Showing 60001 words to 63000 words out of 419207 words

Chapter 21 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1494

lafiyayyen abincin dana sha wanda ba karamin kudi ta karba a wurin Alh ba don shirya ma zuwan yayan nata.
Abinci da abin sha har sun rasa wanda zasu fara dashi a falon suka dan tsukura ana fira sama sama dasu da mahaifiyar su.
Can tace watau dai ya tabbata shi babawo ba zai zo gida ba ke nan zaman can ya fiye mashi dawowa gida cikin yan uwan shi.
Aliyu dake goge bakin shi da tisue yace ba wai hakana bane mama kin san yanayin aikin sa baima da lokacin kansa balle na tafiya .
Ko yaushe shi a cikin aiki yake shiyasa ma ba,a faye samun sa sosai ba ai daiyi hakkuri don muyi waya dashi kafin mu taso na samu layin shi yace zai shigo da yardan Allah.
Sai lokacin habbib da yake shiru shiru yace mama sai kun yi hakkuri da yanayin bros don wallahi aiki yayi mass yawa sosai kin san in mutum ya zama haziki haka kowa ke son aiki dashi.
To amma habbib ace mutum ya shige cikin duniya haka ya manta da kowa nasa kamar bamu a raye ashe idan bamu raye ma shike nan sai ya manta da gida a rayuwan sa tunda shine agogo sarkin aiki.
Yanzu fa akalla babawo yakai shekara goma sha da zuwa kasan nan shike nan shi bama zancen aure yakeyi ba a rayuwan sa sai neman duniya.
Aliyu yace mama ke nan yanzu bros in dai duniya yake nema ai ya samu don ya wuce yadda kuke tsammanin sa gaskiya.
Yanayin sa ne haka tun farko kun sani ko anan din da yake ai kin san irin halin sa na kin shiga jamma,a sosai.
Amma ai zai zo fon ya tabbatar min da zuwan nasa tace yama zauna can idan mun mutu sai yazo gaisuwa .
Haba mama hakkuri dai za a yi yana tafe in sha Allahu don su kawar da zancen dan uwan nasu saboda sunga ran mahaifiyar su ya baci yasa habbib din mikewa yana fadin zai shiga ya dan watsa ruwa ya mike don akwai gajiya a tare da shi.

Nikan ina shiga wurin mu na gyara ko ina na saka kamshi na dawo falo muna kallon catton da kanne na muna dan hira a haka mamu ta shigo ta samay mu.
Bin yanayin fallon tayi da kallo tana zama take fadin yau baki ne a gidan namu yan wirin hjy suka dawo daga kasan waje.
Nace ai ihun murnan zuwan su ya tayar dani daga barci sai mamu duka maman su anty salma ce ta haife su ?
Ashe kin gansu ke nan ta tambaya tana kallona nasan abinda take nufi bangaida su ba nace ni mamu yadda naga suna sakin magana wa Amma ne bai mun dadi ba kamar ba jikokin ta na jini bane su.
Jikokinta ne kuwa don dukkan su uku hjy ta haife su babban nasu ina ganin bai samu zuwa bane kuma shi tun ina gidan mahaifin ki ya tafi.
Da yana dan shigowa lokaci lokaci daga bayane kuma ya daina zuwa don ance yanzu aiki yake ma kasan england da wasu kasashe.
Amma da ganin su zaman turai ya canza su ji don Allah yadda suke rungumar su salma da girman su tace ke dai don baki da yaya na miji ne kike ganin haka.
Ni kan har kwanan su uku da dawowa ban saka ko dayan su a idona ba na shiga part din Amma karban abu na samu suna maganan akan tsaraba da aka raba a gidan wanda suka zo dashi.
Sai nake jin Aisha na fadin kilama ko Fatima itama bata samu komai ba a cikin rabon nan hankalin su ya dawo kaina suna son ji ko an bani wani abu a cikin tsaraban nace .
Ban ma san da su ba balle tsaraban su don ni bada abin wani na dogara ba Amma ina kayan abinci in dauka mamu tace in karbo mata.
Tace shiga ciki yar nan ki duba kitchen sunanan a wanke na shiga kitchen din na fito Amma na fadin halin wanan matar sai ita duk irin kayan da yaran nan suka jibgo abawa yan uwa ta rike sai ita da yayanta ke shiga da fice a ciki.
Ni ban tsaya jin abin haushi ba ba wuce tunda ba magana na bane muna raba abunci da mamu nake fadin yanzu su Amma ke tambayana wai an ban tsaraba bakin gidan nan ?
Wani tsaraba kuma kai gwago ma dai da wani magana take komu da yaya aka bamu wanan tsaraban nasu ina sai da Alh yayi magana a kai ta dan yafuto muna Allah dai ya ba kowa nasa.
Ni kinga irin abubuwan nan ba damuna suke yi ba a rayuwa idan ta bayar ya kare idan bata bayar ba wataran ma ya kare don haka ba wani abin damuwa bane hakan.
Balle ma may ye a cikin tsaraban da suke magana wasu riguna ne sai atamfar holand guda daya yana nan saman gado na aje.
Don basu wani gamshe ni ba dama ake na ajewa su idan kina so a dinka maki su nace da sauri a,a mamu ki dinka abinki kayan da kikai min sun wadatar dani nikan.
Da dare ina zaune naga mamu ta kwashi kayan zuwa part din su amma ta dade a can sai gata ta dawo da su hade da wasu kayan ta zube saman kujera.
Ta fita da abincin maigidan dana gama blending bada dadewa ba ganin bata dawo ba yasa na dauki yan kanne na da sukai barci nakaisu dakin barcin mu.
Na dawo na kwashe kayan na shiga mata dashi ciki na jawo kofan mu na haye dogon kujera na kwanta a falon .
Har barci ya dauke ni sai gata ta shigo na bude idona inga ko waye ya shigo falon tace dama nasan kunyi barci ina can na samay shi da yaran shi suna hirane kin san halin sa yace in zauna in jira fitan su.
Jin banyi magana ba tace ina kayan dana aje wurin nan nace suna ciki na kwase dazu tace dama gwago ce tace akawo maki naki tsaraban kuma in tabbatar da kin dinka su kin saka.
Nace ni ba zan saka ba tunda bani aka bawa ba mamu tace na fada mata tace ai tunda bata baki ba sai ta ganki dashi a jikin ki .
Kai ita Amma akwai son rigima wani lokaci da kawai ta kyaleta tunda ba a tsirara nake tafiya ba.
Wai yar nan ashe da gaskiya akace tashin kaka manyan magana ke ga bakin su ke wai har kin san wanan zancen da kike fada.
Dan dariya nayi nace mamu wallahi har kin sa naji kewan manjo na ko a wani hali take yanzu bari dai in duba lamban Atika ko zanga inda na taba rubutawa a littafina da dadewa.
Ba wanan ba don babba lafiya kalau take don munyi waya da Addah ki kwanan baya take fada min hakan.
Sai dai abinda nake so dake yanzu a gidan nan ki kara kama kanki da zuwan yayan hjy gidan nan don ba mutunci ne dasu ba ko ni da nake mahaifiyar ki.
Ban ishe su kallon arziki ba a yanzu bayan a baya can tare muka taso dasu cikin wanan family din ko don yanzu suna ganin su din wata tsiyace ko kuma zugan uwar sune a kaina ban sani ba.
Nace mamu may zai hadani dasu niko a gidan nan yaushe ma na zauna a gidan ina gurin neman abinda zan zama in tallafawa manjona.
Kallon tausayi tayi min don dama tasan jajircewa a kan karatu da karfin gwiwan maganan manjo datayi min nake yin sa.
Sai dai a fili tace min nasan ki da tsiwa da rashin kunyawa na gaba wanan halin bai min dadi a raina ko yaya ne idan mutum ya girmay ka ya girmay kane.
Ban san irin tsonewa mutane ido da kikeyi ba sayadi duk da nasan kin rage wanan tsiwan naki amma kullun laifin gidan nan bai wuce kanki saboda haka ki natsu sosai da komai da kowa.
Wanan maganan da mamu tayi duk da bata fito fili ta gaya min dalilin ta ba na fagince ta a raina.
Watau tunda gida mahaifin su nazo inbi a hankali saboda a zauna lafiya don ita ba mai son hayaniya bace a rayuwan ta ko kuma tsoron su take ban sani ba.
Don haka naji a raina na tsani hjy jummai da dukka yaranta a raina matar da bata kaunan ganin kwanciyan hankalin mahaifiyata a rayuwan ta akan may zaga mutuncin ta nikuma.
Kamar yadda mamu taja min kunne haka ma Amma da yaya Ahmed don shi cewa yayi bai yarda kwata kwata da tarbiyan su ba .
Kamar sati daya da dawowan su garin ranan ina duke ina shara Aisha tazo shiyan mu tana daga kofa muna magana sai naji tana fadin ina wuni yaya Aliyu.
Ya karba mata a takaice da lafiya yana fadin wanan na ciki wai cewa da mamu yake nufi naso in share shi sai dai na dago ina fadin ina wuni kamar yadda ya amsa mata nima hakan ya karba min don jin zazzakan muryan da nake gaishe shi dashi.
Da sauri ya ware ido ya sake kallo na daga dauke kanshi da yayi da farko da kyar ya kara buda baki yace mai shiyan tana ciki ne ?
Na daure a yatsune nace tafita kawai ba tare da na sake dagowa na kalli inda yake tsaye ba naci gaba da aikina.
Ganin bai tafi ba ya tsaya yana danne dannen wayan hannun shi yasa na aje tsintiyar hannuna na shige part din mu.
Ya bi bayana da kallo har zan shige naji yana fadin idan ta dawo ku fada mata na shigo ban samay ta ba Aisha ce ta karba mai da to yaya Aliyu nan nasan shine Aliyun gidan.
Alhamdullahi ko ina a fadin duniya an dauki azumin watan ramadana har ya fara nisa ana neman rufe goman farko ba wasa a wanan lokacin .
Da safe haka zamu tafi tafsiri da Mamu da yan kanne na idan mun dawo ba wani hutu zan dan gyara gida inyi duk wasu aiyukan daya dace .
Don lokacin muna hutu dana gama zan tafi daukan karatu islamiya don ba kowane ke zuwa a wanan lokacin ba sai yan tsiraru daga cikin mu.
Idan na dawo da nayi sallah azahar zan fara aikin abinda zamu ci a part din mu sai part din su Amma da muke sakawa abinci koba watan azumi bane wannan ka,ida ne sai mun saka masu nasu daga tukunyar mamu.
Sai zamana a gurin mamu ya zamay mara alheri yanzu don dan lokacin ta samu saukin abubuwa a gidan sosai don yanzu na gwane sosai ga komai ba sai ta shiga kitchen ba idan ina gida.
Ga wani girma dana kara makerin yan matanci na ya zauna ya kerani gwanin ban sha,awa duk wani sura da akeso ga ya mace ya fito min fili.
Wanda hakan yake kara mun bakin jini gurin yan matan gidan don sai mutane su dauka nice ma yar gidan basu ba haka ke basu haushi har basu son abinda zai fitar damu tare dasu.

ENGLAND
Damuwa ne karara a fuskan ta ba sai an fada ma mutum tana cikin tanayin bacin rai da damuwa ba a lokacin.
Merry ce tana zaune ta hade kai da kujera tana faman tunanen tafiyan mijin nata wanda zuwa lokacin ya gama duk wani shirin da yake son yi don tafiya gida gurin iyayyen shi ko.
A hankali ya tako zuwa inda take zaune har ya zauna bata iya dago kai ta kalle shi ba sai daya dan dafa mata kafada ta dago jajayen idanuwanta ta sauke mashi.
Merry wanan abin da kikeyi na fada maki ba shine mafita a gare mu ba ina tafiyan nan da yardan ki na shirya yin sa.
Instead ki bani kwarin gwiwan yin sa don mu samawa kanmu da yayan mu mafita yanzu kuma zaki sare min gwiwa da wanan yanayin naki.
Ajiyan zuciya ta sauke tare da dora kanta saman kafadan shi tan??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????a fadin Omar jikina yana bani idan ka tafi gurin iyayyen ka ba zasu barka ka dawo gare mu ba.
Nasan irin rikicin dake a kanmu yanzu wanda dama na dade ina fargaban zuwan wanan lokacin a tsakanin mu nasan halin mutanen mu akan akidar su ta addini.
Abune mai wuya gare mu su yarda ka dawo gare mu idan ka tafi ka barni yaya zanyi da baby mu da sonka dake cikin jinina a yanzu.
Wani irin tausayin ta yaji a ranshi yasan maganan ta gaskiya ne abune mawuyaci mahaifanshi su yarda da zancen auren su kai tsaye.
Sai dai gaskiya ba zai iya barin merry da dancikin ta ko may kuwa zai faru dashi a gidan idan ya tafi wanan ya bashi karfin gwiwan karfafawa merry din zuciya akan zai dawo gareta ba dadewa ba don su tari abinda zasu haifa a tare .
Dadadan kalaman dayayi ta jera mata yasa ta kara yarda da mijin nata dari bisa dari har taji tafiyan nashi yana da muhinmanci sosai a gare su baki daya don ko ba komai yanzu lokaci yayi da zasu daina boye boye wa ahalin shi a san da ita da abinda zata haifa a zurian shi nan gaba.
Tun da safe ita da kanta ta kashi airport inda zai shiga jirgi zuwa gida na Nigeria tare da tarin abin arzikin daya kullo daga can wa iyayyeb shi da yan uwa da abokan arziki na kusa dashi.
Haka suka rabu cikin so da kaunan da suke wa junan su bayan sun dade manne da juna har sai da sukaji ana sanar da pasingers da su hallara a kofan shiga screning.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
16/11/2021, 22:48 - ??5惙5惙5?: WALLAHU GALIBUN ALAH AM,RIHIMM, , , , , , ,


Bakin Nigeria, jirgin su ya sauka a lagos sannu a hankali yake saukowa daga matakalan jirgin da zai sada shi da kasa.
Yanayi yana kokarin gyara nicktie din dake wuyan shi yana mai sauka a hankali iskan canjin yanayi ne ya ke barazanan tunkarar sa.
A hankali ya lumshe idon shi yana mai sauke numfashin shi saboda shakan iskan yanayin gida da ya dade bai ji shi ba.
Ko kadan bazai taba mance wanan yanayin ba kasan shi na haihuwa ba da ya jima baya cikin sa ya samu kamar yadda ya gama tsara komai akan zuwan nasa komai ya kammalu masa.
Motocin da ke dakon zuwan shi sun iso ko ba bata lokaci suka bar filin jirgin don yana son sai ya huta a lagos zai shiga jahar su.
Duk da yana son hutu a lokacin sai dai hakan bai samu gare shiba don masu dakon zuwan shi kasan nan Allah yai yawa dasu lokacin kowa yana kokarin yin bucking dinsa ne ta hanyar PA din shi na nan kasan.
Hakan yasa kwana biyun da yayi a lagos bai samu wani hutu sosai ba don haka yayi haraman tafiya gida don ganin iyayyen shi sai dai bazata yake son yiwa iyayyen nasa da zuwan sa.
Gida kano kasancewa azumi ne sai ya kasance ba kowa ne ke fita da safe ba sai idan rana ya dan buda mutane sun gama barcin safen su zakaga an fara zirga zirga a garin.
Tun daga layin namu har titi mutane jefi jefi zaka gani a waje da sanyin safiyan daidai wanan lokacin na gama shirina don ranan ba zuwa tafsiri makarantar safe zan shi don in tula karatuna wanda bamu samun yin shi sosai yanzu a cikin waran azumin.
Sun dade tsaye a kofan gidan dake rufe suna jiran fitowan wani su aika ayi masu iso ciki don ko ya kira waya a wanan lokacin yasan ba dauka zasuyi ba don basu da sabon layi shi na Nigeria.
Karan bude get din gidan ya nuna masu alaman wani zai fito daga cikin gidan a lokacin haka yasa suka mayar da hankalin su sosai a kofan.
Ina fitowa wasu irin bakaken motocin manya nagani guda uku tsaye a kofan sun faka tsoro naji da farko kamar in juya in koma ciki lokacin ganin yadda layin namu yayi wani tsit kamar abin hadin baki ga mutanen unguwar ranan.
Sai da na dan tsaya tsaye rike da kofan get din gidan naga na cikin motar yana kokarin bude motar yafio na juya da sauri zan koma ciki.
Wata murya naji tana fadin don Allah tsaya ki muna iso wurin mutanen gidan na dan juyo da mamaki ina kallon mai shi din .
Ya na gyara tsayuwa yake fadin nasan baki sanni ba ko ?
Kai kawai na iya daga mai lokacin alaman ehh, .
Ya sake fadin a gidan kike ko kin zo ne nace kaga malam ba shi na fito yi ba balle ka tsare ni da tambaya idan ma aikin jarida ka

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login