Showing 219001 words to 222000 words out of 270738 words

Chapter 74 - NAMA YA DAHU ROMO DANYE COMPLETE TRUE NOVEL BY BADI'AT.doc

zumunci.
Harga Allah ina jin farin ciki sosai inna ganni a cikin dangin Dada, ina matu?ar son Dadane.
Gaga_gaga muka komar da karatunmu zuwa gidan Dada. Inna gama dasu BaWWo da Amaduyal sai in koma wajen Dada itama in mata ?ari a Qur'ani. Nayi iyakar yina dan ganin na koya ma Dada ba?i amman dai ta kasa koya, sai muka ha?ura nake yi mata Qur'ani da hadisi. Su BaWWo kuma Qur'ani, hadisi, da koyoon ba?i nake yi musu.
Cikin sati guda ba sai makaranta ta girma ba, ma?otansu Dada duk suka shiga makarantata ina koyar dasu inajin nishaWi, in sati yayi su bani kuWin laraba nera ashirin_ashirin. A cikin sati uku na tara Walibai talatin cib duk sati ina samun kuWin laraba nera Wari biyar banda su BaWWo. A cikin sati na huWune nake sanar dasu zanje birni amman bazan jima ba in sha Allah.
Gaga_gaga na shirya tafiyata ranar talata na shiga Kano da tsaraba rigi_rigi kai tsaye gidan uwani na yada zango.
A tsakar gida na tarar da kishiyarta tana wanke kayan jarirai, Ummi ?anwar uwani kuma tana wankin kayan jini.
"A'a Anty Iyabo har kinzo? Ko dai tun tana nakudar ta kiraki a wayane?" Cewar ummi da tazo ta tarbeni.
Ta sauka kenan? Ni da ?auyenmu ba sabis ya za'ayi ta kirani ranaku kawai na kintata na tawo. Yaushe ta haihu?"
Kishiyar Uwani ce ta katse mana hanzari ta ganyar gaisheni a turSune.
Fuskata a sake na amsa mata ni da ummi muka rankaya ciki. Hajiyansu Uwani na ciki ita da Hafizun.
"Iyabo kece da magribarnan maraba"
Wallahi kuwa Hajiya. Saina taki sa'a ashe ta sauka?"
"E ta sauka, zauna ga ?ar taki ki Wauka, bata fi minti talatin da haihuwar ba, ita ko wanka batai ba"
Zama nayi na amshi yarinyar tubarkalla da'ita ga hanci.
Gaisawa muka yi da Hafizu sai naga ba yadda muka sababa. Hajiyace ta katsemun tunanina ta hanyar cewa da Hafizu.
"To ya rage a tsakaninka da Uwani Hafizu. Ta riga data haihu idda dai ta ?are. Sai kaje ku sasanta inta amince maka sai a sake sabon Waurin aure. Ni kam tunda Iyabo ta iso zan tafi"
Hajiya ta tashi ta fice. Ni wallahi mamaki ma ya hanani yin sallama da Hajiya. Uwani kawai nake kallo, ita kuwa sai shan shayi take yi a ?aton jug.
"Iyabo tunda Allah ya kawoki komai zai zo da sau?i nasa. Kuskurene ya shiga tsakaninmu da Uwani har takai da na furta mata kalmar saki. To Allah cikin ikonshi Wazu ina tasha ana mun lodi sai kawai sanarmun da haihuwarta akayi. Kinga idda ta sauka a kanta. Ki tayani bata ha?uri ni ko nawa take so na sadaki zan nemo in bata. Inma so take yi in yi mata akwati wallahi zanyi"
"Iyabonce zata sa in koma sabida uwatace? Ai wallahi kama ji na rantse na gama aurenka kenan. Kuma yara zasu koma hannunka babu yaron da zan ri?e. DaWine ma yayi maka yawa in ciyar da kaina da yarana, in biya musu kuWin makaranta akan mitsiyaciyar matarka mai kama da bulugari Ni Hafizu ka jefa da kalmar saki. Ai aure da kai har duniya ta naWe. Gashi can za'a shiga sallah kayi da jiki"
Kasa?e ni dai na kasa magana. Tashi Hafizu yayi yana sharce zufa har ya kai bakin ?ofa yace.
"Iyabo ki taimakeni. Wallahi inason Uwani. Jarabarta ce duk taja mana.
Jeka Hafizu zamu tattauna in sha Allah za,a samu haske"
Godiya yayi mun ya fice.
Uwani kar kiyi haka. Ki tuna Hafizu na sonki sosai. Sannan ki duba yara"
"Iyabo in kina so ?awancenmu ya cika. To ki kaso aurenki kizo ki maye ma Hafizu gurbina mana. Ni ba tsuntsun soyayya bace da soyayya za tai ta jan rayuwata kamar ke da kika zama bagidajiya ba
Jibakki yadda kika dawo fa ruwan kwara_kwara. Ni bana ma son namiji mai nacin soyayya kin ganni inason a dinga barina in samu sarari, ba ko da yaushe nake son takura ba.'
Le?owar ummi ce ta katse Uwani.
"Anty an kai ruwan wankan kije kiyi"
Fita Uwani tayi, ni dai nayi jigum sai ga kishiyar Uwani ta shigo da kulolin tuwo dana miya, harda gaushi. Itama da ciki a jikinta.
Ajjiyar zuchiya na sauke na ajjiye yarinyar a gado na sakko da su Hassan duk bacci suke yi na shinfiWesu na fito. Alwala na Waura na koma ciki, na tadda kishiyar Uwani na zaune tana cin tuwo.
Ina kan rama sallolina Uwani ta fito wanka. Sallamar sallar magriba nayi wacce tayo daidai da shigowar Hafizu ya nemi waje ya zauna harda leda a hannunshi cike da balangu.
"Gashi kici ki sha tea, gobe zan shigo da kayan tea Win. Ke kuma in kin gama sai mu tafi ko?" Yace da matarshi.
A_a Hafizu ku dukka ukun inaso zanyi magana daku. Domin na fahimci kamar akan amaryarka ne aka samu wannan saSanin"
Ai sai ya gyara zama yace.
"Alaja kinga maganarnan a batta kawai babu abinda zata haifar sai fitina. Kuskurena Waya na sakinta da nayi ne"
"Sabida kana ba?in ciki da Waukakar da Allah yaimun akan kasuwanci ba. Hassadarka harta fito fili Hafizu na gama zama da kai Allah shine shaidata nayi iya yina. Iyabo na ro?eki da girman Allah karki tursasani komawa gidan Hafizu ki barni in auri wanda a ?alla ko abincine zai iya bani. Wahalar Hafizu waccece ni Uwani ban shaba. Ke kuma ki ficemun daga gida kar in sake ganinki a gidana. Yaranku zuwa anjima in suka dawo daga gidan Hajiya zan rakosu da kayansu kije ki haWa da ubansu kiyita rainonsu gaki ga rijalu tsohuwar makira"
A zafafe kishiyar Uwani ta tashi ta fice harda doka tsaki dogo. Uwani ta bita da manyan ashariya ba sai faWa ya tashi ba gaga_gaga da ?yar ?urar ta lafa wallahi Uwani dake jego itace har waje wai zata daki kishiyarta sai ma?ota aka jayeta ta shiga.
"Da ki tsaya mana kiga. Tsohon mitsiyaci saika bita ai."
Ni dai da ?yar na dinga jan Uwani har cikin gida. Hafizu na koma na samu a waje yama kasa tafiya.
Hafizu kayi ha?uri ka Wan Wauke ?afarka zuwa Wan wani lokacin inta huce. Kafin in koma zanyi iya yina"
Murmushi yayi yace.
"Alaja karki Sata yawun bakinki in dai ta balbalin ce ba zata dawo hannuna ba. Ki mata godiya a bisa halaccin da taimun Uwani ta zauna dani cikin ba?ar wuya. Bana mance sanda take fita ta nemo mana abinda zamu ci. Sannan bana mance sanda talauci yasa ni da'ita duka muka bar ?asar dan neman rufin asirin kanmu dana yaranmu. Iyabo kice mata Nagode ?warai Allah ya bata miji nagari wanda zai tausaya mata"
A wajen ya tafi ya barni. Kai na girgiza na koma cikin gidan.
Gaga_gaga haka muka wayi gari cikin hukuncin Ubangiji. Ina tsakar gida ina ma ?an biyu wanka, Ummi kuma tana mana dumamen abincin kari. Uwani kuma sai gyaran Waki take yi ta kwanta ta hutama ranta ta?i fur. Kayan Hafizu ta jefo tsakar gidan a jaka. Ni da ummi me zamu yi in ba dariya ba. Haka Uwani ta kuma jefo kayan yaranta tsakar gidan.
Wai Uwani da gaske yarannan mayar dasu zaki yi gidan Babansu, batun karatunsu a ina zai kwana. Bakya jiye musu wahalane?"
"Bana jiye musu. Iyabo ke bakisan yaran da suka sha wahalar rayuwa Allah ya fi Waga darajarsu ba? Wallahi ko wayo da sanin ta kan duniya sunfi. Batun makaranta ba dole sai sunyi karatu zasu rayu ba. Wallahi bazan ri?e su ba gidan ubansu zasu koma"
Muna cikin wannan jawabin sai ga Zaliha da yaran sun shigo. Suna ganina suka yo kaina da murnarsu. Jakar tsarabarsu na mi?a musu.
"Zaliha da ke da ummi ku kwashi kayannan ku kai gidan Hafizu ku haWa har da yaran." Mai sunan Hajiya dake itace babba tace.
"Umma can zamu koma?" Uwani tace.
"Canne yafi dacewa daku Ummu Kulsum. Maza bi su ummi su kaiku"
Uwani ta kaWa yarannan ko a jikinta. Harara ta doka mun ta zuba mana Wumamen tuwonmu muka shige ciki. Saida na shirya ?an biyu tsab na zauna muna cin abinci muna hirar yaushe gamo. Harna ba Uwani labarin naci gaba da yin makaranta kuma abun dai kamar zai Waure.
Ki taya ni da adda'a dai Uwani. Inaso in zan tafi in yi sare_saren kayan kwalliya da magungunan mata ko da iyakar tsumi ne in jaraba. Amman meye shawararki tsoro nake ji, amman kuma zaman haka ba daWi. Ga Hamma ni bansan ma yaushe zai dawo ba."
Saida Uwani ta barbaWa yajin daddawa ta saka lomar tuwo ta haWiye kana tace.
"Hakanma yayi Iyabo. Tunda ai dama hannu mitsiyaciyar kishiyarki ta saka miki. Yanzu kuma da izinin Allah munfi ?arfinta. Zan kaiki gidan Sharubutu ya baki rubutu ki dinga sha. In sha Allah sai kin zama Hajiyar rugga Iyabo. In abubbuwa suka bun?asa sai kici gaba da Wakko kaya daga saudiyya. Ni nan da wata huWu ma zanje saudiyyan da kaina zan saro kayan. Kinga lokacin in al'amura sun warware kasuwa ta buWe miki sai mu tafi tare ai. In ma Hamman bai dawo ba sai ki tambayi uwar mijin naki. " Dariya nayi nace.
Da wanne kudin duk za'ayi haka Uwani?"
"Ke dai kiyi ta adda'a kawai. In dai Allah ya dafa miki aka ci gaba da siyan kaya a hannunki zan sai da ?aramin gidana in ara miki jarin ki juya ki samu alkhairi. Iyabo ai hakan shine ?awancen"
Mun daWe munata tattaunawa da ?yar wajajen la'asar na yakice bayan na gama yima Uwani tuwon dare na le?a gidansu Iyaa Debisi.
Suna shago kamar kullum Iyaa Debisi ta hangoni, saita soma rawa tana ma ?an biyu wa?ar sunansu da yarbanci. Iyaa Kokodeen ce ta fito ita ta Wauki Hassan Iyaa Debisi ta Wauki Usaini.
"Masha Allah yara sai girma suke yi. Ke ma ba laifi kinyi kyau ba kamar sadda muka je suna ba. Amman jibi shigarki dai irinta fulani kin Wauko koriyar atampa kin saka"
Cewar Iyaa Kokodeen kenan. Iyaa Debisi kuwa naci sa'a bata ce komai ba jikokinta sun janye mata hankali.
Ina shiga gidan na tarar da Bose ta fito tana son zata tafi gida da yaranta.
"Ahhh Antimi Iyabo. Kece da magriba haka muna shirin guduwa?"
Rungume junanmu muka yi muna farin cikin ganin junanmu.
"Ina yaran kuma?" Ta tambayeni.
Suna wajen su Iyaa a waje.
Na bata amsa ina Dariya.
Matan gida duk suka shishshigo ganin yara bayan su Iyaa sun shigo dasu. Yaran suna da mugun farin jini sosai da sosai. Ni dai har nayi sallar isha, na fita na raka Bose da yaranta suka tafi gida. Yarannan suna hannun Iyaa Debisi.
"Ina Daso, da mai gidanki, da kuma ?an uwan naki?"
Lafiya ?alau Iyaa. Dada tace in gaisheki sosai. Ga tsarabarta nan, wannan kuma tawa ce a raba ma su Iyaa Beji." Kai Iyaa Debisi ta girgiza tace.
"Angode. Iyabo kuma kina jin daWin rayuwarki a wannan rugar? Naji labarin mijinki ya tafi cirani ya samu waiwayar gidane." Kai na sauke ?asa a sanyaye nace.
Iyaa inaji babu abinda yake damuna. Shi kuma bai dawo ba tukunna bai ko yi aike ba ma"
"Hmm ba sai su shekara biyar ba ma basu waiwayi gida ba. Wasu ma sun fito sunji daWin birni basa sake waiwayar rugarsu shinfiWa sabuwar rayuwa suke yi. Uwani tasan kinzo kuwa?"
E ta sani tama haihu jiya ta samu Wiyarta mace. Gashi aurenta da Hafizu ma ya mutu"
"Ahhh Ahhhh"
Ta shiga jerawa tana dukan cinyarta.
"Ai Shikenan ta huta ya huta. Ba'a matsa ma kai. Yayanki Debisi ma sun rabu da Yemisi fa. Yanzu haka yana neman wata yarinya a bayan layinnan. Kinsan gidansu Bola?" Ta tambayeni.
E nasan gidansu Bola"
"To yarinyar a gidan take Auwa. Yarinya mai hankali tazo ta gaisheni ma Debisin ya kawota"
Allah sarki. To Allah yasa hakan shine mafi Alkhairi "
Tayi carab tace.
"Shine ma alkhairin. Ke kinsan rikicin da akayine? Ai ni da Uwar Yemisi har abada. Yemisi fa kusan kashe Debisi tayi da duka. Duk ta farfashe mishi fuskarshi. Har Winki akayi mishi a gefen idanunshi. Watanshi guda a asibiti Yayanku Kokodeen na jinyarshi"
Ta dinga bani labaran abubbuwan da suka faffaru, harda rashe_rashe da ?aruwa da aka samu. Mun jima sosai kafin mu kai bacci, zuchiyata sai naji tayi sanyi sosai.
Washe gari duk nabi ma?ota da ?an uwa duk aka gaggaisa. Sai wajajen azahar muka wuce gidan Uwani ni da Iyaa Debisi ta yi mata barka da jajen mutuwar aurenta ta tafi ta barni akan in anyi suna zan dawo"
Mun sha suna lami lafiya. Kuma Hafizu yayi bajinta sosai, ya yanka tunkiya ?atuwar gaske, ga kayan fitar suna kala ukku na mai jego, kala ukku na jaririyar yarinya taci sunan mahaifiyarshi. Taron suna ya watse lafiya, saina soma haramar tafiya, na shiga kasuwa na Wan yi sare_sarena dai amman ban zura jikina ba dai KuWin hayane da Uwani ta ajjiyemun a wajenta da su naketa siye_siyena. Na sai su maggi, da kayan abincina harda taliyar murji Iyaa Debisi tayi mun, iyaa Kokodeen kuma ta haWamun su elbo, da garin Amala, ga garin eba. Tsaraba dai rigijib. Uwani ma ta tsinta mun kayayyakin yara tace in siyar in jaraba ko zasu karSu, in sun karSu shikenan sai inci gaba da kasuwanci na. Sai da na yi sati biyu cur na tattare inawa inawa Burodami Debisi ya rakani tasha na tafi, ya bani kuWi masu yawa, dan har nama ya kawomun mai yawa na soya nayi miyar tumaturi cikin ?aramar robar fenti. Yanzu ya riga daya saduda yayi ha?uri har yarinyar da zai aura saida ya kawota da daddare ta gaisheni.
Da yamma sakaliya sai gani na duro. Nayi lalle, da kitso, ga sabon lace da uwani ta Winkamun shi na sako.
Matan gidan suna tsakar gidan anata hada_hadar girki sai ga ni na shigo da sallamata.
BaWWo da Safiya ne suka tawo a guje suna yi mun oyoyo. Yaran ma?ota na biye dani da kaya ni?i_ni?i. BaWWo ta tsaya saukesu, ni kuma na shige Wakin Yafendo. A cikin Wakin na tarar da Daso, da Yafendona Maman Dason kenan, da kuma Dada.
"Ah Jabu kece da yamma lis haka. Lale da zuwa"
Cewar Yafendo. Da fara,ata na shiga na nemi waje na zauna a gefen Daso. Sai kallona take yi, taga na sake yin kyau fiye da lokacin sunan Cubu da ta ganni, na kuma ?iba. Damuwa to Waya ce a yanzu a raina rashin dawowar Yaya Hamma.
Yaran na sunto a bayana idanunsu biyu na mi?a ma Yafendona Waya, na mi?a ma Yafendo Waya. Na gaishesu da ladabi. Daso ta harareni naga har yatsa sai da ta ciza. Ni dai na kada baki na gaisheta ta amsa a da?ile dai. Ni ko ko a jikina.
"Kin samu su Toyosi lafiya, ya kika baro uwani?"
"Lafiya lau Dada. Iyaa tace a gaisheku, su Iyaa Beji duk suna gaisheku. Uwani kuma ta samu Wiyarta mace Fatima"
"Allah ya yara, ina amsawa"
Taja bakinta ta tsuke. Yafendo tace.
"Hama ma ta haihu yau kwana shida kenan gobe suna. Abinda ake tattaunawa kenan ma kika shigo kika sakemu. Sai ki shirya goben aje sunan dake in Allah ya kaimu. Amman sai dai kuyi fitar sassafe ?auyen da Wan tafiya"
Allah ya raya. Me muka samu Daso?" Na tambayeta dan itace sa'ata. Su inna tambayesu kamar nayi rashin kunyane.
A taSe tace.
"Mace ta samu"
To Allah ya rayata da imani. Bari inje in Wan huta in rama sallolin da ake bina.
Gaga_gaga washegari muka tashi da kacaniyar shirin zuwa suna. Ni dai har ga Allah banso ayi tafiyar dani ba gudun wula?anci, ga dangin Hama duk zasu ganni ?ila aita zunWena.
Kaya masu kyau sababbi fil na sama ?an biyu. Nima na Wakko sabuwar atampata na saka na Wauko Wankunne da sar?ana na saka, na saka takalmi da jaga, zobe, awarwaro duk na saka na fito shar, dama kunsan nace muku nayi kitsona, na yi ?unshi. Sai suka sake haskani. Na goya Hassan, Safiya ta goyamun Usaini.
MRS BUKHARI B4B GIDAN ?AMSHI


ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba....

Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya...
ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji?

Rashin dandano ko ni'ima?
Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa?
Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya?
Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki
ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani
ramlex266: 07069722234 ko 08064421211


Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801
Hello Maamas..
Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadar???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?ai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa.
Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi=?? Muna da;
Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su.
Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata=?
?
Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci
08067145801


Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri=?O??#? samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata =؃??#? idan matsalarki rashin sabbin plates Akwai
1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k =؃? Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa =؃?

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login