Showing 66001 words to 69000 words out of 419207 words

Chapter 23 - Sarka Complete Hausa Novels By Zainab Idris Makawa.doc

29 Oct 2025

1495

Nima tun ranan nake fushi da Amma don bata kara sakani a idon ta ba har yau ko mamu ta ban abinci in kai mata sai in kira kanne na muje tare zan labe daga kofa su mika mata mu dawo oart din mu.
Yau ma suna gama sallah isha,i ya shigo gidan don cin abincin buda bakin a wurin ysohuwar nan ya rutsani labe ina jiran fitowan kanwata dana ba abinci ta kaiwa Amman nina labe daga kofa.
Girshi na ganshi a gaba lokacin kaina yana duke a kasa don haka banga zuwan shi ba sai ganin sa danayi a kusa dani.
Bai mun magana ba ya shige abinshi kawai falon haka yasa na sauke ajiyan zuciya a hankali ina mai bin bayan sa da kallo.
Kamshin turaren sa da ya bari a gurin yasa na dan lumshe idanuwana a hankali ina kara shakan kamahin a hanci na.
A raina nace sai gyara kamar wata karuwa komai nasan tsab yake kai dukan su ma dai hakan suke da shegen tsabatan tsiya wai su sun waye.
Ina jin muryan Amma tana taron shi daga ciki a cikin fara a tana fadin dan halas, yanzu nake zancen ka a raina don naga ka dade baka shigo ba.
Yace da nai may Amma yana zama yake tambayan ta tayi yar dariya tana fadin ai baka laifin dan gidan Amma zance dai nake na dabi,un ka dabai canza ba a rayuwan ka.
Gaka kana ibandan ka yadda ya dace ko wani dan musulmi yayi dama shine fargaban mu akan dadewan nan dakayi a cikin masu jajjayen kunuwan nan.
Ya dora hannun shi saman cinyar ta yana zama a kasa kusa da ita yana fadin haba Amma idan nayi haka ai ba kaina kawai na cuta ba har daku da kuka bani tarbiya a baya.
Ganin Fauziya a tsaye tsakan falon yace wanan fa kafin Amma tayi magana yana tambayan fauziya da bai sani ba a gidan.
Amma tace kanwar kace yar gidan maimuna da suka fara samu da mahaifin ka a gidan nan yace ikon Allah har ta girma haka ?
Ai auren nasu ya dade kai ko don dai baka gidane kake ganin saurin sa kasan yar tata babba tana nan gidan nasa an dauko ta don barin marainiya haka yanzu abin tsorone tunda ita kadai ta samu a can.
Ko ita ce na gani labe a kofa yanzu da zan shigo tace ja,ira wai fushi take dani bata shigowa inda nake tunda nayi mata fadan bata gaida kai ba.
Fauziya ta karbi kulan abincin asuba a hannun Aisha da ta juye ta fice tana fadin Amma zan wuce sai Amma tace yar nan yanzu banda abin baki sai idan kin dawo anjima don ta saba da bamu dan wani abu idan mun kai mata abinci.
Tana fitowa nayi saurin jan hannun ta muka wuce a hanya muka hade da mutum biyu din suma zasu shiga part din Amma din wanda nasan zuwan dan uwan nasu nan ne ke sa suna shiga.
Suna shigowa daidai lokacin da Amma ke miko ma Umar fura mai sanyi da take saka mai a fridge, Aliyu yayi saurin mika hannun shi ya amshe furan tayi saurin fadin kada ka karasa gawan da ba naka ba dan nan.
Ya kwashe da yar dariya mara sauti yace Amma ai idan naga mai karasa ki sai inda karfina ya kare gara muna ganin kin nan muna wanan fadan dake da murasaki a yanzu sai kin goya yayan mu a bayan nan naki.
Yana fadin haka ya zauna gap da ita yana sake mata nautin shi tace kaga ja,iri kai da ka zama wani jibgegen kato dakai dibeka don Allah kana sakar min nauyin ka.
Duk suka kwashe da dariya habbib da sai lokacin yagama miskilancin shi yai magana yace ni fa na dauka wanan tsohuwar ta daya tun tuni ai.
Hararan shi Umar yayi yana fadin idan ta daya aiko kai ba zakaji dadi ba ina yanzu wanan ya gama fadin sai taga yayan mu ta goya su.
Harara Amma ta aika mai tana fadin kaji min dan banza zaka fadi haka mana tunda ni ba uwarka bace da kace uwayen ka na Dalla su mutu.
Suka fashe da dariya jin abinda ta fada habbib ya sake fadin kaji tsiyan tsofin nan da anyi maganan mutuwa sai su kama zage zage.
Yo ai ko na mutu yanzu na ci gari don na mutu nabar baya a duniya da za, a gani a tuna dani kai ko fa insha Allahu yanzu akwai sa,annin ka dake da diya biyar hudu a duniya.
Da sauri umar yace kai ban fura na in sha kunzo kun cika mutane da surutu muna shirin buda bakin mu mai dadi.
Dama shi ya shigo dasu zancen mutuwa suka kara fashewa da dariya gaba dayan su tace barin karo ma wa yan nan yan kwara kan sun bar abincin suna turawa can sashen uwar su sunzo nan zasu sauke muna rani.
Da sauri habbib yace bar abinki indai nine furan nan bai damay ni ba sai Aliyu yace shikan zai sha ta shekaran jiya tayi mai dadi sosai daya sha.
Tace dama ban taya maka ba miskilin banza kawai idan anyi magana kace an matsaka wallahi kuyi wa kanku fada kuyi aure haka na idan ba kuna son mutuwa a haka bane.
Bata rai sukayi suna fadin da anyi dan magana ku matsawa mutane suyi har nawa muke yanzu da zaku dinga muna zancen aure.
Ido Amma ta ware waje tana fadin kai dan nan kace nawa kuke idan da a kasan nan kake da yanzu bamu dade da shan bukin ku ba har ma matayen ku sun haihu kila.
A hankali yake shan furan shi bai kula da zancen su ba kamar ma bai wurin a lokacin sai da tace har kai nawa gaskiya ina dokin ganin auren ka a rayuwana.
Dan murmushi ya sake a gefen fuskan shi kafin yace Amma kwantar da hankalin ki kamar kinga aurena ne ai do yanzu ni kusan magidanci nake a idon ki.
Tace da kyau dan albarka shiyasa nake kara son ka a raina ba kamar wa yan nan ja,irai kake ba yanzu gashi naji magana mai dadi a gurin ka.
Ya kamata ace kun mayar da hankali rayuwan nan yanzu tsada take da shi sai kaga an dauki yaro karami an bar mu mu tsofi.
Amma bari dai in huta akwai maganan mai muhinmancin da nake so muyi dake a natse idan na samu lokaci.
Shigowan mamu falon gaida Amma da shan ruwa yasa sukai shiru gaba dayan su don tun zuwan su ba wani gaisuwan kirki a tsakanin su ko yanzu da tasan sunan ba zata shigo ba.
Ta shigo da sallama ta kai kasa tana gaida gwagon nata kafin ta juyo wurin su tace barkan ku da shan ruwa ya gajiyan tafiya ?
Suka amsa ba yabo ba fallasa a fuskokin su Amma da taga yanayin su tace haka ikon Allah yake yau ga maimuna ta zama cikin iyalin mahaifin ku.
Abin Allah bai karewa a duniya wanan rubutace ne daga Allah akwai rabo a tsakanin su idan rabo ya rantse sai mai shi.
Zanso kada ku biyewa iyayyen ku ku maza ne kunsan abinda Allah ya halasta kanku ko ku din nan haka yana iya faruwa a kanku don ba wanda ya wuce kaddaran sa cikin ku.
To baki kike muna muma muyi auren cin amana nan gaba habbib yayi gatsal ya fadi yana kallon Amma da ta tsaya tana kallon shi sarara.
Umar yace what noses talk kakeyi waye a ciki dan cin amanan mahaifinka ko ita da take zaman kanwar mahaifin namu kuma macen aure a wurin shi yanzu.
Ban son kuna saka kanku ciki shimay gin don ku maza ne ba mafa ba ya juya gurin mamu yana fadin maimuna kiyi hakkuri da abubuwan da suke faruwa a gidan nan.
Sai dai ba za mu so jin kuna yawan tashin hankali da mahaifiyar mu ba don kwanciyar hankalin ta yanzu shine namu.
Sai da ta murmusa tace ,
Haba Umar ko wanda zai tayar wa hajiya hankali na gani kasan ni mai tarewa ce ko banza don kishi ya hada mu yanzu kuma sai idona ya rufe .
Sauran dai tunda wan yayi magana su basuga abin magana ba don da ta nasu cema da bai tankawa maimuna din ba yadda suke jin zafin ta a ransu, kan ta hana uwar su shakat a gidan ta.
Salama tayi masu ta fita daga shiyan don ba zata iya zama ba suna gurin har takai kofa amma tace watau mutumiya ta fushi take dani dai kan nayi mata fadan gyara kayan ka sai kuma ta dauki fushi dani.
Gwago ba tazo ko dazun kawo maku abinci ba tace bata shigo ba yar nan karama taba ta shigo min dashi.
Kyale ta kurciyane wataran zata gane gaskiya na fada mata ai mamu tace haba gwago a kyaleta kamar ya karama da ita tasan fushi da babba haka.
Tace na dai ce ki kyale ta sanda zamu shirya kina ina ai fushin mu bai kai ko ina da ita ina zaune zata samay ni nan nasan ko yanzu ta gaji katfin hali dai ne irin nata.
Bayan wuce wanan mamu part din nasiha ta kara masu wanda yasa suka dan rage jin zafinta a ransu kan auren mahaifin su da tayi tana zaman kishi da uwar su inda Amma ta lurar dasu fa,idan abin.

Ina kwance saman two seater na dunkule a wuri daya ga goran ruwan sanyi a gefena haka nake da zaran ansha ruwa banda katabus a jikina duk sai jikina ya mutu sai ruwa da zanta sha a cikina idan nayi azumi.
Mamu ta shigo tana fadin kin kuwa je kingaida mutanen gidan nan da shan ruwa sayadi ?
Na dago kaina da kyat ina fadin ban tafi mamu so nake in dan huta tace sayadi may yasa magana daya bai huda kunnen ki ne ke ?
May ye a cikin gaisauwa idan kin je ba sai ki dawo ki kwanta ba har na mike zaune ina bata fuska don ni banga wanda ke shigowa part din mu gaida ita ba yaro da manya na gidan.
Amma ni sai ta matsa min kan sai naje na gaida su wanda zuwan bai amfanani da komai sai bacin rai wata ma son karta karba haka zata kyale ni a tsaye kamar basu ganka ba.
Naji tana fadin watau ke ba ai maki magana kiji a gidan nan yanzu ashe fushi kike da gwagona don kawai.
Ita Amma ta faye surutu shi yasa na kama kaina da ita a gidan nan haka kawai zata sani gaida mutanen da basu ganin ki da daraja ko kadan kowa fa yasan zafin uwarsa mamu.
Hannu ta miko min da dakuwa tana fadin sannu mai uwa ai ban san kin san zafina ba don banga kina bin magana ta ba ke ma.
Na mike ina fadin ke mamu ai duk abinda mutum yayi kanki bakya gani ni dai gani zan je gaida su tace fauziya tabini ida banje gurin Amma ta fada mata idan mun dawo.
Da shiyan hjy maryam muka fara shida ke kusa damu inda na samay ta tana uwar daka sai yaranta neva falo ina shirin fita ta fito tana fadin A ruwa ce an shigo gaidamu ko anzo ganin abinda ke nan .
Nace abinda ke nan hjy ai akwaishi a gurin mu kila ma na aurin mu yafi na nan don yawan ku yafi namu a can.
Ina fadin haka na juya ina jin yar ta na fadin tau rasa kunya yau mommy mu zakiwa rashin kunyar naki ?
Uwar tace kyaleta tayi aiko ta dama akayi ta fada min magana tunda itace bata data ido ni dai na wuce ban kula ta ba.
Shiyan hjy jummai tun bamu shiga ba nake jiyo dararakun su da yaran ta haka yasa nasan suna cikin shiya na shigo da sallama ta ban san wa ya karba a cikin mazan ba.
Daga kofa na tsaya ina fadin hjy ina wuni banji ta amsa ba na sake fadin ina wunin ku ansha ruwa lafiya sun baje a kasa gaba dayan su suna buda baki ?
Lafiya aka sake amsa min daya daga cikin mazan da ba zan tantance muryan ko waye a lokacin ba cikin su na juya abina na fita.
Part din Ammace karshe da muka shiga da sallama muna shiga sai mama hadiye ke fadin kai yar nan kina gidan nan ban saki a ido ba kwana biyu ?
Kya ganta kwana biyu tana fushi dani tun ranan da saudaki ya sauka a garin nan a, a hajiya kems kya mata magana haka a cikin mutane bayan kin san yadda take mutanen nan ?
Yo ko basu so dai ina sai sun ganta a gidan nan kamar yadda dan kowa yake cikin gidan nan in banda lalacewan zamani A ruwa ne wai abin kishi gin yan gidan nan ?
Na kai zaune ina fadin mama ansha ruwa lafiya ya ibada ?
Tace ibada Alhamdullahi faima ki bar fushi da hajiya don kada ta shammace ki kinji.
Naji mama har karana takai gun mamu wai ina fushi da ita ban shigowa wurin ta don hadin fada kin san mamu da tsohuwar nan haka yanzu ta hauni da fada.
Salati Amma ta saka tare da fadin yanzu yar nan ashe sai da tayi maki fadan dana hana ta nace ai na kare da fadin ni dai bani fura insha in an jima.
Kinkoyi rashin sa, a don yanzu samari nan suka shaye furan sai dai idan wanda suka rage gashi ba yawa ki dauka.
Nace kai amma dai Amman nan ni zan sha ragowan wasu katai can da sauri ta tareni tana fadin yanzu ragowan yayyen naki ne ba zaki sha ba yar nan ?
Bafa zan sha ba amma nace ina mikewa ta kara fadin ga na jiya nan baiyi komai ba ni sai in sha wanan din.
Amma in dai shima ragowar su ne ba zan sha ba gaskiya tace wai da gaske kike baki shan bakunan su sai ta kyalkyale da dariya da ban san ma,anan shi nidai na shiga kitchen wurin fridge na dauki furan a cikin gora nayi masu sai da safe na fito.
Mun samu mamu tana cin anbinci take fafin fauziya ta shiga ko tace eh mamu sai na daga mata goran furan dana karbo a wurin ta.
Nan dai ta kara yi min nasiha akan hakkuri tana cin abinci muna dan hira sai fauziya tace mamu ki bar tura anty gaida hjyn su anty ikilima tana zagin antu idan munje .
Ita kuma hjyn su anty Nafisa sai ta kama hararan mu bata karba muna gaisuwan mu kullun.
Kallon inda muke tayi tare da fadin wai abinda take fadi gaskiyane sayafi nace gashi ko fauziya ta fada kullun haka muke dasu wai leken asirin abinda sukaci kike turani yi.
Kai ta gyada tana fadin karki damu da wanan mu dai muyi kokarin sauke hakkin mu na zama a tare dasu da Allah ya shari,an tawa musulmi nace insha Allahu mamu.
Don ban son zancen yayi gaba nace mamu kunyi waya da Addah na yaya manjo take ciki ina son jin muryan ta.
Ta dan tabe baki tace wallahi kwana biyu ban samun wayan ta ko da nackirata lambar baya shiga.
Mikewa nayi tsab ba tare da magana ba na shiga daki wurin tsofin litatafaina na nuna na kama bincika sai ga abinda nake nema na gani can kasan kayana.
Da sauri na fito zuwa falo inda nabar mamu a zaune ina zuwa na dauki wayanta na shiga loda nomban mahaifiyar Atika a ciki ya fara ringing can aka dauka.
Da sallama nima na amsa masu mamu ido kawai ta tsura min lokacin bayan mun gama gaisawa ne nace Umma Fatima ce.
Wata fatima sai na rasa abinda zance mata don kunya tunda nazo ban taba kiran su sai yau din dana kira layin don ina bukatan jin muryan kakata.
Wace fatima nace da sauri nace ta kano yar wurin manjo makwaciyar ku da sauri tace fatima kai amma yar nan yar kin tabbata yar halasa da yamman nan mukai maganin ki fa.
Fatima shiru haka tun tafiyan ki ba kira ni ina dauka baki da layin mu ne yasa baki kiramu ba gashi kuma ranan nayi rashin azanci in karbi layin mahaifiyar ki.
Umma kuyi hakkuri ba waya a gurina ne yanzu ma ina tone tone naga lambanki da na taba rubutawa ranan shine na kira ko zai shiga.
Aiko muna lafiya sai naji kunyar tambayanta wurin manjo sai ita din tace min kakarki ko ba lafiya sosai don har Addah ki ta shigo dubata.
Da karfi nace

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login