Showing 342001 words to 345000 words out of 419207 words

Chapter 115 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1471

zancen a ranki har kizo ki gujeni Fatima daga karshe.
Idan kin muna haka baki dauki sakkayan da Allah yai maki ba ke nan a zuciyar ki da wanan tunane na kwana a raina Fatima ina tsoron sherin Lami ya rabamu dake nan gaba.
Baffa idan banzo wurin ka ba wa nake dasu nan duniya da zan nuna a matsayin yanuwana na jini idan baku ba ko kadan wanan tunanen baizo min a raina ba baffa na bashi amsa.
Allsh yai maki albarka Fatima dake da iyalan ki banda abinda zan baki sai addu,a a tsakanina dake Fatima.
Saidai ina kara rokon ki da ku boye maganan nan ga mahaifiyarki don idan taji maganan ranta ba zaiyi dadi ba ina kunyar kawun ki Fatima da mijin ki na rasa wani irin hukunci ya dace in daukawa Lami a gidan nan da raina zai min dan sanyi ba.
Baffa tunda Allah ya mayar mata da abinta ta gani ka barta da Allah Alhamdulillahi dai tunda ba wanda wanan abin y???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?aiwa sanadi a cikin su.
Mun dan dauki lokaci tare da baffa har rana ya hasaka muna wurin tun inatsugune har nakai ga samun wuri na zauna yana koro min irin hakkurin zama da umma lami da yakeyi.
Nace a karshe zamu biya wurin Addah mu gaida ita kafin mu koma gida yayi murna da jin hakan.
Mun shirya tafiya manjo tana asibiti ita da su yaya hashimu suna jinyar Sanusi bata san da zancen tafiyan mu a ranan ba saida na tura driver ya dauko ta.
Tana zuwa ta saka muna kuka wai umma lami ta rabata damu ke nan kan abinda tayi muna.
Hakuri na bata tare da kebewa gefe da ita nayi mata bayanin komai yadda zata fahinta dani akan ba saboda wanan maganan zan tafi ba a ranan.
Mun rabu kamar kada in rabu da yan uwana a lokacin musanman kaka ta mafi soyuwa a gare ni na tafi ina tausayawa halin rayuwar da na barta a cikin shi.
Saida muka biya kauyen da Addah take muka dan dade kafin mu kama hanyar kano sai dare muka isa kano din.
Mun samu baya gari ya tafi Abuja a nan muka kwana tare dasu murja gidana sai washe gari nake warning din su kan su boye min sirin gidan mu kan abinda ya faru kada su fadawa kowa wanan zancen.
Sai dana dan hada masu tsaraba da zasu kai gida cikin dan abinda muka samo da wanda muka sayo a hanya na kaisu gida a muna sannu da zuwa .
Na shiga wurin mamu mun dan dade muna hiran gida da ita kafin in fito in koma gida duk da yamma ya soma ina sallah la,asar na kwanta a wurin.
Maria ce ta shigo min da jakkata dana bari a falo da wayana a ciki yana ringing na dauka nomban Baffana ne daya bani ya kirani dashi.
Naji nauyi da kunyar rashin kiranshi da banyi har ya kai ga kirana a wanan lokacin.
Na dauki wayan da sallama na fara gaida shi yace mun iso lafiya lafiya Alhamdullahi ya jikin sanusi ?
Sanusi sai dai muyi hakkuri Allah ya kira abinsa jiya da dare ya kare yanzu ma na kirakine ki kira babba ki mata magana kin san mutumin tane tana nan ta tayar da hankalin ta mun rasa gane kanta.
Banji sauran karashin maganan da kawu yake min ba don tashin hankalin dana shiga a lokacin ya wuce musali.
Gaisuwa nayiwa Babffa mun dade muna magana kan mutuwan Sanusi inda jikina yayi sanyi sosai wanan maganan dolene in fadawa mamu shi babu zancen boyewa a nan.
Gani ni kadai a gidan haka yasa na fito falo muka zauna da su maria ana hira har zuwa lokacin da akai sallah magariba duk bani cikin yanayin dadin rai a lokacin.
Sallah nayi na shiga daki nayi ban kara fitowa waje ba waya mukayi da yaya nake sheda mashi dawowan mu.
Yace yana hanya shima yanzu haka bai samu jirgi ba mota ya shigo zuwa gida shida Aliyu nayi masu Allah ya kawo su lafiya.
Haka yasa danayi sallah isha,i na fito don tanadar mai abinda zaici idan ya isa na koma dakin shi don nice mai gyara na kara gyara ko ina na fito bayan komai ya kammalu na shiga nayi wanka na dan kwanta.
Basu shigo garin ba sai goma da wani abu na dare suka iso gida ina kokarin daga sai gashi a dakin nawa hakan bai hanani mikewa ba ina taron shi da zuwa.
Ya rungume ni a jikin shi yana fadin wanan kara girma da kikeyi haka kamar kin kara dauko biyu a wanan karon ?
Da sauri na daga daga jikin shi ina fadin haba yaya baka tausaya min kake min wanan fatan ina zan kaisu yanzu idan na dauko su.
Ina tausayin ki yace yana kallon cikin nawa tare da ci gaba da fadin wanan cikin duk yafi sauran cikin da kikayi a baya girma.
Nace kasan yanzu tunbina ya kara budewa abincin can kuma ba mai nauyi bane irin wanda nake ci yanzu a nan don yanzu tuwo shine abincina tunda na samu cikin nan.
Tare muka fito zuwa dakin shi saida naga ya shiga wanka na fito zuwa falo lokacin ne maria ke fada min tsaraban da yaya yazo dashi nace ba matsala zan gani da safe idan Allah ya kaimu.
Saida yaci abinci nake fada mai zancen rasuwan da akayi a bayan mu baiji dadin jin hakan ba yai min gaisuwa tare da fadin da safe zai kira baffa su gaisa.
A lokacin ne kuma nake mai godiyan irin dawainiyar dana samu yayiwa iyayyena a gidan mu hannu ya daga min alaman in bar zancen kawai.
Washe gari tunda na tashi da safe na kara kiran Baffa nayi mai gaisuwa nace ina son akaiwa manjo wayan an dan dauki lokaci kafin akai mata waya ta karba tana fadin.
A ruwa da nasan Sanusi ba zai rayuba dana biki kin tafi garin ku dani a daidai lokacin yaya ya shigo dakin tana fadin A ruwa ke kin tafi sanusi kuma mai kula dani a madadin ki ya tafi ya barni yanzu.
Wa zai kula dani yanzu a gidan nan wanan yaron shine idona shine kafata yanzu kuma bashi.
Zama yayi a kusa dani yana sauraren mu tana fadin kizo ki daukeni tun basu karasani ba A ruwa idan baki zo ba zaki dawo ki samu bani.
Manjo kiyi hakkuri zanyi magana da mijina musan yadda za ayi da hidimar ki amma ki bar kukan nan tunda kika iya rabuwa ni kikai hakkuri a baya.
Bayan munyi sallaman na dago na kalleshi zuciyana ba dadi a lokacin .
Ki kwantar da hankalin ki ya kalleni yana fadin rudun tsufane zan saka koda kin tafi can azo maki da ita ta zauna maki idan kin haihu haihu zata dan debe maki kewa.
Kana ganin idan mun dauki kakata hakan ba zai zama matsala ba a gurin hjy matsalan me har taje ta dawo tunda ba kasa daya kuke ba ina zata san taje.
Mikewa yayi yana fadin muje ki ban abinci fita zanyi yanzu sai na biya gida na gaida su zamu tafi wani unguwa da Nasir.
Mikewa nayi zuwa falon na bashi abinci nima na zuba nawa muka karya ya fita daga gidan dan kwantawa nayi a falo ina kallo yara suna min hira sai barci ya dauke ni.
Can a cikin barcin wayana yai kara firgigit na falka ina daukan wayan tare da duban mai kirana a lokacin.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
17/11/2021, 07:16 - ??5惙5惙5?: Da sauri na mike tsaye don jin abinda ake fada min a wayan da mamaki nake kallon wayan dake hannuna ina ayyana lalai idan ina duba aikina zaici.
Na riga dana nasa hakan dama kuma gashi yanzu hakan ya tabbata hasashena ya zama gaskiya garesu sune din suke fada min gasu a garin kano.
Sai dai girma da fadin garin yasa sun rude sun kasa fahintar kwatancen da nayi masu shine nace su jira a airport za a zo a tafi dasu.
Dakatar da tunanen danakeyi nayi lokaci daya don tunawa da nayi suna dakon mu a lokacin a daidai lokacin da nake shirin kiran yaya a wayana sai wayan ya sake daukan kara lokaci guda.
Take sheda min cewa na bari kawai mijin ta ya kira za,ayi amfani da addres din dana basu a samu gidan nace ba matsala.
Murja na kira ta dauka nake fadin kije dakin mamu yanzu ki gyara duk wani abinda bai dace ba dakin cikin awa daya ki tabbatar da kin gama komai nima gani nan zuwa a lokacin.
Ban hakkura da kiran yaya ba don kada in fita yazo bai sameni a gida ba don bansan ko ba zasu dade ba inda sukaje.
Yana dauka wayan yace zahra yaya akayi ne nace yaya mutanen nan iyayyen mamu sune suka kirani yanzu wai gasu a kano .
Yace what nace wallahi yanzun suka kirani suna sheda min shine nike son muje can su samemu a gidan kafin su zo.
Ok ku tafi yace kafin inzo da sauri na shirya bayan mun gama wayan daga ni har yan aikina gaba daya muka nufi gidan kawuna.
Ban shiga dakin mahaifiyata ba saida na gaida kowa na gidan a gurguje kafin in fito zuwa wurin mamu .
Na samu murja ta gyara part din na mamu duk da dai a gyare yake tana zaune suna hira da mamu tare da fauziya nayi sallama.
Ban kai ga gaisheta ba take fadin kin dauka ni irin kine zakice wai azo a gyara min daki kuna daukan kowa zaune yake sai an mashi abu mutum da karfin shi ya zauna jira.
Dariya kawai nake mata ina zama tare da fadin yau ba ranan fada bane gareki mamu don tukwaici ya kamata ki bani babba kan hakan ba kuma tukuicin komai nake so ba sai fauziya zan tafi da ita idan zan wuce.
Wai hauka kikeyi ko me haka Sayadi yau gaba daya kin wani zare min kafin in kai ga bata amsa wayana yayi kara na dauko ina dubawa yaya ne ya sake kirana yana tambaya na su nawa ne sukazo nace ban sani ba yaya don basu karaso ba tukunna.
Ok kawai yace ya kashe wayan shi na dago ina kallon mamu data tsareni da ido tana son jin bayanin wanda zasu zo muke magana.
Nace a hankali mamu yau dai Allah yayi wanan jumma,an zaki gana da mahaifiyar ki in sha Allahu wace zuwa yanzu suna cikin kasan nan ko sun sauka dazun da safe.
Ban rufe baki ba mukaji diran motoci har da jiniya sun tsaya a kofan gidan kawu wanda hakan yayi daidai da fitowan yan gidan kawu gaba daya a daidai lokacin da murja take kwalawa Amma kira ta fito yau ga mahaifiyar mamu tazo.
Hjy dake kokarin fitowa daga part din ta a daidai lokacin tace haukan banza ina wanan magana ya fito haka kuma ga yarnan.
Har kawu sun fito da sauri shida hjy maryam suka tsinkayi muryan murja dake shela a gidan na zuwan bakin.
Kowa mamaki ne ya cika shi a lokaci daya suna tsaye suna kallon juna ba wanda ya iya magana a cikin su a lokacin.
Tabbatar da lalai a nan motar ya tsaya yasa kawu kokarin fita waje ya duba ko su waye wajen don ya tabbatar.
A lokacin na fito zuwa kofan gidan nima mukai arba da wanan matar mai suna sumaiyya wace ke zaune a London.
Ko wacen su na cikin shiga irin na al,adan su nace sai dai ko ba a fada maka ba kasan ko a can din manyan matane sudin.
Don zinare na sarka ne zuwa awarwaro ke nuna kanshi a jikin su sun kai su shidda mata sai maza dake da kama mutum hudu.
Bayan dan bayani da wanda akasa ya rakosu daga gidan gwaunati yayi wa kawu ya basu daman shiga gidan lokaci guda.
A daidai lokacin da Amma ta fito tana fadin da gaskene yau Sadiya ce a garin nan ko kuwa.
Ai kuwa arba sukayi da ita tace hjy kece itama amma tana fadin tsarki ya tabbata ga Allah halima ce kuwa da kanta nake gani nan.
Sai ta fashe da kuka a lokaci daya wanda hakan yasa matar hamshakiyar da aka kira da maimuna itama ta fashe da kuka tana rungume Amma.
Ga yaran maza kamar su dauke uwar don manne mata da suke a jiki lokaci guda.
Mamu tana kokarin fita aka turo get din gaba daya da sauri kawu yake kokarin bude kofan na karba nida murja muka wagale get din gidan suka fara shigowa ciki.
Sai bin gida da kallo suke suna yaren su har lokacin Amma da matar suna rungume da juna basu sake dan uwa ba.
Ji nayi an dafa ni na juya dayan matar wace take yar matashiya a cikin su ne ta dafani na juyo ina kallon ta.
Tace min a harshen turanci kece Fatima ko nace eh sai ta rungume ni tana fadin kamarmu daya dake yasa yar uwarmu ta baiyana ta dalilin mu don ni kika kwaso sak .
Nace harda mahaifiyata don kamartane na kwaso sosai tace da gaske nace kwarai kuwa zaki ganta da ita kuke kama har na kwaso ku.
Muna tafe ake dan fira a tsakanin mu murja dake bayan mu ta rada min Fatima duba hjy kiga ikon Allah yau.
Da sauri na dago na kalli hanyar part din ta tana tsaye a cikin imani da al,ajabin abinda idon ta yake gani muka shigo gidan.
Gaba daya suka ja suka tsaya don ganin mamu dake masu wani irin kallo lokaci guda da sauri matar ta sake Amma tana mikawa mamu hannu alaman tazo gare ta.
Da sauri suka hade lokaci guda har yan mazan dake bayan matar tafe suka rungume mamu suka sakata a tsakiya.
Kowa na sharan kwalla a fuskan shi suna yaren su na can daya bayan daya suke rungumar ta suna mata gaisuwan su na larabawa na sumbata.
Duk wanda ke wurin sai da yai kuka in ka debe hjy jummai da hjy maryam dake tsaye kamar an dasa su a wurin.
A daidai wanan lokacin yaya ya shigo gidan shida Aliyu suna masu sannu da zuwa kafin su dawo inda mahaifin su ke tsaye su tsaya suma.
Can yace min nazo na dan zo yake fadin yaya zamu barsu a nan a waje mu shiga daga ciki mana zaifi.
Nace kukan ne basu kare ba ai yaya sai faman runguma sukeyi suna yare yace shiga dasu ciki don Allah yana gama magana dani ya daga kai suka hada ido da mahaifiyar shi dake mashi wani kallon tuhuma a lokacin.
Don a zaton hjy shine mussababin tono inda mahaifiyar mamu take har suka zo din inda take yanzu.
Mun shiga ciki har lokacin suna bin part mamu da kallo ina kokarin dauko masu ruwa saiga murja na sallama da katon din ruwa da drinks tana shigowa dashi ita dasu Fauziya.
Abinci abinsha da sauran abin baiwa baki duk sai gashi ana shigowa dashi part din na mamu kamar dama an tanadar masu shine.
Banyi mamakin hakan ba dana gani don nasan aikin yaya ne wanan dawainiyar sun sake sosai suna cin abincin ba tare da nuna bakunta ba a gidan ba.
Dakin Amma na nufa don can nakai yara da yan aikina dana zo dasu sai maria ne ke part din mamu tana ba baki abinci.
Hjy maryam tazo har dakin gaida su da zuwa ta dan zauna na dan wani lokaci kafin ta fito suna gaisawa.
Su yaya na fitowa daga gun kawu suka shiga dakin mahaifiyar su don su gaisa sun gaisa din duk da ya fahinci yanayin ta bai hana ya dan zauna tare da ita ba a lokacin.
Muryan ta yaji tana fadin Babawo makirci da sallon yaudara har da kai za a hada baki ayishi a gidan nan .
Subbahanallahi mama mai kuma akace maki na aikata yanzu kuma tace meye baka aikata ba din don yanzu na gaskanta komai dana gani da idona.
An hada baki dakai wurin neman uwar maimuna har wani kasa ka nemota wama yasani ko mai kama da ita kukayo haya a wani kasa.
Aliyu yace haba mama wanan zancen ai bai dace ace anjishi a bakin ba wallahi don Allah mama ki rufa muna asiri ki daina wanan halin haka ?
Yaya za,a yo hayan mutane haka zuwa nan da sunan karya irin wa yan nan mutane har kike tsammanin za a dauko da sunan haya.
Da ganin su kaf yan babban kasa don babu yadda za ayi gwaunati ta turo ayo masu rakiya haka idan basu da mukami a gwaunatin su nacan.
Koma menena dai bai shafeni

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login