusa yace baiyi ba hjy idan kinyi la,akari da haukan da jummai ke nunawa gara ayi a kare komai kowa ya huta hakana.
Allah yasa hakan shi yafi alheri mamu da taji maganan kamar daga samane ta fashe da kuka da bata iya cewa na maynene ?
Kallon ta sukayi yana fadin ke kuma may ye abin kuka anan zaki sarewa yarinyar nan zuciya ne ko may kukanki yake nufi yanzu ?
Cikin karfin hali tace yaya naga komai fa bamu shirya ba kan tarewan nasu a bangaren mu yanzun kuma za,a ce wai gobe gobe ?
Wani shiri ne zakuyi ina ita fatima ba ko garin nan zasu zauna ba tafiya zasuyi don gudun hakane gaba dayan su nace su tare ga goben ai.
Nagaji da wanan tashin hankalin naku da kowa ke mun abinda taga dama a cikin gida kuna son daukana mutumin banza.
Ammace ta bashi hakkuri har ya bar part di mamu bata daina kukan da takeyi ba saida ya fita Amma tace gaskitan yayanku ne ai kukan ki yana nufin kina sarewa yarnan gwiwa ne.
Ki bata kwarin gwiwa da hikimomi muna mata da zai amfane ta don yanzu ba abinda ya rage tunda an daura aure ko.
Gwaggo har nawa sayadi take da za a dauke ta a wanan hali zuwa wani kasa mutumin nan bafa so yarinyar nan yake yi ba wani fuskan tausayi bai taba shiga tsakani su ba har yau.
Ahir din ki maimuna nace ahir din ki da furta wanan kalami ga yarki na karajin wanan a bakin ki nida kaina zan saba maki a gidan nan .
Ganin irin fushin da Amma tayi yasa ta fara bata hakkuri kan kuskuren datayi din nan dai amma ta kara sata a hanya daga haka ta mike tana fadin zama ba namu bane yanzu tunda tafiya ta canza sallo.

Sam basuyi tsamanin shigowan shi ba a lokacin sun zube a falo sai cacakanshi sukeyi ga salma sai kuka take rusa ana mata huduban shedan.
Ganin shi tsaye yana sauraren su yasa aka hau kalon kalon a tsakanin su ashe duk fitsaran hajiya jummai da sauran shakkan shi a zuciyar ta.
Kallon salma yayi yace salma tashi ki shige daga ciki hjy zatai magana ya daga mata tsawa yace nace ki tashi ki shiga daga ciki.
Amma dai Alh kasan wanan abinda ka, , , , hannu ya dagawa hjy rabi data soma magana wace kebiwa hjy jummai gurin haihuwa.
Yace ban yi dake ba rabi ko kina cikin iyalina ne in sani tace banciki amma dalili ya kawo haka ai.
Yace to wanan dalilin ya tsaya iya ku da yar uwan ku banson ina magana da iyalina wani bare na saka min baki ki kiyayye hakan.
Wallahi ba zai yuyu ba hajiya jumai tace tana mikewa an tabamune dolemuyi magana wanan bakin auren wallahi yadda ka daura shi haka zakasa a warware shi yace dakyau.
Ya nuna mata kofan fita tare da fadin magana na yana nan har yanzu ina bisa bakana niko ko ki bar wanan zancen ko ki fice min daga gidan nan.
Hjy rabi tayi caraf tace don gidan ka zata bar maka gidan ka amma ka sani kaida kanka zaka nemay ta ai hjy ce kasan ta .
Suka mike lokaci guda suna fadin don an bar maka gidan sai may dama ai ba a gidan aka haifeta ba diya kuma bada su tazo ba.
Yace ashe kun san da hakan kuke son nuna min yadda zanyi da abina tace ko zan tafi da salma zan tafi bazan barta a nan ba kai mata dole.
Yace kiko tabbatar da idan kin tafi da ita ta tafi ke nan sai dai ki nema mata wani uban bani ba tunda kinfi gareta.
Salma dake saurare daga daki tayi saurin daukan waya ta kira yannen ta tana kuka cikin kashe murya take labarta masu abindake faruwa a gidan.
Kawu ya fice ya barsu a falon hjy rakiya tace lalai anty mutumin nan a shirye yake da ko wani irin mataki zaki dauka akan zancen nan don haka muyi hakkuri ku barshi a yadda yake so daga baya musan shirin da zamuyiwa zancen.
Hjy rabi tace gara mu nuna mashi muma muna da right din mu aiba shi kadai ya haifi yaran ba da yakewa mutane iko dasu.
Ke salma fito muje yayi abinda zaiyi din anty bata kara minti goma cikin gidan nan gidan shi din banza may ya aje a gidan banda tarin matan banza ko a hakan da yake ganin ya gama da ita akwai mai sonta wanda yafishi.
Shi inba ma aure mu kaddari ba har ya isa yace zai auri anty ne bakauyen banza dashi ma.
Ta kara kwalawa salma kira salma taki fitowa har lokacin hjy tace idan baki fito muka wuce ba sai na balbala ki a dakin nan idan na samay ki ciki.
Jin haka da sauri nafisa ta taso ta datse kofan dakin tana

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login