Showing 345001 words to 348000 words out of 419207 words

Chapter 116 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1449

ba ko duniya zasu zo dashi don kaina na sani to mama sai ko ki kyale don Allah wanan abindai kowa ya nuna masu farin cikin shi.
Kin san kuma dole shi yaya yayi wani abu akai tunda dai yana auren jikan ta yanzu ko ?
To ubana saika tsareni kana min fada tunda kun rainani akan matan ku kun fifita matayen ku yanzu a kaina kowa kuma yasan da hakan.
Shiru sukayi gaba dayan su babu wanda ya kara magana a cikin su taci gaba da fadin idan bashi yaje ya nemo masu ita ba ai bata taba tunawa tabar diya a kasan nan ba wullakance.
Ko ita maimunan da yarta suna da halin zuwa har wani kasane neman mahaifiyarta watau ka nuna min ka gaji da gorin da nake mata ko ?
Mama kiyi hakkuri idan kince na nemo masu ita kamar hakane tunda ni nakai ita fatima kasan waje har suka hade da wace tasan mahaifiyar maman ta a can ta hadasu da ita.
Tace bakaji zancen ba ta dalilin ka komai ya faru idan ina magana sai a dinga ganin laifina abinda nake gudu ya faru ke nan yake faruwa dakai an mayar dakai wani binan sai abin da suka tsarama kakeyi a gidan nan.
Haba mama koda ace kudi na kashe wurin nemawa maimuna mahaifiyar ta ai ba zai zama laifi ba don na sama masu martaban su ko ?
Martaba wani martaba ga matar data tafi ta bar yarta shekara da shekaru a wullakance nan wata kila ma zaman banza takeyi a can don ba abin mamaki bane hakan ya kasance .
Innalillahi yace tare da fadin Aliyu tashi muje Nasir yana jirana yana kokarin tashi tace kada inji kada in gani ka saka bakin ka a cikin wanan karyan da za ai muna gidan nan.
Basu ce komai ba suka fita cike da kunnan rai suna maijin zafin halaiyar mahaifiyar su da ta kasance halinta a hakan .
Mata hudu da mazan muka kwasa muka tafi gidan mu dasu zasu sauka a can don zasu fi sakewa a can inda kakata tace a wurin mamu zata sauka ita da kanwar ta guda.
Sun yaba da gidan namu sosai don komai a wadace suke yinsa ko wani daki mutum bibiyu suka sauka a cikin sa.
Inda na shiga dawai niya dasu a gidan kamar yadda ake karrama ko wani bako idan yazo maka bakunta a gidan ka.
Sai washe gari ne bayan sun huta anty Summaiya take min bayanin su kamar haka.
Kakan ki itace babba a gidan mu bayan iyayyen mu sun bar kasan nan da mu muka koma gida a cikin bakin ciki take da kyar aka samu tayi aure a cikin dangin mu.
Ta aure dan wan baban mu a lokacin wanda ya dawo karatun likita daga kasan waje lokacin dashi ne ta haifi wa yan nan yaran da kike gani tazo dasu dukan su diyan cikinta ne su biyar maza hudu da macen nan da kukai kama muke kiranta da Binta.
Da yake yan gidan mu duk gaba dayan su suna ilimi muma komawan mu can yasa aka sakamu a makarantar mukai karatu mai zurfi har ita yayan namu dake da aure bata zauna ba.
Mijin ta shine tsohon minister lafiya na kasan mu da tare dashi zamu zo sai dai aiki yai mai yawa yasa ya hado mu da yan rakiya kawai mukazo.
Ni dai kin san a London nake zaune mijina ne ke aiki a can shine nima zamana ya koma London din sai dai muna zuwa gida lokaci lokaci don hakane baki faye ganina a shagona ba kowani lokaci.
Binta batai aure ba har yanzu saidai tana da wanda zata aura Family din mu daya dashi kin san mu bama auren bare sai dan gida wanan ka,idan gidan mune hakan.
Na tausayawa halin dana samu mahaifiyar ki a ciki dama wanda ta shiga a baya don muna zaune a cikin daula ita tana nan tana zaman hakkuri.
Saidai ke Alhamdullahi da gani baki da matsala a rayuwa don jikin ki bai nuna hakan ba a kullun wanan ne damuwan kakan ki a can tana yawan magana kan rayuwan mahaifiyar ki.
Kin san tsakanin da da uwa akwai motsi na jini dake yawan halin da dan uwa yake a ciki .
Sai dana lumshe idona na fara koro mata matsalolin da muka fuskanta a rayuwan mu nan dama wanda muke a cikin sa yanzu.
Har rana yayi sosai bamu sani ba muna zaune muna hira a wurin sai kiran sallah azahar daya karade unguwar muke danji lokacin muka kalli lokaci muka san rana yayi sosai ashe.
Sallah mukayi mazan suka fita zuwa masallacin don suyi sallah wanan zuwan da sukayi shi ya dage muna tafiyan mu a satin mun shirya zuwa can gidan kawu wurin su kakan tawa don su gaisa da ita.
Da sultana kawai naje nabar sauran a gida wurin maria busy muka samu mamu tana faman dawainiya da bakin nata.
Tubewa nayi na karbi aikin nata naci gaba dayi sai mamakina sukeyi wai da cikina tsoho ina aiki haka.
Bayan magariba muka samu kebewa da mamu na tambaye ta ko hjyn su yaya tazo gaisawa da bakin ta ?
Bata shigo ba ta bani amsa tare da fadin kuma hakan ni bai dameni ba tunda Allah ya karba mi addu,a na wankeni daga sherin da ta dade tana min ga mutane.
Da ranan nan tagama fada da Alhaji wai yana rawan kafa saboda uwata tazo inda Allah zaisa naji sai gashi na shiga wurin shi kai mashi tsaraban da suka zo mai dashi.
Nan ta kama fadan karya tana wani kame kame don tasan naji abinda suke fadi lokacin.
Mamu wanan matar tayi nisa sai dai addua ga lamarinta kawai yanzu don abin yafi karfin kishi sai kiyayya a tsakanin mu da ita.
Dazun da kawun ki yazo gaishe su naji suna fada mai suna rokon idan zasu tafi zasu tafi dani inje inga yan uwa yan uwa su ganni.
Da sauri nace meyace mamu ta dan bata fuska tare da fadin yace sai ya zauna yayi shawara da gwaggo .
Da alama ba zai bari ki bisu ba mamu tace ai ba zan yarda da hakan ba kada kiyi wani magana idan ya hana nace mata.
Amma kin san za a tauyeni da yawa idan yai min haka don yasan suna bukatana can ke nan hakan kuma shi zai sa kowa ya fahinci karyan da hjy ke masu na cewa uwata ta gudu ta barni idan har na bisu din.
Wanan gaskiya nasan kawu ba zai hanaki ba idan kun fahinci juna sai dai ban son ki tayar da hankalin ki kan wanan magana kada yaga kin manta da halatcin da yai maki a baya shi da Amma.
Mamu naso fada maki abinda ya faru lokacin da mukaje misau sai dai hakan bai samu ba nan nake bata rabarin abinda ya faru naga hankalin ta ya tashi sosai tana fadin .
Ni maimuna na rasa me muka tare wa wa,yan nan mutane suke neman rayuwan mu haka mu bamu damu da al,amarin kowa ba amma sun sakamu gaba haka ?

ZAINAB IDRIS MAKAWA
17/11/2021, 07:18 - ??5惙5惙5?: Kwanan bakin mu hudu a kano tare damu wanda yaya umar ke faman dawainiya dasu don fitar damu kunyan su.
Dukko da irin hattaran shi da hjyn su takeyi saidai ya nuna mata shi baida ko lokacin su aikin gaban shi ya sha mai kai don ya bar gari shida dan uwan shi.
Don kada tace lalai shidin ne kuyin abubuwan da take ganin ana shigowa dashi gidan don su.
Sai dai kafin ya tafi ya barwa Nasir abokin shi yin komai don bakin a hannun Nasir wanda yake kawowa ta gidana ni kuma sai inba driver ko in kawo da kaina.
Sai kuma ta koma zargin kawu tana fadin shine mai hidima da bakin yake nuna masu shi baida hali yanzu amma gashi saboda zuwan yan uwan mamu yana fitar da kudi yana kashe masu don kawai a yabe shi.
Yace idan nayi laifine yin hakan don kafin in masu da naki yan uwan nasha dawainiya a baya kika kuma manta da hakan da nayi maki yanzu.
Gori zakai min don kawai na fadi gaskiya yace babu zancen gori a ciki sai amsa daidai da maganar ki kinga kenan baga yan uwan maimuna na fara rawan kafa ba ashe ?
Wasa wasa saiga muryan su yana tashi har yakai sauran sassan gidan ana iya jiyo abinda sukeyi wanda hakan baiyiwa kowa dadi ba a gidan.
Bamu dade da shigowa gidan ba wanan abin ya faru da dabara na dauke hankalin su ta hanyar kara karan tv dake aiki ina masu bayanin abinda mai wanka yake fadi.
Hakan ya dauke hankalin su saidai ita kakantawa dake jin hausa tasan abinda ake fadi sarai a gidan kallon mamu tayi tana tambayan ta tace maigidan ne da uwar gidan mu suke dan hatsaniya .
Tace har yanzu ana irin wanan halin a kasan nan da addinin nan daya zaga ko ina ana wa,azi akan hakan mai yai mata haka take wanan daga muryan haka ?
Nace wanan halin tane mama kamar yadda naji diyan ta suna kiran ta nan na fara bata labarin irin gorin da hjy take wa mamu ita kuma tanawa yan uwanta bayani har ga zuwa aurena da danta har rikicin da mukeyi da ita zuwa yanzu.
Suyi da yaren su suyi da turanci ko da dan hausan da sukeji kadan suna kara bamu shawaran yadda zamu zauna da ita.
Kawu ya yarda dasu tafi da mamu don taga yan uwa da wuri koshi sai da Amma tasa baki a maganan ya yarda don yace sai daga baya zai shirya sutafi tare da ita.
Amma tace sam ba zai yuyu ba yaushe zai samu lokaci yadda yake fama da jikin nan nasa yanzu.
Don haka muka fara shirin tafiyan mamu kasan mahaifiyar ta ta dubosu ba karamin kudi muka kashe ba wurin hada tsaraba irin wanda ya dace suje dashi wanda basu dashi can suna bukatan shi .
Da muka fitar da tsaraban ba karamin fada kakan tawa tayi ba damu kudin data bamu yafi kudin da muka kashe yawa .
Da farko munki karban kudin data bamu din saida ta nuna bacin ranta ga hakan kafin in yarda na karba tayiwa kowa na gidan alheri na bajinta saida kowa ya girgiza bayan tsaraban da suka zo dashi aka raba inda hjy ba kunya ta karbe komai da akabata tana cewa ta rage zagin dukiyan da danta ya barar masu itama.
Mamu zata tafi da su yan biyu da mansur karamin danta nan aka shiga zancen ina fauziya zata zauna mamun tace wueun Amma.
Da kaina nayiwa kawu magana zan tafi da fauziya don ta kamamin idan zan haihu a can yaso ya hana saida ya danyi tunane kafin ya barmu mu je da ita.
Yau dai mamu sun daga muna tsaye muna kallon har jirgin su ya daga saida ya bace muka dawo gida inda kusan gaba daya yan gidan kawu mukai masu rakiya zuwa airport din inka debe hjyn su yaya .
Ta daiyi banjin ta ta rakosu har kofan gidan kawu da zasu wuce saidai kana kallon ta kasan naciki na ciki lokacin.
Bayan tafiyan sune muka hau shirin namu tafiyan don komawa London din dan karatun yara dayace lokaci yana kurewa yasa muka bar kasan, sai dai bamu samu tafiya dashi ba don aiyukan dayace yayi mai yawa a nan.
Kusan yanzu watana takwas rabona da london saidai komai ban canza min ba sai dan kara kawata kasa da kullun suke cikun yinsa su.
Muna komawa akakai yaran makaranta harda yar sultana na sai ya zamanto yanzu fafitikan nemawa Fauziya makarantan da zata shiga nakeyi duk da alkawarin wata uku nayiwa kawuna zatayi don nasan idan na fada mai gaskiya ba zai yarda muzo da ita ba.
Yaya ya bugo waya yana sheda min bude ma,aikatar su da akayi a kasan guda lagos guda Abuja na tayashi murna jin komai ya kammalu bayan fafutukar dayasha na shekara da shekaru wurin neman yayunwan abin.
Tuni nayi mai akan zancen mijin Atika yace bai manta da zancen shi ba ai tunda takardun shi suna a hannun shi .
A cikin hiran namu yake fadin yana son ya samu daddy akan maganan Ahmad don yana son suyi aiki a tare dashi tunda kasuwan nasu yanzu baija sosai kuma sabbin yan kasuwa matasa masu amfani da tecnolagy a yanzu.
Sai zancen salma da zai budewa gidan buga ruwan leda na sha ban san lokacin da dadi yasa na sake dan ihun murna ba a lokaci guda don dadin danaji na hakan har kasan raina.
Bayan kwana biyu sai ga salma ta bugo min waya tana min godiya wai yaya yazo da kanshi har gidan su da abin alheri gare su.
Mun dade muna hira har zamu kashe wayan tace wallahi Fatima yaya har tausayi yake bani hjy ta daga mai hankali akan karin auren shi da ta matsa mai yayi.
Ashe su har sun saka rana ba wanda ya sani sai da zancen yaje kunnen daddy akeji a cikin gida koshi saida baban ita yarinyar ya kira daddy don yace baiga kowa har lokacin daga bangaren mu ba kan zancen ga lokaci sai karasowa yakeyi na bukin.
Gabana ne ya yanke ya fadi lokaci guda nace kai lalai kuwa hjy takai wallahi itako salma sai zubamin labarin takeyi tana fadin.
Kin san halin yaya bai nuna abu ya dameshi saida daddy ya kirashi ne yana tambayan shi yake fada mai yadda mama ta tursasa shi har tana batun yi mai baki idan bai yarda ba.
Yace ma daddy yana son a dage bukin har zuwa lokacin da zaki haihu idan kin haihu sai ayi bukin.
Da salma tasan yanayin da nake ciki lokacin da bataci gaba da fada min wanan bakin labarin datake tsegunta min ba a lokacin.
Duk da ina da kishiya amma sunan ta dai ne nake ji na amfani dashi don nida ita tunda ta samu labari bamu taba ido da ido ba har wanan lokacin.
Ban yarda ta fahinci irin halin da nake ciki din ba a lokacin don kada in katse ta da jin labarin idan ba haka ba sai dai inji wanan labarin daga sama.
Wai kin san wani abin haushi ba naje gidan mama saude ba sai ga yar iskan nagani wai tana yawon nuna anko ga yan uwa na bukin.
A raina nace Allah yasa kada yaya ya aminci muga ta tsiya wani iri nake ji gaba daya jikina ya dauki rawa a lokaci guda har abin cikin cikina saida ya juya lokaci daya.
Nace dama ashe zancen yana nan salma amma kinga yaya bai fada min ba don munafuncin maza.
Haba dai Fatima na fada maki ai bada son ran yaya ba fa wanan shirin duk daga mama da yan uwata masu zugata yake fita.
Ke mama fa kin dai san uwatace wallahi lamarin mama sai addu,a kawai don har tana ikirarin idan kun kama yayane keda maman biyu ita a tsaye take kwana kan danta sai dai idan babu boka ko malam a duniya.
Fatima wanan magana ya kamata mama tana fadin shi kan matar danta don Allah duk da take uwata shi gaskiya ai dayace.
Yanzu ya kamata ace mama ta mayar da lamarin ta ga Allah tana istigifar din kuraren tana bayane ba wanan shirmen ba da ake zugata akai ni nasan sai mama ta dawo tana dana sanin wanan abin daga baya wallahi don ba mutanen arziki ta debowa kanta ba.
Allah dai ya sauwaka nace mata don na kasa furta komai akan maganan don idan nace zan furta din zan iya fadin abinda ba daidai ba ga mahaifiyar nasu dake son ganin tarwatsewan rayuwana a kowani hali.
Ita bata ko tausayin halin da nake ciki da tsohun ciki haka a jikina take kiran ai min kishiya jin nayi shiru ban tanka ba tace amma fa tunda nace ban sani ba don Allah in rufata a gurin yaya kada yaji ita ta fada min yayi fushi da ita kuma.
Nace baki da matsala kan hakan anty salma indai nice ba zan mai maganan ba sai idan shi yayi min.
Ajiyan zuciya na sauke bayan mun gama wayan ina mamaki a raina na wanan halin na hajiyan su .
Haka na wuni sukuku saukina ma yaran da basu gida sai hudu suke dawowa har na samu lokacin yin tunanen mafita akan maganan.
Koda yaran suka dawo hakana suka sameni cikin rashin walwala a tare dani.
Ga wani irin bushewa da makogorona suna faman surtun su haka na zauna kamar mutum mutumi ina kallon su.
Gaskiya akace ciwo ya mace sai mace yar uwarta don Fauziya ta fahinci ina cikin wani hali na tashin hankali ita ta dauko

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login