Showing 351001 words to 354000 words out of 419207 words

Chapter 118 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1503

Ina cin abinci ne sai ga kira a wayana nomban kasan sudan dana gani yasa ni daukan wayan da sauri.
Mamuce a layin take kiran mu a lokacin gaisawa mukayi tare da tambayan kowa a bangarena nima na tambaye ta zaman sudan da mutanen su.
Tace suna lafiya fauziya fa ta tambayeni nace gata naba yarinyar waya suka gaisa take fadawa mamu ta fara zuwa school a nan london.
Bayan ta gama gaisawa da yaran har maria tace su ban wayan na karba ina fadin yaushe zaki koma Nigeria ne mamu ?
Ba yanzu ba ta bani amsa sai naji tace Sayadi mai ya hada ki da mijin ki kike neman tayar mai da hankalin shi ?
Shiru nayi a lokacin na kasa magana saida naji tace ashe baki da wayau sayadi ban sani ba ?
Wani abin yace nayi masa ne mamu kada ki kawo min shegantaka tace min kishi haukane da har kike nema ki zubar da mutuncin ki a idon mijinki.
Sayadi mutumi yana faman kokarin shi a kan ki dama mu duka shine zaki daga mai hankali don wani magana can da bai shafeki ba .
Har kina kokarin jawa kan ki matsala bayan kin san halin da kike ciki akan kine farau kishiya koke ba wata kika shiga kika samu a gidan ba.
Ke mace ina ruwa ki kin san donke za,ayi wanan auren shine don shirmen ki na banza zaki bari har a gane takon ki tun yanzu ?
Me zai dameki da auren shi da zai kara koda shi ya gani yace yana so dame ya rageki dashi a zaman ku.
Ba,a aure ke aka aureki ina wata kika shiga kika sama ta hana ya baki kulawa idan kika nuna rashin damun ki kece da pawer a wurin shi indai kin iya hakuri da gyara da ba mijin ki da yayan ki kulawa.
Namijin bahaushe ana hana shi yawan aure aure ne idan yana da hali yin hakan .
Shiru nayi ina sauren ta tace ki kwantar da habkalin ki Allah ya saukeki lafiya shine adduan mu.
Tadai ta min nasiha karshe kakata ta karbi wayan itama nasiha tayi min kan in kwatar da hankali ina haihuwa in koma makaranta kamar yadda nace.
Idan kin haihu zan ba kakan ki sakon mu na yan nan ta kawo maki ki dinga amfani dashi tace nace na gode grany kamar yadda muke kiran ta dashi.
Muna gama wayan nayi shiru kafin in mike naji abincin dana zuba ya fita min arai ba zan iya cinsa ba kuma a lokacin saboda yadda nake jin zuciyana yai min nauyi.
Na kalli maria da fauziya ina fadin maria kada su wuce tara basu kwanta ba ni zan shiga daki bana jin dadi jikina yau.
Sannu suka fara yin mun ina amsawa da kyat don yanayina daya sake a lokaci guda ina shiga daki na fada saman gado da karfi saida naji dan cikina ya motsa min lokacin .
Wani irin kuka na sake zuciyana cike da tsaban tunane kan sarakuwa da irin kiyayyan da take nuna min haka.
Ina kwance ina kuka sai gashi ya shigo dakin ya dan tsaya yana kare min kallin yadda nake kwance na kifa cikina kamar babu komai a jikina yadda nake.
Zama yayi a gefena yana fadin kin manta kina da mutum a cikin ki ne kika kwanta haka zahra yana magana in a cool voice kamar mai lalashina.
Na dago fuskana dake jike da hawaye nace mai nayi maka haka kake son hadani da mahaifiyata yanzu kuma ?
Don naga kina son wasa da rayuwan kine na kirata tayi maki fada saboda ni yanzu kin rainani .
Don kina ganin muna mu,amula tare ko mai ban sani ba don ban taba tsamanin haka daga gareki ba wallahi.
Eh zakace haka ai tunda kasan abinda kuke shiryawa kuyi min don kawai aga bayana a gidan nan.
Yanzu hardani kike tunanen za a hada baki aga bayan ki idan naga bayan ki in gane me a cikin yin hakan.
Kuka na kara wiwi yaja tsuki yana fadin to meye abin kuka a nan tunda kina ganin zaki kwatowa kanki yanci kuma.
Ko zaki iya fadin wani laifin da nayi maki a cikin wanan magana ke kanki kin sani ban sanda wanan zancen ba sai ta sanadin ki na fara sani.
Don dai kawai ki tayar min da hankali zaki tsiro da wasu halayen da bansan ki dasu ba a baya.
Don wata can da dukkan mu bamu santa ba bamu kuma san halinta ba har yanzu ko tazo mai zata gane a wurin ki yanzu tunda kin gama min da zuciyana ke kadai na sani a matsayin mace ta gari da zanyi alfahari da ita.
Shiru nayi ina sauraren shi don jin abinda yake fada yaci gaba da fadin ko mama ta matsa min sai na aureta ba a wuri daya zaku zauna ba don ba zan hada zuria,ana da wace ban gamsu da tarbiyanta ba.
Dadin kalaman sa da watan kurciya yasa na yarda da kalamin shi na dan dinga sauke ajiyan zuciya a hankali ina rage sautin kukan da nakeyi din.
Hakan ya bashi daman kai hannun shi ya rugumoni yana fadin zaki tayar min da hankali ga banza har yara sun fara maraicin farin cikin ki a cikin gidan nan.
Haka dai yayi tayi min dadin bakin su na maza har na manta da komai na sake jiki dashi muna dan hira sama sama har ya samu ya biya bukatan shi.
Washe gari ban iya fitowa ba har zuwa goma da wani abu ina daki sai danayi wanka na shirya na sauko kasa na samey su zaune tare da yara suna kallo yana zaune a tsakiyan su.
Fauziya da mariya suna kitchen kasancewa yau ranan satine babu aiki ko ina fitowa yaran sukayo kaina suka dugumeni suna gaidani.
Kansu na shafa daya bayan daya ina karba masu dan zama nayi muna hira dasu sai ga fauziya ta kawo min abin karyawa a inda nake zaune .
Lokacin cikin jikina yayi girma sosai ya turo na kara zama wata mace abun kallo da alfahari ga wanda ya mallakeni.
Na jawo abincin na fara ci kenan door bell din mu yayi kara da sauri maria ta mike a inda take ta nufi kofan zata bude .
Gaba dayan mu mun mayar da hankalin mu ga kofan don ganin wanda ke shigowa gidan don bamu faye yin baki ba kasafai sai lokaci lokaci mukanyi bakin.
Dan tsayawa tayi tana magana da wanda ke wajen haka yasa na mayar da hankalina ga abinda nake sha lokacin.
Merry ce da yarta queen sai wata mace da fuskanta kamar na taba ganin ta saidai na manta a inda na san matar.
Wanderful merry tace lokacin da ta karaso taja tsaye tana karewa falon namu kallon har yara da kowa lokaci guda.


ZAINAB IDRIS MAKAWA
17/11/2021, 07:18 - ??5惙5惙5?: Yadda take tsaye tana kare muna kallon daya bayan daya nima haka nake kallon ta yayin da yaran suka mike suka nufi wurin shi sai sultana ne tazo inda nake zaune tana kokarin shige min a jikina.
Daddy who are those kids ?
Queen take tambayan shi tana karasowa gare shi ya dan shafa kan yaran ya kalleta yana fadin they are my kids allso.
Wani irin buga kafa ta kama lokaci daya tana fadin No no no dad i am d only kid you have mummy said.
She just say it to you she know a have those kids also, meet your twin's brother,s and your sister yana nuna mata sultana dake wurina ta haye min jiki don shigowan su.
Da kyat na taushi zuciyana nace masu you're welcome anty have a seat ina nuna masu kujera daga gefen su suna tsaye har lokacin tana karewa yaran kallon mamaki don bata taba sanin yaran sun kai haka ba ashe.
No ba zama ya kawo mu bayi na biyo mijina ne da kike kokarin kwace min daga gareni yanzu.
Murmushi na dan sauke a fuskana ina nuna mata shi da hannuna cikin ko in kula ina kokarin tashi da kyat tace .
What a surprise zan kara gani wani cikin ne kuma a jikin ki again ?
Lalai kun kai macuta na kwarai dake da wanan mayaudarin daya cuceni sai kuma ta kasa karasa maganan da takeyi don hawayen da yazo mata a lokaci guda.
Murmushi yayi a fuskan shi yace you can call me with any name you like na fada maki dama zan baki mamaki ai lokacin da kika tsiro yi min iskancin kan kin gama haihuwa dani .
Fadane sosai ya kaure a tsakanin su lokaci guda ganin haka nayi wa maria data sume a tsaye wuri daya signal da ido ta fahinci mai nake nufi.
Yaran ta fara kokarin ja ita da Fauziya zuwa dakin su don abin nasu yayi nisa sosai kada tazo suyi wani abinda ba daidai ba a gaban su.
Abu kamar wasa karamar magana yana shirin zama babba don hayani sosai sukeyi tun bai daga murya har yakai yana daga muryan shi fiye da nata sunawa juna tonon asiri.
Wani iri nake ji a raina don sai nake ganin hakan kamar rainin wayau ne zata zo har gida tana min wanan haukan haka .
Ya kamata nima in nuna mata nima mace ce don haka ina da yanci kamar yadda take da yancin yin hakan har gidana.
Nan da nan wani courage yazo min yadda nake jin kululun bakin ciki yana rufe min zuciyata lokaci guda.
Look madam merry wanan abinda kika zo dashi ki bari sai idan ya koma can gidan shi kuyi shi can na fadi with full confidence a fuskana.
Gaba daya suka juyo har shi suna kallona da mamaki fuskana babu sauki da gaskiya nake magana ina fadin.
Merry duk wani girma daya dace in baki ina kokari inga na baki daman ki na wace ke gaba a gareni .
Saidai yanzu na gane daga maki kafan da nakeyi yasa har kike kokarin cimun fuska har gidana.
Banje gidan ki ba, ban sakaki a rayuwana ba kamar yadda kema baki sakani ba bani kadai banw kuma kishiyar ki a yanzu da zaki matsa min dani da diyana kina tayar muna da hankali haka.
Na hade hannayena ina fadin na rokeki ki fita mun a rayuwa kamar yadda na fita a naki tun muna ganin mutuncin juna dani dake anty merry.
Ki bincika kiji dagani har shi ga yanan auren mu ba auren son kan mu bane mukayi aurene na hadin iyayyen mu gare mu don haka nake daga maki kafa don nasan mun shiga rayuwan ki a lokacin da bai dace ayi maki haka ba.
Kallon da take min ta mayar gareshi lokaci guda tana mamaki tare da fadin you have another woman again Omar ?
No no no sai ta fashe da wani irin kuka mai tsuma rai lokaci guda ta juya da sauri ta bar falon da sauri queen da dayan matar suka mara mata baya lokaci guda.
Yana tsaye ya huci don bacin rai na dan kalleshi kawai na bar wurin zuwa dakina ba tare danayi mai magana a yadda nake jin zuciyana a lokacin.
Ina shiga dakina kuka ne yazo min mai taba zuciya sai faman tunane barkatai da nakeyi kan wanan rayuwan da muka tsunci kan mu a ciki.
Rayuwane garemu na tsaka mai wuya daga ni har yaya din da yaran mu sai yaushe salama zai samu gare mu wai a hakan.
Ga hjy data sani a gaba ga merry da nata kalan matsala duk kaina ita da mijin ta yanzu kuma ana kokarin jefo muna wata ita kuma ban san da wanda zata zo muna ba dashi .
Ga mama lami can gidan mu da ban san laifin da nayi mata ba take neman halakani ko wani lokaci ta samu sa,an yin hakan gareni.
Da wanan tunanen har barci ya daukeni inda dagani har shi banga laifin mu ba a karshe don rayuwan mu mukeyi ba tare da hassadan kowa a tare damu.
To mu me muka tsarewa mutanene suke kin mu haka wai saboda kawai munyi aure da yaya ne kome haka ke faruwa damune wai ?
Ban fito daga dakin ba sai bayan sallah la,asar na sauko yana zaune tare da yaran suna tula karatun addini.
Mummy you wakeup Abdulsalam yace min dan shafa kan yaron nayi ina fadin karatu kukeyi da daddy ?
Zama nayi dan daura dasu ina sauraren abinda sukeyi muryan Fauziyane ya dawo dani daga tunanen dana fara a lokacin.
Anty kici abinci tace lokacin da take aje min abinci a gabana na dago kai na kalle ta ina fadin na dai gane fauziya kina son ki batani dan kwanakin nan.
Dan dariya tayi tare da fadin naga kamar kina kiuyan zuwa dining kwanan nan kici abincin sai nan yasa nake kawo maki nan din.
Nace ashe kin gane fauziya bana jin dadin zama saman kujerun yanzu ban san me yasa hakan ba wallahi.
Ta juya zata koma kitchen ya kira sunan ta ta juyo da sauri tana amsawa ta nufo wurin shi.
Gani yaya tace tana dan rage tsayin ta don girmamawa Fauziya idan lokacin cin abinci yayi ki dinga kawo mata nata nan .
Da tau yaya ta karba tana tashi daga inda ta dan rage tsawon gare shi a lokacin.
Bude abincin nayi na fara zubawa a plate kafin inji yace dani zaki iya fita zuwa unguwa mu duba su Ramla kafin su tafi Nigeria bukin kannen Ahmed.
Zan iya na bashi amsa ina kai abincin dana diba a bakina don in kawar da komai kamar yadda mamu ta koyar dani nace buki zasu ashe kwanan nan ?
Yace eh bukin nasu ya zama na gidane ya kama dole yaje tunda shine babba kamar ni a gidan su.
Ashe muma in bukin su Nafisa da murja ya tashi zamuje kenan ko yace gaskiya banyi alkawari ba don ba dole bane sai ku kunje.
Dan kallon shi nayi kamar zanyi magana sai kuma na share naci gaba da cin abinci na a hankali mikewa yayi yana fadin zamu dan fita da yaran muje yawo.
Allah ya dawo daku lafiya nace mai ina nuna mai ba komai a raina don har lokacin yana cikin dan guiltynes dani kan zuwan merry da yake dauka zanyi magana a kan yadda tazo muna har gida da cin fuska.
Bayan fitan sune maria ta fito daga dakin su ita da fauziya da har yanzu itama bata iya sake jiki idan yana gidan.
Zaman su a falon ya dan kara sani sakin zuciyana don hira muke sosai dasu don yanzu maria ta zama na jikin mu sosai.
Nan nake masu hiran merry da dalilin da yasa nake dan daga mata kafa kan irin halin da take nuna min wani lokaci.
Basu dawo gidan ba sai da dare wuraren karfe takwas har sultana tayi barci shine ya shigo dauke da ita a kafada ya shimfideta a falo saman kujera.
Ya juya ya fita sai gashi yana shigowa da kaya niki niki a kwalaye da sauri su maria da fauziya suka tashi suna karba a hannun shi suna ajewa.
Daga inda nake zaune na idar da sallah nake mai sannu da dawowa ya karba yana fadin wanan bataci komai ba taki sakin jiki a can.
Wanan kan sai idan da maman ta aka fita take yarda ai fauziya ke fadi ku bata abinci taci yace yana kokarin hayewa sama zuwa dakin shi.
Saida yayi wanka ya fito falon lokacin dagani sai Fauziya a zaune maria taje ta kwantar da yaran a dakin su.
Dining ya nufa ya zauna yaci abinci yana gamawa ya mike yana fadin shi zai shege ke nan muka amsa mai da Allah ya bamu alheri ya shige.
Ban dade ba na mike inawa maria dake kawar da kayan daya shigo dashi kayan yaran ne sai ciye ciyen yara daya kwaso masu.
Wanka nayi na dan dade a dakina kafin in nufi dakin shi na tura na shiga da sallamana yana zaune yana duban computer har lokacin baiyi barci ba ashe.
Samun wuri nayi na kwanta ba tare da nayi magana ba saman gadon shima bai tankani ba sai da ya dan dauki lokaci naga ya mike ya kashe laptop din ya nufi ban daki.
Ya dan jima ya fito ya danyi abinda ya saba yi kafin ya kwanta kafin ya hawo gadon lokacin har barci ya dan fara daukana ko naji hawan shi saman gadon haka yasa na bude idanuna a hankali.
Jinayi yace dani nasan baki barci bako zanso zuwa safe kimin list din abubuwan da kike bukata don zanyi tafiya next week.
Maiyuyuwa koda zan dawo lokacin haihuwan ki ya matso ko ko kuma idan kina iya fita sai na baki kudin ki sayo abinda kuke bukata kafin ki

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login