Showing 414001 words to 417000 words out of 419207 words

Chapter 139 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1427

kai yana fadin why doctor fatima kin san aikin ki kece kiba da muhinmiyar rawa wurin taimaka muna kan maigidan naki har muka kai ga nasara.
Dakin yayi tsit yayin da wasu matan suke ragewa kamar yadda likitan da kawu balarabe suka umurta.
17/11/2021, 07:26 - ??5惙5惙5?: Dan juyo kanshi yayi kadan tare da kokarin mika hannayen shi gare ni lokaci guda sai kuma ya kasa yin hakan don jikin shi da yayi mai tsami a lokacin.
Ganin hakan kawu sani ya fara fadin Alhamdullahi da alama aiki yayi kyau ke nan tunda har ya iya sheda matar shi a yanzu.
Jin hakan hjy ta fara kiran sunan shi da babawo ya jikin naka ya kake ji yanzu ?
Kawu yana ganin hakan ya gane mai hjy take nufi yasa ya bar dakin ta hanyar yiwa matan shi dake wurin nuni da kofa ba bata lokaci suka bi bayan shi suna Allah ya sauwaka tare da adduan kara samun lafiya gareshi.
Dakin ya saura daga ni sai hjy da yan uwanta a tsaye mun zuba mai ido duk da ba magana yake iya yiba a lokacin sai numfashin da yake mayarwa a hankali.
Ganin yadda suke basu ko nuna alaman cewa sun san dani a wurin ba yasa na yanke shawaran fita daga dakin lokaci guda duk da ina son kara duba yadda jikin nasa yake a lokacin.
Wurin Amma na koma na zauna basu fito ba saida nurse tazo tayi masu magana suka bar dakin duk muna zaune a inda muke tare da Amma sai kara kwantar min hankali da takeyi.
Shigan likitan ne ya sa a kirani nazo da sauri yake fadin mara lafiya ne yace a kira mashini ina shiga hjy da suke daga gefen mu suka taso sai dai likitan ya rufe kofan babu halin shiga gare su.
Banji dadin yadda na samu yaya ba a wanan shigar don numfashin shi ba kamar dazun ba da muka barshi.
Isa nayi bakin gadon da yake kwance hankalina a tashe na kai hannuna saman goshin shi lokacin ne ya bude idanuwan shi a hankali yana kallona.
Ido ya dan kura min kamar bai ganeni ba sai kuma naga ya sakar min murmushi a cikkn karfin hali da daurewa na kara matsawa kusa dashi.
Hannuna dake saman goshin shi yake kokarin lalaba a hankali gane hakan da nayi yasa na kai hannuna da sauri na kama nasa.
Ji nayi ya rike hannun nawa sosai ya furta zahra na amsa da hawayen dake zuba a fuskana.
Stop crying yace min a daidai lokacin da likitan ya budewa yaya habbib da Aliyu kofan suka shigo.
Zahra zan tafi in barki da dawainiyar yaran mu ke kadai kiyi hakkuri da hakan zahra haka Allah ya nufa da ra, , , sai ya dan fara shakuwa.
Gaba daya rudewa sukayi Aliyu kan kasa zama a dakin yayi ya fito yana kuka wanda hakan ne ya jawo hankalin sauran mutanen dake waje.
Saida shakuwan ya lafa mai yake fadin habbib ko kasan merry ce ta saka ai min hakan dan yarta .
Wani kuka ne na sake sakewa mai sauti ga hannayen shi rike cikin nawa ya rikesu gam habbib yake fadin mun san da hakan bros don Zahra ta fara fadi.
Habbib i can't survive don haka komai ritsi kada ku bata queen ka hada ta da yan uwanta ku rike min su amana bazan rayuwaba habbib.
Bros ka daina fadan insha Allahu zaka warke habbib ke fadi innallilahi nake iya fada a lokacin sai kalman shahada da nakeyi a fili a cikin gigita.
Dago idanu yayi ya kalleni idon shi gaba daya sun canza kala irun yanan da ake jefawa bawa yayin barin shi duniya sun sauka a idanun shi a lokacin .
Hakan dana ganine ya kara rikitani sosai yaya habbib yake fadin in fita dakin kada in kara daga masu hankali.
Kaina girgiza naki fita dakin don koma nace zan fita din hannayen mu yana sarke da juna yana murmushi jin fadan da yaya ke min a fuskan shi na kara kai dubana gareshi a lokacin idanuwan shi sun kara canzawa ga baki daya.
Allah ya ban hikimar kara furta mai kalman shahada sai naji ya karba min daga haka naji hannayen shi sun sake lokaci guda a take na kira sunan shi da karfi.
Saidai ina Allah ya riga da yayi ikon shi ya karbi abinsa lokaci ya cika babu sauran magani ni din dai da hjy ta tarewa ganin shi take hana in shiga dakin.
Allah ya nufa yaya zai cika a hannuna ta faru ta kare sai mu yanzu tamu ta rage shikan ya tafi abinsa ubangiji ya bamu cikawa da kyau da imani idan tamu tazo.
Likitan ne yayi dan aune aune yaja zanin ya rufe yaya umar a gaban idon mu muna ganin abin kamar a mafalki mai rabawa ya raba tsakanin mu da yaya umar din.
Ban samu kukan ba lokaci daya idanuwana suka kankance ina gani dishi dishi likitan yace yaya habbib ya kamani.
Fitowan mu yasa kowa ya gane abindake faruwa gurin Amma yaya habbib ya kaini itama Amman kuka take sosai hhaka yasa yaya habbib kiran su kawu yana sheda masu abindake faruwa.
Kafin wani lokaci labarin ya zagaye yan uwa da abokan arziki yaya Ahmed ne ya kaimu gida shida salma da Amma gaba dayan mu kuka muke sosai a lokacin.
Dare yayi don haka aka bari sai safe a kawar da yaya zuwa makwancin sa gaba daya lokacin ban san a inda nake ba don rudewa.
Hankalin kowa yana a tashe da wanan mutuwan mai girgiza zukata dayazo muna lokaci guda ga zancen merry dake ta yawo har an fara neman ta a ko ina a cikin fadin kasan nan.
Ba karamin jama, a yaya umar ya samu ba da sukai masa sallah da rakiya zuwa gidan gaskiya ga sheda na alheri da sai a yanzu muke jin irin alheri da taimakon al,umma da makwabta da yaya yakeyi idan yazo Nigeria ashe.
Dama ba a fadin halin ka sai bayan ranka kowa ke fadin albarkacin bakin shi a kanka Allah ya bamu ikon cikawa da imani Amin.
Karfe goman safiyan jumma,a aka kawar da yaya zuwa makwancin sa nayi kuka kamar raina zai fita banci bansha sai idan an tsareni don dole zan dan kurba ruwan kunu a cikina.
Da akai kwana uku yaya habbib yazo akan in koma gidan mu in zauna kada a bar gidan babu kowa don masu zuwa gaisuwa haka yasa muka kwasa muka koma can dani da manjo da Amma da suke tare dani a kowani lokaci.
Iyakata da mutane shine idanu idan kaji maganata sai yara suna kusa dani tunane babu wanda banyi a lokacin ji nake dama mu duka aka harbe da zaifi da barin na da yaya yayi a duniya ni kadai.
Sannu a hankali har na dan fara sabawa da rashin yaya a tare damu inda abin yazo min da sauki har yaran da yake shi yaya mai yawan tafiyane a lokacin da yake a raye haka yasa ko yanzu sai nake ganin kamar tafiya yayi zai dawo.
Hakama yaran kan dameni da tambaya yaushe ne daddy su zai dawo kamar yadda suka saba tambayana idan yayi tafiya.
A wansn zaman makokin da akayine aka samu aka shawo kan kawu ya mayar da hjy dakinta tunda Allah ya raba akan wanda suke fitina a kanshi.
Da farko kawu ya kafe akan har abada bazata dawo gidan shi ba tunda har yanzu bata saduda ba ko bayan mutuwan yaya saida ta tafka wani tsiyan ma.
Don kawai na aiki driver da motar yaya din ba kuma aiken shi nayi haka kawai ba shine yazo min da maganan akwai wasu takardun yaya da zai tafi ya karbo nace ya dauki motar ya fita da ita don sheda.
Shine aka fada mata tunda safe tayi min tas a gidan tana fadin sai a bari a raba gadon yaya da muke kwadayi nida uwata da yan uwana.
Wanan maganan ne yakai kunnen kawu yazo gidan yaiwa hjy tas akan ta fita harkata ta barni inji da abinda ya dakeni na rashin mijina.
Wanan abinda tayine yasa kawu cewa ba zai mayar da ita gidan shi ba saida aka taru dattijan unguwa suka bashi hakkuri da kyar ya yarda da sharadin ba zata kawo mai wani tashin hankali ba a yanzu kuma.
Gidan ya rage dagani sai yarana sai yan aikin dake gidan yaya habbib da yaya umar dama Nasir babban abokin yaya suna tsaye a kan mu bamu nemi komai mun rasa ba a rayuwan mu tankar yaya yana raye.
Mun cika kwana arba,in cif da yake inada karamin ciki wanda hjy sai daga baya ne take jin zancen cikin jikina din tayi fadan hakan kamar tsiya .
Inda take fadin wai da gaiya nake zuba haihuwa haka a gidan yaya dan kawai gadon mijina ga gadin nan dukiyar ai anbar muna muci.
Ni dai tashin hankalin yai min yawa na hjy don kulun safiya da irin fitinan da zata fito dashi duk kashedin da kawu yai mata kafin ta koma bai hana hjy tsula halin ta ba garemu.
Kamar ba dan cikin ta ta rasaba a lokacin gaba daya abinda ya bari a duniya ya rufe mata idon ta sai tsakure tsakuren maganan da takeyi.
Nazo ma kawu da zancen komawa na school tunda yaya dai ya tafi ke nan ba zai taba dasowa gare mu ba kuma gara in nemi na kaina don in kula da yarana da suke kanana tun yanzu .
Don gaba daya ban gane mai ake ciki da dukiyan shi ba kodan ban sawa kaina damuwa da hakan bane a lokacin oho ?
Saida kawu ya tambaya aka fada mai mudfin zan kula da kaina in tsare mutuncina zan iya komawa can in kammala har zuwa lokacin da zan haihu don dama idda ya saura min kuma ga ciki a jikina.
Aiko hjy najin zan koma London da yara ta samu kawu da zancen bata san wanan maganan ba har idan zan koma ne ma sai dai idan za a hadani da wani muje tare don ita sam bata yarda in koma ni kadai ba saboda ba,a san abinda ya bari acan ba.
Kawu yace a kausashe jummai kina da hankali kuwa kin ko san abinda kike fada kuwa da alama dai kamar kin dan motsu.
Tace da hankalina sarai Alh yardane kawai banyi da ba da ko wace mace ba matarshi bace tayi sanafin barin shi duniyan nan don me yanzu zan yarda da wata kuma.
Kiran habbib yayi bayan ta fita don kawu bai kara kulata ba yace suzo yana neman su bayan sunzo ne yake fada masu bukatana.
Sai habbib din yace nima nayi tunanen hakan gareta tun farko sai dai ban sani ba ko tana da daman yin hakan ga addini tunda tayi nisa ga karatun nata.
Kawu yace to ba wanan ba dazun muka gama magana da mahaifiyar ku ta nuna bata yarda Fatima ta tafi ita kadai ba don ba,a san abinda ya tara a can ba kada ta tafi tayi rub da ciki dasu ita kadai.
Innalillahi suke maimaitawa tare da fadin kai haba mama koma mai yaya ya bari a can ai ko fatima taci abinsu ita da diyanta taci bana wani ba.
Ku kuka san da hakan kawu ya fadi lamarim mahaifiyar ku a yanzu sai addua don abin nata kara yawa yakeyi ko yaushe.
Kafin su fita suka aje magana kan za,a bincikeni yaushe ne zan koma don su sani a shiryawa tafiyan mu don sun amince na koma harda yaran gaba daya can har zuwa lokacin da zan kara sakewa .
Naji dadin wanan halarcin da sukai min din don dama yadda za a rabani da yarana nake ji dashi nake kwana nake tashi a raina.
Sai gashi abin yazo min da sauki sosai ba bata lokaci na shirya na koma London nida yarana inda za a dinga kulawa damu a karkshin oga mansur mijin Ramla.
Mun tafi mun bar hjy da tarin dukiyan da take fada a kanashi inda bata san can ma dan nata ya bar arzikin da bata taba tsamanin irin sa ba gareshi.
Don aikin yaya ba karamin samu sukeyi ba wanda yake harkan international samu yake kamar ba gobe a kullun.
Sosai na mayar da hankalina ga karatuna inda nake tare da maria sai manjo da na wuto da ita don kara debe min kewa.
Hakan baiwa hjy dadi a ranta ba sai jefa magana takeyi tana fadin wai rashin tsoron Allah yasa aka turani in koma don ansan abinda aka kitsa na koma na wawashe abinda aka bari a can tunda nan babu halin ci a gareni.
Itace tace nayi ta haihuwa kamar bera dama mun san abinda muka shirya a kanshi merry sawun barawo kawai ta taka.
Duk da ina samun kulawa a bagare daban daban daga yan uwa da abokan arziki na yaya umar hakan bai hanani kewan mijina ba muna tsaka ga exam din shiga matakin karshe na haifo dana mai kama da ubanshi sak wanan ba inda ya ragewa yaya umar shi wurin kama.
Tun fitowan shi na fara kiran shi da habibi da kuma wanan sunan oga mansur yayi mai huduba watau umar faruq.
Gida basu samu labarin haihuwana da wuri ba don nina hana a fada ba saboda komai ba sai don in dan samu natsuwa don hjy na iya tayar da fitinan in dawo tunda na haihu ayi suna a nan gida.
Ban damu da fadan kowa ba a yanzu idan ma har koyone na koyi halin boye sirina a wurin uban diyana.
Tunda labarin haihuwana yazo kunnen hjjy ta dan bada lokaci sai kuma ta matsa sai in dawo gida a raba gado tun tana boye hakan da farko tana fadin in kawo yaron dana haifa su gani har dai ta gaji ta fara fadin in zo asan inda kowa yake zaifi.
Kin dawowa nayi nace duk abinda sukayi daidai ne a gareni ba don komai naki dawowa ba sai don yarana da nake jin kishin kishin din za, a rabani dasu wai idan muka dawo gida haka yasa na share kowa nayi zama tare da yarana a can .
A haka na samu labarin wai hjy dai zaman yaki ta tare yanzu a gidan mu kuma tana amfani da babbar motar da yaya yake amfani dashi.
Duk wanan bai dameni in dai ina tare da yarana hankalina yana kwamce gasu da jikjn girma sunyi wani girma hausa ma ya fita bakin su.
Kodana kara karatuna na samu aiki a can ta hanyar oga mansur mutumin kirki da bai gazawa damu ga business da mukeyi nida mamu ina shiga kashe ina saro kaya in turo nan kano yaya Ahmed yana kula min da sana,a ta.
Bani nazo gida ba saida na share shekara biyar da watani a can koshi don ciwon Amma da aka buga min bata da lafiya na shigo.
Lokacin na kara bunkasa na zama wata wayyaya dani ko dole yanzu yaji shakkan takani kamar yadda ake min a baya.
Don a karskashin WHO nake aikina idona ya bude sosai bani daukan raini a gurin kowa a yanzu.
A bangaren merry kuwa tunda ta samu ta bar Nigeria a furgice bayan barin ta gidan lokacin da abin ya faru ta koma America a firgice tana nadaman abinda ta aikata din har labarin rasuwan yaya yazo mata gashi bata san inda yakai mata yarta ba ya rasu kuma.
Gashi taji labarin ana neman ta a Nigeria ido rufe kan zargin kisan mijin ta da tasa yan bundiga suka zo har gida sukai mai.
Wanan dalilin yasa ra boye kanta ga kowa bata yarda ta kara waiwayan yar nata ba ga rashin ya ga rashin mijin da tayi don bata san abin zai kai ga kisan shi ba.
Hakan ya jawo mata gaba da yan uwan mahaifiyar ta da suka bata shawaran ayi kidnaping din yaran sai ya fito mata da yarta a bashi yaran shi sai gashi plan din ya basheta.
Mun iso Nigeria mun samu Amma abin ba dadi don jikin ya matsa mata sosai tun rasuwan yaya data saka damuwa a ranta.
Muna da sati biyu da zuwa Allah ya karbi rayuwanta mukayi wani babban rashi tsohuwar arziki a cikin mu.
Duk da Amma tsohuwace saida wanan mutuwan nata ya taba kowa na halin don anji mutuwanta sosai a gidan.
Saida komai ya lafane sai ga yaya habbib ya tsiro da wani zance wai yana son a daura muna aure dashi ya maye min gurbin dan uwan shi.
Wani sabon tashin hankali kuma ke nan don hjy naji ta hau bakin ta da bala,i ga kuma matar kawu balarabe da ta fito da nata bala,in ina muka fito nida mamu.
SARKA MAI RIKICIN GANGAN ina wuta su sakani na dawo bauchi wurin gaisuwan umma da ta rasu na samu wanan fitinan kuma duk ina jin su ban

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login