Showing 60001 words to 63000 words out of 270738 words

Chapter 21 - NAMA YA DAHU ROMO DANYE COMPLETE TRUE NOVEL BY BADI'AT.doc

da farin ciki da haWin kan iyalinshi. Akan Wan wani dalilin da bai kai an kirashi dalili ba duk wannan abun yaketa faruwa, har waWanda aka auro a baya_baya suma suka shigo da nasu fitinar. Amman in sha Allah komai zai zo ?arshe a kwana a tashi" Sun jima sosai anata tattaunawa sai kusan sha Waya su kai sallama da Baba Fhatsima, su Auwala suka nufi shashensu, Yaya Tasi'u ma ya nufi nashi Sarayin.
A daren wannan rana Gwadabe ya kasa runtsawa, duk da tarin gajiyar wahalar aikin daya kwaso. Kwakwalwarshi sai hasko mishi hotunan ?an matan gidan kawai take yi. Da wannan tunani ya wayi safiya, suna kan shirin fita Hadiza ta kawo musu abincin karin kumallo. Kunu ne a jug, sai Wunamen tuwon Sula da lafiyayyar miyar kuSewa Wanya. Da idanu Gwadabe ya bita bayan ta gaishesu tana shirin ficewa.
"Hadiza" Auwala ya kirayi sunanta hakan yasa ta dawo cikin Wakin. Komanta da sanyi take yi, kuma yanayinta na nuna halamar kunya tsantsa.
"Ga kayanmu kala bibbiyu ki wanke mana, Gwadabe bata kuWin sabulu, ko kai ko Mammada" Gwadabe ne ya zaro sefa ya mi?a mata, tasa hannu ta amsa. Auwala kuma ya bata kayan nasu daya cusa a cikin wando Waya.
Kafin su dawo Hadiza ta wanke musu kayannan tas, harma ta yi musu kwalima ta haWa da zannuwan katifunsu du ta wanke. Dama su kan yi ma yayyen nasu hakan lokaci zuwa lokaci. Wanki dama suke yi musu kasancewar su basu da lokacin kansu.
Yau samarin gidan a mugun gajiye suka shigo sharkab_sharkab da zufa, hakanne ma yasa basu shigarma Baba Fhatsima Waki a haka ba suka nufi shashensu. Anan suka tarar da sabitu yana kutuntumama Hadiza zagi tare da faWin kalma marar daWi a kanta.
"?ar iska dama naji labarin ?azamin kishine irinna gado yasa aka sakoki ai. Dama yaushe zaku iya zaman aure, yara an sangartaku, an Waure muku ?ugu, an Wauraku akan bigiren kishi" Karab a kunnen su Gwadabe. Sabitu na ganinsu yazo da sauri zai wuce, Auwala yayi zafin naman riko hannunshi ya fincikoshi ya dawo gabanshi.
"Ai ba ka zazzageta ka tafi a kyauta ba. Dan Allah sai munje gaban Malam yaji duk abinda ya haWaku har ka zaSi cin zarafin mahaifiyarmu da shi kanshi Malam Win. Kai dai Sabitu baka ?aunar buWe idanu ka ga muna rayuwa kyakkyawa. Wannan ciwon hassadar ne ya hanaka ci gaba sam, kuma gashi munfi ?arfinka nesa ba kusa ba. Hadiza wuce muje gaban Malam. Da ?arfin damtse Auwala ya figi Sabitu suka ratso tsakar gidan iyayen nasu, duk suna baje a tsakar gida suna shan iska. Baba Asshi taga Auwala ri?e cab da Sabitu, ba shiri ta cire hannunta a cikin abincin da take ci ta bi bayansu har da gudunta, daga ita sai fallen zani babu ko Wan dires a jikinta. Baba Fhatsima ganin harda Hadiza aka fita yasa itama ta mi?e ta rufa musu baya."


Anan na kawo ?arshen free page.
Wasa farin girki, labarin yana da tsawo ainun, dan ba mui komai ba. Sannan akwai tarin rikita_rikita da abubbuwa da dama na darasi, kar ki yi sake ayi wannan tafiyar babu ke.
Akwai tarin abubbuwa da zasu biyo baya.
Sannan akwai kyautuka da zan rabama masu yin dogon sharhi na musamman.
Ki biya kuWinki kisha karatu.
Wasu suna ro?on in buWe VIP
To 1000 ne VIP Win normal group 500 ne. Nagode sosai da soyayya

Nagode nice taku a kullum Mrs Bukhari. Mu haWu a paid group dan jin yanda zata kasance.


+22785548912

?an Nijar ga number da zaku turama da kati nan nera 500 a kuWinmu na najeriya.
Nagode

3064127935
Buhari Ibrahim Ladan
First bank

Sanya nera 500 Winki kuWin karatu anan. Wannan asusun gudauniyarmu kenan.
Ki sani in kika siya wannan littafin tamkar kin taimaki iyayen marayune, dama su kansu marayun
Kuzo mu yi tarayya cikin aikin lada. ?ar?ashin Amila Foundation gidauniyar da muka buWe ni da megidana domun iyayen marayu, ko tainakon marasa lafiya.

WaWanda suke cikin group dina mai suna (NAMA YA DAHU ROMO ?ANYE)
300 kacal zasu iya kuWin karatu


*?ar uwa ina fatan baki mance da kayan ?amshin Mrs Bukhari gidan ?amshi ba ko? ?ar na gata ba take haye ba, Kanuri gidan ?amshi. Matso kusa ?ar uwa ina da turarukan wuta nau'i daban_daban. Turaren kaya da zaki turare gidanki ?amshi ya ri?e miki surura, sannan inada kabbasiyya turaren ruwane da ake fesama sutura a yayin da ake turara kaya a kabbasa, kana inada turaren wadrop da ake sa?awa a tsakankanin kaya.
Turarukan wutana kuwa in kika turara gidanki yana sati guda yana ?amshi. Inada turaren turara jiki gangariya wanda yake kama fata.
Akwai kulaccam ta matan aure mai sirrin rikita maigida, ga gyaran fata. Akwai kuma kulaccam ta gashi, haWe da turaren fesawa a gashi.
Mai gayya mai aiki humrata ta matan Aure mai sirrin ?ara dankon soyayya, kiga oga na shinshinarki kamar mage taji ?amshin kifi Wanye.
Inada humrori kala_kala.
Ina da room freshener, da mopping mix mai sirrin ?amshi.
Kar in ta lissafo muku duk wani nau'in ?amshin da kikeso in kika samu Mrs Bukhari ?ar mutan Maiduguri kin samu ?amshi.
( Albishirinku akwai package na musamman dana tanadarma masoya wannan littafi nawa. Package ne mai Wauke da abubuwa huWu manya kuma a kan kuWi ?alilan karki bari garaSasarnan ta wuceki zaki ciji yatsa kwasha_kwasha nayi da kayana domunku)*
NAMA YA DAHU...
ROMO ?ANYE
LITTAFI NA BIYU
1




*Ina kuke mata ?an ?walisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haWaWWun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.*
*Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu*


Iyabo
Motarmu na dira a tsaha idanuna su kai tozali da kyakkyawar fuskar Yaya Hamma. Yana jingine a jikin wata Bus ya ?urama motarmu idanu bai ?ibtaba, bai kawar da kanshi daidai da na sakan guda ba, har sai da yaga na fito a cikin motar. Da sauri ya nufoni fuskarshi Wauke da yalwataccen murmushi, murnarshi ta kasa Suya. Yasa hannu ya karSi ledar kayana.
"Jabu tunda na shigo tasharnan zuchiyata bata dena dokawa ba har sai da na ga sakkowarki a cikin motarnan. Wata zuchiyarma ce mun take yi baza ki dawo garemu ba kwata_kwata" ?an murmusawa nayi kawai nace.
Yaya Hamma kenan, na gode da kulawa, amman kafin ma in tafi na sanar maka zan dawo." A jere muka fito daga cikin tashar, a bakin titi muka samu motar Girai muka shiga, wata kwaraSaSSiyar Bus mara gudu muka samu. Bayan tafiyarmu ta Wan yi nisa sai nace dashi.
Ni ko ya jikin Dada Yaya Hamma?"
Wannan tambaya tawa farad Waya saita sauya fuskarshi, daga farin ciki izuwa Waurewar fuska, harma da alhini. Lamarin daya dagula jinin jikina kenan, ruWewar da nayi da yawa ne yasa yace dani.
"Ki kwantar da hankalinki Jabu. Bawa baya iya tsara ma kanshi yadda zai rayu. Nayi imani da hakan na faruwa Al'umma babu mai zubar da hawaye. Bayan tafiyarki abubbuwa manya sun faffaru marasa daWin labari. Amman bazan baki labarin komai a cikin motar haya ba. Kiyi ha?uri in mun je gida zaki ji komai"
Bai daina rarrashina ba har muka iso Girai. Ni dai ko da muka shiga akori kura bana iya ko magana sai fargaba da nake cikinta. Jikina sai bani yake yi Dada ta haWiyi zuchiya ta mutu ne ?ila bayan tafiyata, ko kuma ma?etacin mijinta ya kasheta. Da waWannan tunane_tunanen muka shiga cikin JaSSi lamba. Sai gamuwa da mata masu tallar nono muke yi
Yaya Hamma gidan su Dada zaka kaini, zan tsaya a ?ofar gida sai kai ka shiga" ?uramun idanu yayi, sai naji idanun nashi sun yi mun kaifi ba shiri nayi ?asa da nawa idon, tare da sauraren amsar da zai bani.
"Dada bata gidanta, tana gidan Baffa Musa, ki bini kawai in kai ki"
Ai jin haka yasa na kuma tsurewa har hawaye sai da ya zubo a idona. Tafiya muke babu mai cewa da Wan uwansa ci kanka har muka isa gidan Baffa Musa, tafiyar ?afa ce mai mugun nisan gaske. A ?ofar shiga gidan naci karo da Burodami Debisi shi da Jatau. Sai nayi turus ina dubanshi cike da maWaukakin mamaki. Shi kuma cikin sanyi yake kallona irin kallon da naso in samu irinshi daga gareshi a shekarun da suka shuWe, shekarun da wutar sonshi ta kusan ?one mun rayuwata. Sai a yanzu da bana bu?atar kowa a cikin rayuwata ne, zai dinga jifana da irin wannan kallon? Ko zan iya ba maza wata damar, babu Burodami Debisi a cikinsu, zaifi mutumci ya ri?e matsayinshi na wa gareni
"Iyabu Ekabo ( Sannu da Zuwa)
Burodami Debisi yaushe a gari?" Na tambayeshi da yaren hausa, babu yabo babu fallasa a fuskata. Jatau yace.
"Ai tun ranar da kika yi tafiya shima ranar yazo. Tare muke ta zuwa kiwon shanu" Da mamaki na dubeshi, kuma na yaba ?o?arinshi daya iya har kwana biyu a ?auyenmu.
"Mu je ciki Jabu, ki ga halin da Dada take ciki, naga kamar kin sha'afa" Cewar Yaya Hamma da muryarshi a kausashe har Wan rawa take. Wucewa nayi cikin gidan, Yaya Hamma na biye dani a baya, su Burodami Debisi na biye dashi har zuwa cikin bukkar Goggo matar Baffa Musa.
A kwance na tarar da Dada kanta naWe da bandeji, sai kuma hannun damanta dana ga an ?ulle da tsumma, ga kara an jera mata kamar mai karaya. Sai numfarfashi take fitarwa, BoWWo na gefenta a zaune, su Yusufu, da Cubu duk suna kewaye da'ita, harda yaran Baffa Musa waWanda suke gidan miji, Yafendonmu Jabu, da Yafendo kaSoji mahaifiyar su Yaya Hamma, da Yafendo A'i suna wajen duka.
Kuka kawai na fashe dashi domin na rasa ma abinda zance, bansan wa zan tambaya ya bani amsa ba, kowa a cikin damuwa yake. BoWWo ce ta dawo kusa daf dani ta ri?e hannayena biyu.
Meke faruwa da Dada BoWWo, naga hannunta kamar karayace ma?" Baffa Musa ne yace.
"Abinda ya faru kusan sanadiyyarki ne Jabu. Wannan ?iyayyar da mijin Daso yake yi miki abune daWaWWe sosai. Kuskuren da ita Daso tayi shine data yarda da sharaWinshi kafin ya aureta. A lokacin da mahaifinmu Allah ya ji?an rai ya matsa ma da Daso kan a cikin gwarazan samarin da suke neman aurenta za'a saka shaWi, a lokacin shaWi gwarazan mazan fulani suke yi su auri mace, dole sai namiji ya nuna jarumtarshi. Aka saka ranar shaWi, Allah cikin ikonshi sai mai nagge yai nasarar cinye wannan gasa ta neman auren Daso. Gashi matashi mai dukiya, dan Allah ya albarkaceshi da tarin shanu a lokacin. Amman mutumne shi mai zuchiya da kafiya akan ra'ayinshi ko mai muninshi. Duk da wannan kusan Wabi'ace dake gudana a jinin ko wanne bafulatani, amman na mai nagge yayi yawa. Bayan anyi aure kafin ta tare sai yake sanar mata shi mutumne mai tsananin kishi shi baya son ya saka Wiyarta ?ar margayi a idanunshi sam, ta yi mai al?awarin zata kiyaye mishi hakan, amman bazai hanata zuwa ganinki ba, bai kuma yarda yaranshi suyi zumunci dake ba. Ita kuma Daso cikin rashin sanin girman furucinshi sai ta amince mishi da duk abinda ya gindaya. Duk da dai ba'a musu dashi.
Jabu daga ranar da yar mahaifnki Toyosi ta Wakkoki ta kawoki garinnan dan kiga dangin mahaifiyarki, bayan tafiyarku sai da igiyar auren Daso ya kutsure, ta fuskanci tashin hankali, da faWa sosai harda duka ma a wajen mai Nagge kafin ya korota gida.
To shekaran jiya kinje mishi gida, a gabanku ke da Daso ya fashe mata kai. Bayan ya rakaku da gudu sai ya rufeta da duka. Ana cikin wannan hali ranar ko tallar Nono ta kasa zuwa. Sai ga Debisi shima da yamma lis. Zuwanshi ne yai silar da kika ga Daso a kwance tana jinya. Hamma gashi shi yaita kai kawo akan nema mata lafiyarta. Debisi kuma da Jatau suka kaita asibitin Girai aka duba lafiyarta. Wai hawan jinine ma da'ita a yanda su suka ce. Kinji abunda ya faru, amman kuyi hakuri wata rana fa sai labari, masu ba da labarin ma wata rana basu. Haka zamu shuWe kamar yadda magabatanmu suka shuWe.
Kuka mai taSa zuchiya na fashe dashi kawai. Wannan zalunci da mai yayi kama, yama za'ayo a raba uwa da Wiyarta Wiyar ma ta fari marainiya bugu da ?ari.
Tsit Wakinnan yayi bakwa jin komai sai sautin kukanmu ni da ?annena da suka kewayeni suna rarrashina.
"Jabu ki dena wannan kukan. Ki yafe mini kinji? Yarintace tasa bansan girman sharaWin da mai nagge ya gindayamun ba, ba dan bana sonki bane na amince mishi ba. A cikin yarana kab nafi jinki fiye da kowa, kasancewarki marainiyar yarinyar da bata taso a gaban mahaifanta ba. Bugu da ?ari soyayyar Toye kanki ta koma kacokam."
Hannunta nayi carab na kama, idanu ta lumshe wasu hawayen nadama suka gangaro mata. Mayafina nasa na goge mata. Baffa Musa ne yace.
"Daso baki da lafiya bai kamata ki yawaita magana ba. Hutu kike bu?ata. Na faWa ma Jabu wannan labarinne domun tasan abinda ke gudana, ba dan in tashi hankalinki ba. Kai kuma Debisi duk sanda zaka zo wajen Jabu, ka sameta a gidan Yafendonta, ka sanarma Toyosi itama. Jabu ku tashi ku koma can gidan Yafendonku, ki samu ki huta"
Ba haka naso ba, so nayi su barni in yi ma Dada jinya. Amman Baffa Musa ya?i fur sai cewa yayi ma dinga zuwa dubata, matanshi zasu kula da'ita.
Muna tafe a hanya amman tunani ya cika kaina, damuwa tayi ma zuchiyata yawa, ina neman wanda zan kwanta a kafaWarshi in ci kuka ko zan samu salama. Gwadabe ne ya faWo mun, tunashi kawai da nayi wallahi sai na tsinci kaina ina murmushi kawai.
Tare duka muka shiga gida. Ni da su Daso wacce tunda na dawo naga ta fita sha'anina. bukkarmu muka shiga, na nemi waje na zauna jigum. Yaya Hamma ne ya shigo hannunshi ri?e da kayana. Yana shigowa sai naji Daso ta sau siririn tsakin da ba kowa ne zai ji ba.
"Ga kayanki Jabu. Ku kuma ku bamu waje zan yi Magana da Jabu" Su Cubu duk suka mi?e suka fita, banda Daso wacce kwanciya take shirin yi. Sai da ya yareta kuma da faWa naga yana magana. Kuka kawai naga Daso ta fashe dashi ta fice fuu.
Ni dai ba ta fishin Daso ma nake ba, ta kaina nake yi. Zama yayi a ?asa yana fuskantata. Idanu ya zubamun ya?i cewa dani komai, ya?i kuma ya dena kallona. Ni kuma duk sai na tsargu. Jatau ne ya le?o.
"Jabu ki zo Debisi yana son zaku yi Magana, yana gindin bishiya, ki je da tabarma, ga fura Hari ta dama sai ki tafi mishi dashi"
To" kawai na iya cewa, ya saki asabarin yayi tafiyarshi. Yaya Hamma kuma naga yayi ?asa da kanshi kawai yana wasa da layar dake Waure a tsintsiyar hannunshi"
Yaya Hamma bari in je in dawo, tunda naga kamar baka son yin maganar da kace zamu yi" ?agowar da zaiyi sai naga idanunshi sun rine, jijiyoyin fuskarshi sun yi burWun_burWun. Gabana ya yanke ya faWi ganin yanda cikin ?an?anin lokaci na ganshi a cikin wani irin yanayi. Cikin kaurin murya mai cike da karaya yace.
"Shikenan gobe zan dawo, nima zanje gida in kwanta jiri nake ji" Haka kurum sai banji daWin ganin shi a sabon kamanni ba. Kafin in gama tubkewa ya fice bankai ga warwarewa ba. Jikina a mace na fito tsakar gidan. Tabarma da damammiya fura Hari ta mi?o mun nasa hannu na karSa. Har na kai ?ofar fita na juyo na kalli BoWWo nace.
BoWWo ku jirani in je in dawo. Inaso zamu je gidanki akwai muhimmiyar maganar da nake son mu tauna" Ina faWan haka sai naga Daso ta zare idanunta, firgici ya bayyana karara a fuskarta"
Ficewa nayi waje. A tsaye a gindin bishiya na hango Debisi yana kallon garken shanun da suke wucewa. Kurama juna idanu muka yi, ina daga tsallake ina jiran shanun su gama wucewa"
Zuchiyata ce naji tana bugawa da ?arfi, idanun Debisi naji sunyi mun kaifi. Na so Debisi so na ha?i?a, soyayyarshi ta wahalar da rayuwata, dan zuchiyata bata iya son abu ba, in zata so abu da gaske take sonshi, haka kuma ban iya ?in mutum ba" Bamu dena kallon ?udan da muke ma juna ba har sai da garken shanunnan suka gama wucewa. A hankali na isa ?ar?ashin bishiyar. Carab ya amshe ?waryar damammiyar furar dake hannuna. Na shimfiWa tabarmar dana fito da'ita, tare da cewa.
Bismillahi Buradomi ka zauna"
Murmushi yayi mun, irin wanda ada nake mafarkin ganin yanai mun. Banda a yanzu dan tu?u?i naji zuchiyata nayi mun. Kuma ina fatan ba cewa zaiyi sona yake yi ba, dan zan iya zaginshi tsab, laifinshi mai girmane a gareni, babu abinda zai iya faWamun in yarda ba yaudara bace"
Waje na samu na zauna kamar yadda yai mun izini.
Shiru ne ya biyo baya na tsawon minti shida kafin yace
"Bansan ta inda zan soma ba Iyabo. Gashi zuwan nawa ya haifar da matsala mai girma, ina mai neman gafararku baki Waya. Amman kafinnan me kika je yi a Kano, sannan wannan ramar duk ta rabuwa da Gwadaben ce, ko kuna cikin wata damuwane?" A jijjere yayi mun tambayoyin da na yi jim, ina cinka cinkar wanda zan sona amsawa a cikin zuchiyata. Sai na sake jin amon muryarshi yana cewa
"Da zan baki shawara, da nace ki shirya ki bini mu koma Kano. Tunda kika baro Kano kika barmu cikin kewa da alhinin rashinki. Nawa kuwa yafi na kowa. Kuma a kwana biyu kacal da nayi a rugarnan na tabbatarma kaina rayuwarki ba zata taSa yi miki daWi ba. Ke da kika taso a maraya, ga hasken lantarki, ga ruwan famfo, ga makarantu, ga titina, ga_ga_ga. Amman anan fa babu abunda suka sani sai kiwo da tallar nono, ace kamar Dada tallar Nono itama take zuwa yi, su ?odWo ma tallar suke Wauka fa" katseshi nayi ta hanyar cewa.
Tambayarka ta farko gareni shine. Naje Kano ne nayi fasfo zan tafi ?asa mai tsarki da izinin Allah neman kuWi. Tambaya ta biyu kuma. Ciwo nayi mai tsayi shi yasa na rame. Gwadabe kuma yana Wamfare a raina tsaiwar numfashinane kaWai ka iya kawo ?arshen soyayyar Gwadabe.
Batun

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login