Showing 180001 words to 183000 words out of 419207 words

Chapter 61 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1487

tafito hakan yasa masu saurin kuka yin kuka a lokacin.
Suka fice suka barni sai su hjy Asmau da yan uwansu da kawayen ta a gidan.

Ankaisu fa kukace hjy rabi tace wallahi anty yanzu yaya yazo yana fada muna wai harsu asma,u sunje taron amare kawu ya turasu suka tafi.
Ni Alh zaiwa haka ni ni jummai zai tozar, , , sai ta kasa karasawa ta fashe da wani irin kuka lokaci guda.
Abinda bata taba tunane ba a rayuwan ta shine ya faru da ita ayau suma sin tsorace da ganin tana kuka don ba abu kadan ne zai girgiza ta ba a rayuwan ta har ta sake hawayen idon ta ya sauko kasa.
Da kyat suka shawo kanta tayi shiru duk shawaran da sukeyi tana jin su ta kasa furta ko a alokacin.
Sai mikewa tayi tana fadi ku tashi mu tafi .
Ina zamu tafi anty ?
Hjy rabi ta tambayeta cikin son jin inda zasu tafi din don kallon bata cikin hayacinta suke mata.
Wani tsawa ta daga masu tana fadin idan ba zaku tafi ba ku ban makulin motata in tafi ni kadai idan baku zuwa dole suka mike suna mara mata baya.
Sai dai suna zuwa wurin motar ta kawo masu cikas taki tashi kuma lafiya lau aka aje motan don cikinta suka zo gidan.
Wanan ya kawo masu cikas aka tsaya duba masu motar tana ji kamar tabi motar haya ta tafi inda tayi niya din.

Kawu sai hankalin shi bai kwanta yayi sa,a umar yazo gidan ya samu basanan zaifita sai gasu suka jera a tare zuwa falon shi .
Ya zauna shima ya samu wuri ya zauna tare da kura mai ido na san lokaci kafin yace Umar faruq dama ina son ganin ka a yau din nan.
Ga Amana yata nan na baka koda bana raye ban yarda kaci amanan yarinyar nan ba ban yafe wani kalman saki ya shiga tsakani ku ba ko wani mugun hali amana na danka maka kamar nima yadda aka ban amanan ta naga ya dace in ba wani ahalina wanan amanan .
Alhamdullahi kai ka zaba nayi farin cikin wanan zaben naka fiye dana kowa a cikin ku don dama kaine hope dina kanta.
Nasan zaka rike mun ita amana kamar yadda nake rikonta a nan zaka tayani cike mata gurbin da girma bai bari in cika mata shi a yanzu.
Umae faruq kai namiji ne nasan zaka kai hankali a inda na nufa a yanzu don nasan kasan girman amana sosai a wurin ka.
Sabanin yadda iyayyen ku mata suke hangen abin da wani manufa a zuciyar su sai suka fassara abinda kishi a nasu manufan .
Idan ka lura yar nan marainiyace a ckin mu dole mu riketa kamar yadda Annabin rahama yace mu kula da maraye .
Don Allah umar ga amana nan na baka nauyin komai nata yanzu ya rataya a kan ka kazama mata kaine uwarta kaine ubanta data rasa a kusa dakai.
Kan ahi na kasa idanuwan shi sun kade sunyi mai ja da wanan kalaman daurewan da mahaifin shi kemai a lokacin.
Daidai lokacin da kawu yake fadin fatima tana son karatun likita a ratuwan ta saidai ban san naka ra,ayin ba a yanzu ko zaka bari tayi wanan fannin ko kuma kana da naka ra,ayin ne na daban ban sani ba ?
Lokacin ya dago kai ya bude baki da kyat yace daddy karatu sai idan ita da bakinta tace ta gaji dhi insha Allahu.
Kawu yace nagode nagode ubangiji Allah yai maka albarka ya haskaka maka samun ka duniya da lahira nagode kwarai umar da wanan halarcin da kukai min kun nuna min ku diyane nagari a duniya ina alfahari da samun ku a duniyan nan.
Sai kuma ya fashe da kuka saida yayi mai isanshi shima umar din kukan yakeyi kawu ya tsagaita yace mahaifiyan ku takasa fahintana umaru.
Maina rage jummai dashi a duniyan nan duk abinda jummai keso shi takeyi amma kan wanan burin nawa nason raya zumuncin ku da yan uwana ko bayan bana raye ta kasa cika min shi.
Daddy kayi hakkuri don Allah zata gane abinda kake nufi da hakan daga baya ayi hakkuri don Allah mama ta dawo dakin ta.
Ko yanzu ka nuna mata kai namiji ne sama da ita ayi hakkuri don Allah bamujin daddin haka na faruwa a tsakanin ku.
Ai zanyi amma ina son jummai ta gane kuskuren ta ne na yin hakan agare ni ko don watan watarana.
Mama hadiye ne ta shigo falon tana fadin kai tsufin nan da rikici suke ganin umar falon zaune a yanayin da suke da mahaifin nasa yasa tayin turus tace ashe kana nan ma ?
Ai gara dana samay ka wanan tsohuwar ne kakan Fatima take kuka wai a barta taje tayi sallama da jikanta don Allah.
Kawu yace ku barta tatafi mana ku kaisu can don Allah ai zasu iya kwana a wurin ta don yau kawai ku kaita don Allah dai.
Gashi ina gidan zaka yanzu sai ku tafi ka saukesu dayani yace ba matsala daddy idan sun shirya sai su fito.

Gidan salma ta fara zuwa sun samu an fara watsewa a gidan sai gasu mamakin ganinta mutane keyi a gidan.
Ana taron su da zuwa ba wanda ya amsa daga cikin su sai kokarin shiga tana tambaya ina dakin da salma take ?
Aka nuna mata ta nufi kofan gadan gadan Nafisa ne ta fara lekowa don jin muryan su da tayi tace salma ga mama nan.
Wani irin zabura salma tayi tace da gaske wallahi ko nafisa ta fadi da sauri suka nufi ban daki suka rufo dukka su biyu sai kawayen su suka bari zaune a dakin suna mamakin su.
Suna shiga tun falon takebin wurin da kallon mamaki tace ma kawaye ina salma take da yake suna da wayo sun dan san halin da ake ciki sukace ta fita an kirata.
Bata fita ba tana dakin nan hjy rabi tace tana kallon kofan bandakin da idanunta.
Tana cikin bandaki ta rufe ko tace a hasale nan suka hau aika mata da zagi sai ta fito su wuce yau bata kwana wanan matsiyacin gidan wallahi.
Hayaniyan da matan sukaji yasa su shigowa dakin nan suka shiga bata hakkuri tace su suka haifa mata yar da zasu bata hakkuri ?
Ganin haka yasa wasu kiran Ahmed hankali tashe suna fada mashi ranshi ya baci ya kira kawu yana sheda mai.
Umar na shirin barin wuri mahaifin shi kiran ya shigo mai yake fada masu abinda ke faruwa a gidan nasu.
Jummai ko nada hankali kawu ya ambata hankali tashe haka yasa umar dake sa takalman shi tsaya daga kofan falon ya dawo ciki yana fadin daddy wani abin tayi ne kuma cikin sanyin murya yake magana ?
Wai gidan salma suke yanzu ala dole sai sun fito da salma gidan ta jimmai ko nada hankali ?
Barinje gidan daddy a kwatanta mun gida yace a, a kada kaje ai kaima tana tafe gidan ka kaje ka kwashi matan ku tafi ku barni da ita.
Badon yaso ba haka ya bar gidan ranshi a bace sun hadu dasu mama hadiye da saurin su zasu shiga wurin kawu din.
Yasan shine ya kirasu a kan maganan hakana dai ya wuce ya dan jira su manjo suka zo tunda suka shiga motan suke kwarara mai addu,a har yakai gidan baiyi magana ba.
Suna sauka yaja motan ya fita wuri ya samu ya faka ya kira layin habbib yana fada mai halin da ake ciki dashi da Aliyu.
Wai may yasa mama take biyewa su mama rabi ne tana bar muna abin kunya nafara gajiya da halin nan na mama habbib yace.
Yanzu ba wanan ba yaya za ayi shine na kiraku muji Aliyu yace ba daddy yace a barta dashi ba mu bari muji matakin da yake son dauka Aliyu yace.
Ina tsoron kada daddy yai fushi ya hadata da hukuma umar ya fada rai bace yace ba zai kaita ga hukuma ba nasani inji habbib.
Can kuma su mama hadiye na shiga suka samu suna cacan baki da Ahmed yana fadin kema kin san ba don ki na yarda da wanan hadin ba .
Kamar yadda kike kyamana numa haka nake kyaman halayan ki a rayuwana ban taba ganin uwarda bata san ciwon kanta irin ki ba hjy.
Amma jummai kinji kunya idan kin santa ai gasjkiya surikin ki ya fada yau yay da kawo yarinya ki gidan mijin ta kizo masu da tashin hankali haka ?
Sarka mai rikicin gangan yau kan sarka ta rikice a gidan Alh sani har bata iya haduwa don rikicewa.
Sun gwada mata suma yan zamani ne sosai don sun barda abin fadi kafin su bar gidan zuwan kawu mustapha gidan ya tsayar dasu.
Don dole badon taso ta bar gidan don taga abinda batayi tsamani ba gare su dan hakkin daka raina sukai mata.
Tana sababi a cikin motan tace dauki hanyan gidan babawo inje in fitar da yar iskan nan itama kafin in je gidan sauran yau yadda suka hana zuciyana sanyi suma nasu ba zai taba sanyi ba garin nan.

Ina takure a dakin sai ga su Atika da murja sun shigo shigowan su ya dan sani sakin dan jiki na tsagaita kuka da tunanen ba,a sona da nakeyi.
A haka su manjo mama saude da umma su Atika da sauran suka shigo suna sallama gidan ne da shegen gima haka ya hanamu jin sallaman nasu lokacin.
Da tayake Addah tasan dakin ita ta kawo su inda nake ina ganin su na bata rai na bada baya waini nayi fushi muna cikin har akai sallah da isha,i muna ta hira manjo ke fada min ai nan zasu kwana tare dani.
Naji dadi hakan yasa na saki raina muna tsaka da hirane hjy ta fado dakin daidai an kawo muna abinci suna ci ina rabe gefen Manjo dake cin abinci da kyat.
Eyyah lalai har kunga gidancin abinci ko to ba mamaki andade ba a hadu an samu banza ai dole aci yanzu kamar mayunwata.
Hjy rabi ta karbe to keko anga gidan ci ba dole baje anacin dadi ba dole a baje talauci ba a nan ana kwasan banza.
To ba wanan ba kune matsiyatan yan uwan yarinyar nan ko wa kike da suna koma dai wa kike ke ya shafa.
Yadda kuka shigo gidan nan ku tatara kayan tsiyan ku, ku kwashi munafukan yar ku kubar gidan nan tun muna sheda juna daku a wurin nan.
Amma hajiya wanan kamar ba mutuncin ki bane a baka kuautan dan mutum baki gode muna ba sai ki zo da zancen Allah waddai.
Umman Atika ke fadin hakana daga inda ta kare sallah ke kuma a wa kike idan ma baku sani ba ku sani ni dai na haifi maigidan nan da cikina.
Don haka nace ba zai auri yarku ba indai nono na yasha a duniya aure da ita ya haramta gare shi.
Banga laifin Alh ba daya gargadaki ya nuna maki shi namiji ne aikai sha,anin nan salin alin ba zamu bar gidan nan sai idan shi mijin nata yazo ya koremu da yar tamu zamu fita ko minti daya ba zamu kara ba zamu fice maki gidan dan ki.
Addah ke bata amsa tace aiko zan nuna maki bana magana biyu yau ba sai dana yazo ba zaku kwashi tsiyan ku kubar gidan nan.
Nan suka fara cire gyalen su suna shiri fada kamar an jefo part din yace cikin tsawa haba mama wanan bai dace ba gaskiya.
Tsayawa tayi tana kallo shi kafin tace gara da Allah ya kawo ka yanzu maza ka saki yar kauyen yarinyar nan tun kan na saba maka .
Mama ku fito muje waje muyi magana do Allah tace ba ida zan tafi sai ka sakar masu yarnan yau yau ta koma masu gida.
Ya dukar da kai kafin yace ba zan iya ba mama amana take a gurina kamar yadda nayiwa daddy alkawari tun farko.
Ta juya da sauri wurin ya uwanta tana fadin may na fada maku dama na fada maku maimuna ta shanye shi tun farko.
To kaji da kyau ko ubanta ya baka amana saika saki yar nan yanzu ba ko sai na gusa daga nan ba .
Mama kiyi hakkuri don Allah ba zanyi hakan da kike so ba don wani dalilina .
Babawo kai da bakin ka kake fadawa uwarka hakan a kan wanan matsiyacin yarinyar da aka kwaso aka daura ma wahala.
Mama rabi wanan abinda kukeyi bai da kyau kuna zuga mama tana abinda bai dace ba don Allah kuyi hakkuri ku fita daga waje mayi magana.
Baza a fita nace babawo koni ko ita yau a gidan nan ka zabi daya a wurin nan.
Ba zai zabi kowa ba kawu balarabe ne yake fadin haka daga kofa kawu mustapha yace amma dai jimmai kinji kunya dakin santa.
Kin gama da gidan yarki kinzo nan suma zaki tayar masu da hankali don baki san ciwon kanki ba.
Mama rabi zatai maganaz ya daga mata hannu yana fasin malama ba dake muke magana ba don Allah.
Ku fice gidan nan in ba hala ba yanzu hukuma ta futar muna daku gidan.
Hukuma ai nafi son kuje ga hukuma ayita ta kare ba aamuje ko ina ba dole ki fita kibar gidan nan yanzu in ba haka ba zakiga ba daidai ba yanzu kin dai sanni ki san halina.
Sanin waye kawu balarabe tace kuzo mu tafi ai zamu hadu ku rubuta ku aje sai yar na tabar gidan nan.
Kamar yadda mutuwan auren ta yake daidai da mutuwan naki auren ba ke baki da wayau wallahi suka fita suna cacan baki.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
16/11/2021, 23:13 - ??5惙5惙5?: ALHAMDULLAHI ALA QULLI HALIM, , , ,


Jirgin da nake mafalkin shiga yau gani cikin sa saidai bada dadin rai ba don da kunci da takura nake zaune a jirgin.
Kujeran mu daya dashi sai dai tun shigan mu jirgin danaji yayi ajiyan zuciya bai waigo inda nake zaune ba a hankali ina tunane da kewan gida bansan lokacin da barci ya dauke ni ba.
Barci nake sosai har bansan lokacin da na rankwafo kaina gare shi ba barin abinda yakeyi yayi ya waigo kadan yana kallo mm a gani yayi barci nake kaina a saman kafadan shi.
Baison ya tayar dani yasa ya aje wayan hannun shi ya barni ina barcin tare da sauraren saukan numfashi a cikin kunne shi a hankali.
Idanuwan shi ya lumshe a hankali tunanen abubuwan da suka faru a gida suna dawo mashi a rai daya baya daya.
Ido ya bude tare da danke hannunshi guri daya ba komai yasa shi haka ba sai tuna kalamin kowa a kansa kowa zaiyi magana sai ya furta umar ka rike amanan yar marainiyar Allah.
Ido ya kara runtsewa a ranshi yace may yasa suke daureni akan wanan yarinyar hakane ?
Shi wani amana a yanzu zai iya rikewa na wani yaro wanan ai wani sabo aiki daddy ya hadashi dashi ga yarinya karama haka under etheety.
Wani aure zaizo nan yayi da ita kawai daddy yace rainon ta ya bashi yau daba don daddy bane ba wani mahalukin daya isa ya dora mai wanan nauyin haka a kansa shida ko yarsa mimi bai tsaya ya kula da ita ba yaushe ne zai tsaya duba wata babba can.
Shi dai zaiyi kokari yaga ko yaya ya inganta rayuwan yarinyar kamar yadda daddy su ke son yayi din don alkawari ya daukanwa daddy.
Dan tabanin da naji anayine yasa na bude idona da sauri dan bansan na dauki awani haka ina barci ba lokacin.
Ba tare daya kalleni ba yace ki tashi mun kawo idan zamu sauka sai mun huta zamuci gaba da sauri nayi yunkurin tashi sai lokacin na farga a yadda muke.
Ganin ya tashi ya dauki yar jakkarshi yasa nima tashi nabi bayan shi muka sauko daga jirgin binshi kawai nake a baya don ya fini sauri banda lakkan da zan iya jerawama dashi lokacin.
Tsuki naji yayi lokacin da yake jan yar jakka na da mamu ta lodamin kayan amfanina a ciki wanda a lokacin ban san may ye acikin jakka bama.
Wani guri muka shiga bayan mun fito daga cikin haraban wurin inda naga dakuna a jere ya bude wani daki yace in shiga dakine mai nuna wurin hutawa gado da yan abubuwan bukatan daki.
Na zauna a bakin gadon tare da bin dakin da kallo aje jakkana yayi ya fice daga dakin har yakai kofa ya juyo yana fadin zaki iya watsa ruwa idan kina so ki dan huta.
Bayan fitan shi na mike tare da duban lokaci nayi

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login