Showing 207001 words to 210000 words out of 270738 words

Chapter 70 - NAMA YA DAHU ROMO DANYE COMPLETE TRUE NOVEL BY BADI'AT.doc

yaran fulani. Da wata riga mai ruwan hoda, bulu, yallo. Nasan kun ganeta duk uwar da tayi renon Wa shekaru ashirin baya ta san wannan riga da wannan wandon.
"Jabu ga namu kayannan babu yawa ayi ha?uri, yanayin garinne kinga anyi annobar Dabbobi an samu karayar arziki sosai"
Murmushi nayi . A raina ina tuno haihuwa biyu da nayi a gidan Gwadabe, a leda ake kawomun kayan dangin miji shima a wula?ance.
Nagode sosai Yafendo mai yawan kenan ai. Dama yanzu nake son in gama a fitar da kayan da su Bose suka tawo dasu ma.
"Ki barshi in Adda Daso ta kawo na wajenta sai a saka a bawo biyu a fito dashi a shimfiWa tabarma haka muke yi. Tubarkalla kunyi kyau ke da yaran. Naga yayyensu ma suna tsakar gida duk anci kwalliya"
Murmusawa kawai nayi ta saki labule ta koma Sarayinta.
Ina gyara Waurin Wankwalina saiga Kari da Cubu da kaya ni?i_ni?i a buhu sun shigo dashi, daga Sarayin Yafendona suke saida aka kai mata sannan tace a kawo mini. Uwani ce ta shigo.
"Iyabo wannan man kamar bazai isa ai suyan kayan cikinnan ba gaskiya. Ahh cancaWi kaga Amarya a gidan Hamma. Kai inama angon ?arnin yananan zanso ganinshi a wannan rana"
Dariya nayi dan ta sosa mun inda yake yi mini ?ai?ayi. Tun a daren jiya nake kewar rashin mijina a tare dani a lokacin da nafi bu?atarshi.
To kafinnan Uwani zo kiga abubuwan arziki da aketa samu. Sannan a sakasu a bawo a fitar tsakar gida kamar yadda suke yi a al'adance"
Nan Uwani sukaita jejjera kaya, ta Sangaren Dada ma masha Allah ?an biyu sun samu kaya sosai. Bawo uku aka fitar sha?e da kaya. Nan ma?wabta akaita tururuwar zuwa ganin kaya. Da bakinsu suke labarin tunda ake haihuwa a rugar babu mai jegon data kaini goshi. Hama kuwa kamar zata haWiye zuchiya ta mutu ta huta da ba?in ciki.
Jallof Win shikaface sai zoSo da Amala da miyar ewedu da miyar tumatur da taji ganda. Dan tafi da gidanka su Iyaa Beji suka yi na bushasshiyar ganda, tun jiya da dadare aka ji?ata cikin bokiti da ruwan zafi.
Ma?wabta akaita bi da abincin suna, gidan sunan cike da yara da manya, kowa ka gani abinci da lemun kwalba yake ci.
Ina cikin matan abokan Yaya Hamma suna bani tasu gudunmawar, mai atampa, mai omo, mai kayan yara, masu mi?o kuWi nayi sai ga Hama ta shigo babu ko sallama. Ganin na canja kaya nasa atampa me kyau dinkin ya zauna sosai a jikina saita sake Sata ranta.
"Danginane abincin da aka bani bai ishesu ba. Ga kula a zubo musu. Mutum biyu basu samu lemun kwalba ba sai zoSo"
Kular hannunta na karSa na mi?a ma Uwani dake zuzzubama jama'a abinci. Babu musu ta cika mata kular tab da jalob ta Waura mata kayan ciki.
"Gashi lemun kwalba ne ba zasu iya samu ba. Kinga waWannan lemun kwalbar da masu shi, suyi ha?uri da zoSon da suka samu ma" Cewar Uwani kenan.
Hama dai ganin idanun abokan Hamma sai tace.
"Ai babu komai Uwani. Hakanma mun gode"
Ta karSi kularta ta fita Waya daga cikin matan abokan Yaya Hamma sai kurantata take yi tana cewa tayi kyau wannan kwalliya haka.
Haka dai wannan suna ya gabata sai yamma lis kowa ya watse, akabar ?an gida da wanke_wanke. Tare duk aka haWu akayi wanke_wanken ragowar abinci daya rage kuma matan gida duk suka Webe ko wacce tana faWin ta huta da Waura tuwon dare.
Sai bayan isha su Uwani suka kammala aikinsu tsab. Uwani ta shigo da ban?ararrun ragunan da aka rataye a tsakar gida.
WaWannan ragunan fa Uwani"
"So kike a bari a waje a sace? Uwargidanki tun magriba take sunturi a lungunnan kuma duk wucewa sai ta kalli ragunan taja ?wafa na jima ina lura da'ita. Yanayinta kaWai ya nuna ba mutuniyar arziki bace. Cewar Anty Mulka.
Dariya nayi nace.
Yanzu saita Wauki rago to ta kaishi ina?
Uwar harara Uwani ta doka mun, nayi mata dariya kawai.
Washe gari duku_duku su Iyaa Beji suka tashi da suyar rago. Su BaWWo kuma sunata kiciniyar haWa musu karim kumallo.
Yafendona ce ta juyo ruwan wankan yara, nima ta kai mun nawa.
"Maza Jabu je kiyi wankan kar ruwan ya huce"
Mayafi na Wauka na fito. A ?ofar bukkata na tarda Taiwo da Kahinde suna zaune suna kuka.
Kallonsu nayi tausayinsu ya kamani, tsugunnawa nayi a kusa dasu. Na shiga rarrashinsu na samu su kai shiru nace su shiga Waki su kwanta a kan gado. Ai kuwa babu musu suka tashi suka shige.
Murmusawa nayi nabi bayansu da idanu. Hawaye suka taru a idanuna.
Wallahi barin yara a wani gidan babu daWi. Kuma duk yadda mace takai sai yarannan sun mance da'ita kuma zasu kasance babu wannan sha?uwar ta ?a?a ga mahaifiyarsu. A hakama Gwadabe yayi namijin ?o?ari sosai da har ya aiko a kawo mun yaran.
Da ?yar naja ?afata na shiga wankan, ban jima ba na fito, na samu Yafendona tana yima ?an biyu rawa sunsha fararen ovaroll sunyi kyau yara kamar yaran Turawa. Kan gadona na kalla Taiwo da Kahinde sunyi baccinsu sai ajjiyar zuchiya suke saukewa.
Haka aka soya namannan guda Waya surutum Yafendo tace a ciremun Wayan ragon suka kasa kashi huWu. ?aya nasu Yafendo da mutan gidan. Waya na Dada da ?annena. ?aya na ma?ota, sai Wayan na dangin Babana. Yafendo tace in dibarma Hama a nawa, an kuma bata kai da ?afan rago Waya, Wayan da safe shi aka dafe mun naci.
A leda na ?ulla mata na tura yara suka kai mata. Nayi tunanin ba zata karSama ma sai kuma ta karSa. Na ?arama su Iyaa Beji a nawa da Uwani.
Washegari su Iyaa Beji suka kama hanyar Kano. Uwani dama tace saita yi sati guda kafin ta koma.
Wata ranar alhamis muna zaune a tsakar gida ni ina wanki, Uwani na yi mun kwalimar Wakina saiga Hama ta fito da jaka ni?i_ni?i da yara wai gidansu zata koma ita acan zata haihu taci gaba da zama har sai Yaya Hamma ya dawo.
Kai kawai Yafendo ta girgiza tace.
"A sauka lafiya. Ni bazan hanaki zuwa gidaba tunda wanda kike zamanshi bayanan. Amman ki ajjiye yara a gidansu suci gaba da zama a cikin ?an uwansu.
Jabu ki karSi yaranki kici gaba ds da ri?esu har zuwa sanda zata dawo."
Bafa haka Hama taso ba. Cikin fishi ta ajjiye jakar yaran tayi ficewarta tana maganganu marasa daWi.
"Allah ya shirya. Jabu kici gaba da ha?uri nima kaina ha?urin nake yi da Hama. Tunda dai aka auroki gabaki Waya kafatanin halayenta suka sauya.
Babu komai Yafendo. Ku kuma kuzo mu shiga ciki ko?"
Na tattare yaran muka shiga cikin Wakina dasu.
Ana gobe Uwani zata tafi da daddare na tattaro mata kayana atampopi kusan kala goma cib nace duk ta Winka mun inna tawo sunanta sai in tawo dasu.
"Ki haWo da waWannan rigunan masu zubin ?an ?auye dukka sai in shiga kasuwa a yi canjin kasuwa in zaSa musu masu kyau, tunda naga kin samu dayawa"
Ai kuwa kin kawo shawara me kyau."
Tattaro mata nayi kusan duka kaWan na rage.
Washe gari sassafe ta yi mana sallama ta kama hanya, kafin dai ta tafi ta faWamun watannin daya rage haihuwarta sabida kintata zanyi in tawo tunda bamu da network.
Haka rayuwa taita tafiya su Taiwo sukaita bani wahala in wannan ya warke ciwo sai wannan ya kama, canjin ruwa da zaman ?auye duk saiya sa suka rame ga ?uraje caSa_caSa ya fito a jikinsu babu masaka tsinke.
Ranar da suka cika wata guda a ranar Bara'u ya tawo ya kwana a gidan Dada washe gari suka wuce. Na haWama yaran goma sha tara na arziki. Taiwo Atampa biyu na bata. Na kulle atampa biyu daban na matan Gwadabe. Toye da Kahinde nasa Uwani ta sai musu kaya kala bibbiyu ?an kanti duk da dai irin na ?an ?auyene amman dai na siya musu. Na siya ms Iyabo kaya itama.
Dada ta haWa musu tsarabar ?auye, hakama Yafendo, da su BaWWo. Aka dai haWa musu tsaraba rigijib harda zabi huWu aka haWasu dashi wai suyi kiwo.
KuWi masu yawa Bara'u ya mi?o mun da kaya cikin babbar ?atuwar leda yace wai inji Gwadabe yace a bani kuma yanayi mun barka.
Allah sarki Gwadabe. Dan Allah Bara'u kace nagode Allah ya saka mishi da Alkhairi "
"Babu komai ai tsuntsun soyayya. Naso mu tawo da Sakina ma amman tayi nauyine sosai haihuwa ko yau ko gobe. Amman wata rana kwatsam zaki gammu."
Allah sarki Sakina Allah ya raba lafiya. Nima indai na shigo kano nanda wata Waya in sha Allah zan shigo Takai Win da izinin Allah."
Da haka mu kai sallama ya tusa yaran a gaba suka tafi. Mu kuma rayuwa taci gaba da garawa damu. Shayarwa tasa nayi kyau na ciccika sosai. Hankalina ya kwanta sosai a tafiyar Hama gida har ga Allah ni dai saida nayi fatan inama karta dawo.
Gabaki Waya gidan da matan gidan duk sun sake. ?an biyu kuwa suna ganin gata a wajen Yafendo da ?annen Yaya Hamma.
Haka dai naci gaba da shayar dasu cikin tsabta da lafiya. Abun mamki nayi ?iba sosai baku ganni ba, sabida ?an biyu suna da tsotso sai nima cin abincina ya ninka, dani dasu duk mukai Sul_Sul damu."
Yau tun safe na tashi da shirin zuwa dubo Dada. Da wuri naima yara wanka nayi mana wankin kayanmu na shanya, na goya ?an biyu na fito.
?arayin Yafendo na nufa nai mata sallama inaso in je dubo Dada daga can zan le?a Cubu dan ance bata ji daWi ba."
"Sai kun dawo ?ila anjima nima in le?o gidan in duba Adda dan jiya ciwon kai ya sata a gaba" Ni banma sani ba sai yanzu da nake ji.
Ayya ai kuwa zan tafi mata da ?wayar bature ta haWiya. Sai mun dawo Yafendo"
Fitowa nayi duk inda na wuce sai na tsaya an gaisa sun ga ?an biyu kafin in wuce. Ga rana sosai a garin zafi akeyi sosai safiyace amman har rana tayi zafi. Sai naji idona wannan marar ganin ya soma ciwo har yana zubar da ruwa.
Da sallama na shiga gidan Dada ina haki abunka da masu kitse.
A tsakar gida na samu Dada a kwance Yusufu na mata fifita Kari kuma tunda ban ganta a tsakar gidanba nasan bata nan an tafi talla.
"Jabu kune da safe haka? Saifa da nace da BaWWo ba sai sun faWa miki ba shine saida ta faWa"
Zama nayi a kan tabarmar, na sunto ?an biyu da suketa kukan zafi. Yusufu ya karSi Waya Dada ta tashi zaune itama ta mi?o hannu in sa mata daya.
A_a Dada kiyi fama da kanki Usaini nauyine dashi ga tumbuWi"
Murmushi tayi tace.
"Kema lokacin da nake koyonki ai kin fishi girma da nauyi. Cika bayana dam kike yi. Duk inda na wuce sai an kalleni, har ciwon ?irji saida ya kamani a goyonki. Mi?o shi"
Murmusawa nayi. Ni dai Allah ya jarabceni da tausayin Dada. Sanyin muryarta kaWai ka iya cika idona da ruwan ?walla. Usaini na mi?a mata na tashi na Webo ruwa a randa na Salla mata fanadol biyu. Na bata ta sha ta kwanta.
Na samu Yusufu ya ri?e mun yaran nayi mata kwalima, na wanke mata tufafinta tas na share tsakar gidan.
Bani na bar gidan ba saida na yi mata miyar tumatur na aika Yusufu ya siyo mun nama da shinkafa. Sai wajajen biyun rana na nufi gidan Cubu.
Da sallamata na shiga cikin gidan abun mamaki kishiyoyinta da girmansu wasu da yaransu a gidan miji ma amman suka saka Cubu a gaba uwargidan ta zauna a ?aton cikinta sai ihu take yi. Ragowar kishiyoyin suna ran?washinta.
Subhanallaah me zan gani kasheta zaku yi ko me?"
A firgice suka juyo suka zuba mun idanu. Hawaye suka gangaro a kumatuna. Cubu numfashinta sai kokuwa suke yi ita dashi"
Mrs Bukhari

ramlex266: Ina mata da suka amsa sunan su ba Muna mata ba....

Ina macen da take so ta zamo tauraruwa a gidan mijinta,itace uwargida itace amarya...
ramlex266: Uwargida ko Amarya shin minene matsalar ki a wajen miji?

Rashin dandano ko ni'ima?
Bushewar farji qayau kamar busashen ciyawa?
Rashin samun gamsuwa a wajen maigida ko rashin sha'awar ce ga baki d'aya?
Budewar farji kamar kofar wambai ko qarni/wari ke damunki
ramlex266: Kina so ki zama tauraura kuma sarauniya a wajen oga a rasa gane sirrin naki? Ki zamo yar gaban goshi sai yanda kika ce wato kin mayar da oga mijin kafin ta ce? Ba boka ba malam gyaran shimfida kawai Hajiya to ki nemi hjy ramlex domin qarin bayani
ramlex266: 07069722234 ko 08064421211


Message Safmam Palace on WhatsApp. https://wa.me/2348067145801
Hello Maamas..
Shin ko kunsan AMASI'S TREAT from SAFMAMPALACE ta tanadar muku da ingantattun sinadarai na fito da martabar abinci da abin shaa? A AMASI'S TREAT Muna da spices and herbs irin su;Curry powder, Mixed Spices, special Jollof mix, fried rice, Mandi Spice, Garlic powder, Cinnamon, cloves, Tea blend, Yaji, Spiced daddawa.. Gasu nan dai dayawa.
Har ila Yau AMASI'S TREAT bata barku haka ba Seda ta tanadar muku da kayan maqulashe Don gusar da kwadayi=?? Muna da;
Kwakumeti, Ridi, daquwa, Cin Cin da sauran su.
Bafa anan muka tsaya ba Muna da bangaren qayatattun dinke dinke.. SAFMAM CLOTHING zasu fito muku da kyawun dake materials dinku ta hanyar tsantsara muku dinki musamman na yaranku mata=?
?
Muna nan a Zaria Muna aika Kaya ko'ina cikin aminci
08067145801


Assallamu alaikum mutanan kirki Ina Miko gaisuwa daftn alheri=?O??#? samun damar mallakar duk abunda kakyeeda bukata. Cikin sauki ta hanyi Yi muku adashin gata =؃??#? idan matsalarki rashin sabbin plates Akwai
1, zubi duk sati 2k sati 10 kwasar kayan 20k =؃? Akwai zubi duk sati 2k sati 20 kwasar kayan 40k har zuwa duk yanda mutum yakyee bukata zamu turo maka da kayanmu idan lokacin kwasarka yayi da yarda Allah kazabi duk abunda kakyee bukata da yarda Allah to mekakyee kikyee jira ki tintibene domin jin yarda raguwar tsarukan sukyee insha Allah idan Kuma kyee ma,aikaciyace to kyeemafa =؃? Akwai kayan Yara yankanti
Akwai takalman da jakunkuna da mayafai
Da sauran kayan amfani kyeedai maxa ki hanzarta kafin mu Fara zubi
Insha Allah zamu Fara zubi a farkon( sabon watan August ) Allah yadafa mana nagodee sossai zee Musa takuce =؃??p? ga number din da zaa iya damuna =؃??#?=???=??? 08029882667


*Ina kuke mata ?an ?walisa irin Shanono? Ku firfito ga Uom Taufiq veils bead work and Abaya stone work gliter veils lafaya. Ta zo muku da haWaWWun aikin beat na hannu domin kwalliyarku da fito daku ku yi tsab.*
*Aikinta babu ha'inci ni na tabbatar. Nima Badiat Ibrahim zan bata aikin lafayata ta zuba mun aikin beat work kuzo muje tare ta gwangwajemu*
07082649563 whats app number kira 07036028230
NAMA YA DAHU....
ROMO ?ANYE
BADI'AT IBRAHIM MRS BUKHARI B4B GIDAN ?AMSHI

19




GWADABE:.

Ya daWe yana shafa bayan Shafa amman ta kasa bama zuchiyarta ha?uri ta dangana. Zuchiyarta ta daWe tana ?unsan wannan takaicin na yadda yake kasa Soye soyayyar Hadiza a ko'inane ko kara baya yi mata. Sai dai ita tayi mishi kara ta tayashi son abinda yake so. Haka Hadiza ?iri da muzu ta?i amincewa asa ma Wiyarta sunan Iyabo. Amman ita tambaya Waya yayi mata ta amince mishi. Ko kusa bawai dan tana son sunan bane, tayi hakanne domin son abinda mijinta yake so. Duk kawaici na danginta saida saka sunan Iyabo ya taSa ransu, Tamu ne yayi kinini a cikin lamarin ya hanasu tayar da zancan.
"Kiyi ha?uri Shafa koma menene ya saki kukan na ro?eki kukanki yana dafani?
Da sauri ta Wago ta zuba idanunta a nashi a ?o?arinta nason ganin da gaske yake yi kukan nata na gasa ranshin kuma. Ja taga idanunshi sunyi harda mai?on hawaye. A hankali ta sauke kanta a sanyaye tana sauke ajjiyar zuchiya.
"Inason sanin damuwarki da abinda ya sakaki wannan kukan. Ko dai ganin Hadiza da kikayi a ma?ale danine ya zaburo miki da kishin ki uhm?"
Shiru tayi tana share hawaye. Niyyar tashi daga jikinshi tayi yayi wuf ya sake dawo da'ita jikinshi. Kyakkyawan ri?o yayi mata ya tallafo haSarta tare da yima bakinta ri?on alewar yara. Wata duniya suka shilla ta masoya Gwadabe da Shafa sunma mance a duniyar da suke jin daWin rayuwarsu kawai suke yi.
Labulen Wakin suka ji halamar kamar a Wage yake. Shafa ce ta yi saurin juyowa suka haWa idanu da Hadiza dake tsaye tana hucin kishi. Gwadabe na zaune ko gezau baiyi ba balle yayi yin?urin tashi.
"Lafiya zaki buWemun labulen uwar Wakina babu sallama balle neman izini, in da kinga abinda yafi haka kuma fa? Kinga hakan ai bai dace ba. Baban Abba tashi kuje Allah ya bamu alkhairi."
"Ni kike faWama wannan maganar, ashe ba har zuchiyarki kika sallamamun mijin ba? In ba haka ba daga zuwa yayi miki sallama zaku Sige da soyayya ba kunya babu tsoron Allah. To yayi zamanshi anan wajenki ki bashi abinda yake bu?ata. Namiji da kishiya duk amincinku watarana sai sun munafurceka"
Tana kaiwa nan ta saki labulen tayi ficewarta. Shafa ta dubi Gwadabe da taga yayi shiru baice komai ba, shi bai tashi ba, shi bai magantuba. Ha?i?a taji ciwon maganganun Hadiza, ko dai dama ba yau ta soma yi mata ire-irensu ba, dannewa kawai take yi da ?o?arin a zauna lafiya"
"Shafa kiyi ha?uri ki daWa zan kuma yima tubkar hanci danna fuskanci Hadiza zuma ce sai da wuta. Ni na Wauka lallami zai bi da'ita ashe ba haka bane. Jeki shinfiWe yara sai ki dawo"
"Kaifa ai ya kamata kaje ka rarrashi ?ar gwal Win taka da baka ?aunar ganin Sacin ranta." Shafa ta faWa cikin sigar kishi da muryar tausayi ainun. Kunya ta shigi Gwadabe dan tabbas yasan Shafa akwaita da kawaici da yakana.
"Ke dai jeki ki dawo, anan zan kwanta ke ba a gabanki tace in yi zamana ki


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login