Showing 6001 words to 9000 words out of 197828 words
Chapter 3 - IDAN BA KE 1 TO 2 COMPLETE By Na'ima Suleiman Sarauta Nimcey luve .txt
gamawa ta Ajjiye. Gari na fara haske bayan tai sallah ta kaɗa shannun zuwa cikin jeji. Har zuwa lokacin bata da nutsuwa ita a yanzu ba wasan majin ya dameta ba, illar rashin lafiyar Dada idan har macijin ya kasheta waye zaici gaba da kula da Dada? Zama tai a gefen wani dutse ta shiga rusa kuka da iya ƙarfinta.
Commissioners Quarter's
Haɗaɗɗiyyar unguwa ce wacce take cikin Jimeta, iya haɗuwa da tsari unguwar tayi, wanda bai saba fita kasashen waje ba idan ya shiga Commissioners Quarter's zaka ɗauka a ƙasar turawa kake. Gidajene duguwa zaka gansu kamar tangaran sbd yadda suka haɗu aka zuba dukiya. Unguwa ce ya masu kuɗi wanda talaka sam bai isa ya shige ta ba. Unguwannin masu ci da gindin biro kenan.
A hankali take sakkowa daga kan strains ɗin benan hannunta riƙe da waya tana latsawa, jikinta sanye da wani Short pencil jeans sai Balenciaga top a saman t.shirt ɗin jikinta. Ƙafarta cikin wani Hermes slippers. "Binta! Binta!!" Ta shiga kiran maid ɗin dake yi musu abinci tana zama saman Kujera, jinin Binta na rawa ta ƙaraso tana zubewa a gaban Zahrah ta ce "Hajiya gani" harara ta watsa mata cikin rashin ko ina kula ta ce "Kin san ban son buɗe murya sbd kawai zan kiraki?" Binta wacce a ƙalla zata iya yin shekaru 55 zasu iya kusan sa a da mahaifiyar Zahrah ta sunkuyar da kanta ƙasa cike da girmamawa ta ce "Afuwa Hajiya, ina can ina duba time table na list ɗin abincinki na me za a dafa miki zuwa dare" shiru Zahrah tai ba tare data ƙara cewa Binta komai ba, hankalinta yana kan wani abu da take searching akai, ita dai da karatun boko na yin magana a jikin mutum da tuni ya jima dayi a jikin Zahrah domin kaf gidan tafi kowa zurfi karatun boko shi ya sa take taka kowa hankali kwance. "Hajiya me kike buƙata?" Binta ta tambaya. Idanunta ta ɗaga ta kalli Binta a hankali taja tsaki ta ce "Nikam Binta na tambayeki?" "Ina jinki Hajiya" Zahrah ta gyara zama sosai tana ajjiye wayar hannunta a gefe kafin ta ce "Wai yaushe za kiyi hankali ki fahimci abin da nake buƙata, matsalar rashin ilimi kenan fa, gaba Binta ƙwaƙwalwarki bata riƙe abu ba lallai ko primary kin cika ba, wallahi na tsani harka da midille class,uneducated, villagers" da tsananin mamaki Binta ke kallon Zahrah ƴar cikinta ke faɗa mata wannan maganganun? "Kiyi haƙuri Hajiya" a fusace Zahrah ta ce "Sorry for yourself Binta, kije ki haɗa mini salad ki saka lemon sosai ciki" Binta ta jinjina kai tana Miƙewa tsaye tare da barin wajan idanunta cike da hawayen baƙin ciki. Wata mata wacce ta fito cikin parlourn ta kalli Zahrah ta ce "Why are you shouting?" Murmushi Zahrah tai ta ce "No Mimi ina game ne, akai mini game over" Zama Mimi tai ta ce "Ok, kwana biyu na jin labarin Deen a bakinki? Lafiya dai?" Zahrah ta ce "Baya nan ne Mimi" Mimi ta ce "Ai fa, naga idan yazo sai ku kai awa uku zuwa huɗu a part ɗinki kwana biyu shiru" Murmushi kawai Zahrah a haka Binta ta kawo mata haɗin salad ɗin. Mimi tabi Zahrah da kallo kafin ta ce "Wai lafiyarki ƙalou kuwa? Kullum cikin cin haɗin Salad kike?" "Lafiya Mimi, kawai zuwa makarantar nan ke sani gajiya da kwaɗayi naji bana son cin komai" Mimi ta jinjina kai ta ce "Lallai, ni banga me zaki da kuɗi ba da kuka zaɓi lecturing Zahrah" ba tare da data amsa ta ba ta ce "Mimi ina Daddy ne?" Mimi ta ɗauki waya ta ce "Jiya ya dawo, but yaje kano wajan wani babban abokinsa" "Ok" cewar Zahrah a nutse Mimi ta kalli Zahrah cikin damuwa sosai ta ce "Fatima-Zahrah yaushe kike tunanin yin aure ne, boko kin gama ta, completely sai abin da yai saura, familyna sun fara mini surutu akan wai na zuba miki idanu, wasu har cewa suke maybe yawonki kawai ki ke, ni dai nasan ba haka bane i trust you babyna" marairaicewa Zahrah tai kamar ƴar 20 nan kuwa shekaru 31 take da shi. "Mimi kin san familyn nan naki basu san darajar karatun boko ba, ta ya ya zan haɗa karatu da aure? Kana yin auren kuma ace ka haihu, kuma ba zan iya haɗa aikina da aure ba gsky Mimi a barni zuwa 35 na gama komai sai na fara tunanin auren, su kansu mazan ai mai ilimin boko suke buƙata ba kuwa ya damu da ilimin addinin nan ba, suna buƙatar mace wayayyiya a very educated women" murmushi Mimi tai cike da gamsuwa da maganar ƴarta kafin ta ce "Na fahimta, ko Dadynki sai dana kammala University mukai aure muna dai soyayyya a waje, dake kuma na wuri na shiga shcl shi ya sa na gama before we getting married" jinjina kai kawai Zahrah tai hankalinta akan salad ɗin da take ci sbd yadda cikin jikinta ya sanya mata kwaɗayi kala-kala. Da sauri Mimi ta ce "Subuhanallahi, maza kunna mini Plasma ɗin nan ki jonata da DS.TV tafsirin Sheikh sai shigeni" kwaɓe fuska tai kafin ta ce "Mimi wai kin damu da wani Sheikh, ni wallahi ban son tafsirin ɗin ko kaɗan, ga wata ƙinƙina da yake, da ƙyar fa yake iya karatun sbd ƙinƙina wani time ɗin har hawaye yake to me za'a gane?..." Da idanu Mimi tabi Zahrah tana mamakin jikar ƙirjinta a kullum "To ai kuwa da yadda, ƙinƙina kuma ai larura ce kuma a hakan Ubangiji ya ba shi bawai Zahrah".
Gudu take sosai hankali a tashe sai haki take ita kam sam ba zata iya irin wannan wasan na sai da rai ba, wacce ƙaddara ce take shirin bibiyarta ne? Tsayawa tai tana mai da numfashi, sai a lokacin idanunta ya sauka akan wasu fararen Kurciyo masu kyau da tsari ita a rayuwa tana son ko wacce kalar dabba ta daɗe tsaye tana kallonsu, ɗaya daga cikin kurciyoyin ya tsora mata idanu. Tunawa da tai ana gab da fara wasan macijn ya sanya ta ƙara saurayi domin samun wajan ɓoya. Girgiza kurciyoyin sukai wata iska da guguwa ta mamaye ilahirin wajan iskar data kasance mai daɗi sosai wacce ta haddasawa Halisa Dajeno rufe idanunta wani barci na fisgarta a hankali ta sulale a wajan babu jimawa barci mai nauyi ya ɗauketa. Kurciyoyin suka rikiɗe zuwa wasu samari masu zubin halitta ɗaya daga ciki wanda yake sanye da farar Alkyabba mai taushi wacce ta sauka har ƙasa ta rufe masa ƙafafuwansa yaja numfashi a hankali cikin ƙasa da murya ya ce "Danejona ba zata iya wasan nan ba" ɗayan dage gefensa ya ce "Haba Prince me ya sa kake da taurin kai ne? Sarki yace ka yanke duk wata alaƙa tsakaninka da bil-adam musamman wannan yarinyar Danejo amma kaƙi" murmushi mai taushi Wanda aka kira da Prince yai yana sake kallon Halisa Dajeno ya ce "A wannan karan ba zan iya yiwa Sarki biyayya ba, babu haɗi tsakanin mutum da aljani, amma kasan ba zan iya zutar da wani rai ba, muddin idan ba Danejo zai cutar ba? Na jima a jikin mahaifiyar Danejo tun tana da cikinta, amma rana ɗaya akai mata magani suka rabani da ita, wanda ya sanya na kwanta jinya, wannan dalilin yasa na koma kan ɗiyarta Danejo na shirya duk wani abu da sarki zai faɗa, ƙarshe dai ya ce zai koreni daga duniyar Aljanu ba?" Ɗayan zai magana Prince ya daka mishi tsawa ya ce "Ka saurara mini Safwan" ya faɗa idanunsa na juyewa zuwa kalar na aljanu a tsorace Safwan ya ce "Afuwa nake Yariman Aljanu, yanzu me ka shirya akan raba Danejo da wasan macijin nan?" Gyara Tsaiwa Prince yai tare da durƙosawa daidai inda Danejo take kwance tana barci ya ɗauke ta cikin nutsuwa ya ce "Ubangiji nake nema ya bani Sa'a, ina son Matata bana jin zan jure ganinta da duk wani wanda zai cuceta, balle kuma ya taɓa mini ɗana dake cikinta" buɗe baki Safwan yai da Mmki yace "Prince yaushe ta zama matarka? Har kuka samu ɗa?" Murmushi Prince yai yana shafa cikin halinsa wanda yake jin farin ciki na ratsa masa zuciyarsa kafin ya ce "Matata ce ita ɗin, duk wanda ya shirya rabani da ita to ya shirya zuwansa lahira, bani da lokacin magana Safwan, maza ku ɓace daga wajan nan" kamar gilmawar walƙiya haka suka ɓace, nan da nan Prince ya rikiɗe zuwa Almajiri mai yagaggun kaya. A nutse ya fara tafiya da ita zuwa cikin Rugar Rome dai da yaje daidai bakin bukkar su Danejo ya ajjiyeta da sauri ya bar wajan, sbd gaba ɗaya jama'ar Rugar suna filin da za'a gabatar da wasan Maciji. Prince ya ce "Ubangiji ka bani Sa'a da nasara" yana faɗin hakan yai Girgiza nan take ya zama ƙaton wani baƙin maciji mai narkeken kai a hankali ya sulale ya fara tafiya tsakanin bukkokin Rugar Rome har ya Ƙarasa wata bukka kai tsaye ya kutsa kansa ciki, kwance ya samu wani maciji shima baƙine sosai, da alama shi ne macijin da Matarsa Danejo zatai wasa dashi. Kallon kallo aka fara tsakanin Maciji Prince da kuma Macijin da Danejo zatai wasa dashi. Kamar haɗin baki haka suka fasa kai a tare lokaci guda kuma suka nufi kan juna.
🫣Bala'i🚶🏽♀️kada a manta labarin ya faru a gaske babu ragi babu ƙari👌🏾. Muje zuwa
#Sarautar marubuta
#True life story*🌈 IDAN BA KE 🌈*
Nimcyluv sarauta
_*Arewabooks@Nimcyluv*_
4.
A kusan tare macizan guda biyu suka ƙara fasa kai tare da kaiwa juna sara, ko wanne maciji ƙoƙarin jiwa ɗan uwansa ciwo yake da ganin ya kashesa har lahira. Gaba ɗaya macizan suka sarƙafe juna tare da nan na ɗewa waje guda ko wane huci yake yana fitar da hayaƙi ta baki nisan yadda Prince wanda ya a rikiɗe zuwa maciji ya matse macijin da Za'ai wasa dashi, gaba ɗaya ya ji masa rauni a hankali kuma Prince ya buɗe bakinsa ya fara haɗiye Macijin zuwa cikinsa sai daya haɗiyesa tsaf kafin ya sulale gefe guda ya kwanta yana mai da numfashi Wahala, sai fasa kai yake kamar zaici babu zuciyarsa tayo sama baki ɗaya zai iya sarar ko waye a wannan lokacin.
Sarkin ruga ya kalli tarin jama'ar da suke wajan hadda Shatu da Hamma Yabi, da sauran mutanan rugar kafin ya numfasa ya ce "Lokaci ya yi ake a kawo mana Halisa Dajeno Rome cikin fili, domin su fafata da maziji yau ranar tace" Wani mai suna Giɗaɗo ya rusuna tare da faɗin "Yanzu za'a kawota" yana faɗin hakan ya kalli Hamma Yabi tare da faɗin "Maza jeka kawo ɗiyar taku, tana ɓata mana lokaci" Hamma Yabi ya ce "Yanzu za'a kawota" yana faɗin hakan ya juya da sauri ya nufi bukkarsu tun daga nesa ya hangeta kwance a bakin bukkar inda Prince ya kwantar da ita tana barci.
Cikin sassarfa ya ƙara yana faɗin "Assha Subuhanallahi barci a ƙasa Danejo" ya faɗa yana ɗagota tare da jijjigata sosai, da sauri ya buɗe idanunta tana zabura "Hamma Yabi yaushe na dawo nan?" Kallonta yai ya ce "Kina nufin baki san lokacin da kika kwanta a nan ba?" Girgiza kai tai ta ce "Aradun Allah ban shina ba, kawai naji iska mai daɗi ta lulluɓeni wani barci yazo mini daga nan ban san komai ba" Girgiza kai yai yana kama Hannunta ya ce "Danejo ƙurushiya, maza muje sarkin ruga na jiranmu" dafe ƙirji tai cike da tsoro ta ce "Na shiga uku na lalashe, Kur'ani na manta yanzu hamma yabi shikenan mutuwa zan, zan mutu na bar Dada? Zan mutu banyi karatu na zama babbar mace ba? Don Allah kada na mutu yanzu bana son wasan nan" rirriƙeta Hamma Yabi yai sosai ya ce "Ma zaki mutu ba Danejo, sai na kai ki burni Kinyi karatu kin zama babbar mace abar ƙwatance, sai kin zama mace ta farko wacce zata kawo sauyi cikin Rugar Rome, ki daina kuka kinji" kai ta ɗaga masa kafin da sauri ta ce "Kuma zan zama wannan mutumin na jikin bango?" Zare idanu Yabi yai kafin ya ce "Wannan gwamna ne fa" murɗa baki tai cikin shagwaɓa ta ce "Ni dai irinsa nake son zama" Yabi ya dungure mata kai ya ce "Aradu ƙarya kike, ina zaki iya yin siyasa tayaya zaki zama gwamna daman mata na zama gwamna ne?" Banza tai masa bai ƙara ce mata komai ba ya jata zuwa filin da za'a gabatar da wasan.
Giɗaɗo dake tsaye shi da Sarkin ruga suna jiran zuwan Hamma Yabi da Danejo ya ce "Me ya sa ka zaɓi Danejo kasan ba zata iya wasan ba" murmushi Sarkin ruga yai kafin ya ce "Ina son ganin bayanta ne, kuma a hankali zan ƙarar da zuri'ar Manga a cikin Rugar nan, wannan macijin na tsafi ne hatta mutuwar Manga ni na shiryarta"... "Amma me Manga yai maka haka?" Cewar Giɗaɗo. Sarkin ruga ya ce "Sirri ne.." kaifin su ƙara magana Hamma Yabi ya ƙaraso hannunsa riƙe da Danejo wacce ta ƙanƙamesa sosai jikinta na rawa da ɓari.
Alƙalin wasan ya ce "Yawwa yanzu zamu fara, Danejo ta shigo cikin fili jama'a ku buɗe idanunku da kyau yau za kuga wasa wanda baku taɓa ganin irinsa ba" Halisa Dajeno Rome na tsakiyar fili ko kuka ta kasa a wannan lokacin ta tsaya ne kawai tana jiran taga ta inda mutuwa zata zo mata, domin abune mai wahalar gaske ace yau ta rayu ko ta tsira da ranta. Sarkin ruga ya bada umarnin a fito da Macijin, da sauri Alƙalin wasan ya nufi bukkar da macijin yake. Yana kwance sharkaf yau lamo a ƙasa tare da yin gammo da jikinsa, wani irin zabura yai tare da fasa kansa a lokacin da alƙalin wasa ya shigo cikin bukkar, ƙuri yai masa da idanu yana ƙare masa kallo. Ko me ya tuna Ohhu a hankali ya fara sauka daga dokin zuciyar ya koma ya kwanta, shi kansa Alƙalin wasan ya tsorata jikinsa na rawa yasa hannu ya ɗauki Macijin da ƙyar sbd nauyin da yake da shi.
Tun da Halisa Danejo Rome ta saka idanunta akan macijin taji gabanta ya faɗi, jikinta ya ɗauki rawa hawaye suka fara sintiri a saman Fuskarta, bata taɓa ganin maciji mai girman wannan ba, tama rasa wacce kalar addu'a zatai duk da ba wani abu ta iya sosai ba. Alƙalin wasan ya ajjiye macijin nesa da Halisa, aka fara kallon kallo tsakanin Danejo da Macijin, an shafe tsayin wasu daƙiƙo aka rasa waye zai fara kaiwa wani hari tsakanin Danejo da Maciji Prince?. Zaro idanu tai waje ganin ya fara warware tare da yin tsayi sululuuuu kuma ya nufo inda take, tana ja baya yana biyota har ya ƙaraso dab da ƙafarta tare da tsorawa zoben hannunta idanu. Juya tai tana neman inda zata gudu can idanunta ya sauka akan wani ƙaton dutse. Da sauri ta ɗauka tare da riƙewa a hannunta, ganin haka yasa Macijin bin ƙafafuwanta suuu haka ya dinga sufa a jikinta, har ya naɗeta ciff kansa daidai Fuskarta yana tsora mata idanu tare da kallon cikin idanunta.
Jirkinta na ɓari ta ɗaga dutsen tare da kwaɗa masa a tsakiyar kansa, wani kalar ihun azaba macijin yai yana fasa kai kamar zai sarata, sai kuma ya saki kansa tare da ɗorasa saman ƙirjinsa gaba ɗaya naman Macijin rawar azaba yake, kansa tuni ya fashe ya fara zubar da jini. Ganin nasarar da Halisa Danejo Rome ta fara samu yasa Hamma Yabi da Shatu tare da sauran jama'ar Rugar Rome suka fasa ihun murna, Sarkin ruga da Alƙalin wasan hankali tashe suka kalli juna tare da faɗin "Me ya samu macijin nan? Ki dai asiri akaiwa Yarinyar nan?".
Halisa a tsorace Macijin a tsorace amma a haka cikin dakiyar zuciya ta ƙara ɗaga dutsen a karo na biyu ta ƙara bugawa Maciji, Innalillahi a wannan lokaci kururuwar da Macijin yai sai da kowa na wajan yaji, jini ya sake ɓalle masa a hankali ya sulale ƙasa baya ko motsi alamar ya mutu... ajjiyar zuciya ta sauke haka kurum taji kuka ya ƙwace mata, durƙushewa tai a wajan ta shiga rera kuka tausayin macijin ya kamata musamman yadda taga jini na zuba a jikinsa, Hamma Yabi ya ƙaraso wajan Halisa Dajeno Rome tare da ɗagata yana dariya ya ce "Danejon Dada kin kashe macijin, kin kashe sa bana faɗa miki cewa ba zaki mutu ba? Zamu samu ƙwayar nono da Nagge masu yawa" ƙanƙame Hamma Yabi tai cikin kuka ta ce "Bana so Hamma Yabi, mu bar nan wajan kaina juyawa yake, bana son ganin jinin nan kaji" hannunta ya kama sukai gefe guda. Cike da taƙaici Sarkin ruga yake bin Macijin da kallo bai taɓa tunanin haka ce zata kasance ba, cike da baƙin ciki ya amshi wani sanda ya shiga kwarɗawa macijin aka tun macijin na motsi har ya daina jikinsa yai face face da jini tare da raunuka. "Ka ɗauke sa ku cillar a gefen gaɓar ruwa wani abin yai kalace dashi" Giɗaɗo da Alƙalin wasan suka ɗauki Macijin tare da nufar cikin jeji da shi. Suna zuwa suka cillar gefe guda da sauri suka juya cikin Rugar Rome.
Sanyin gaɓar ruwan daya ratsa cikinsa ya sanya ya fara Girgiza yana juyi tare da murmurɗe jinsa gefe guda, wani kalar ihu yake mai nuni da azabar da yake ciki, ya daɗe cikin wannan halin kafin yai Girgiza tare da rikiɗewa ya dawo siffarsa yadda yake fitowa a mutum ba Aljani ba, yana kwance sambal gefen ruwan Farar Alkyabbar jikinsa duk ta ɓaci da jini. A hankali ya ɗaga hannunsa tare da dafe kansa inda yake zubar da jini, runste idanun yai sosai cikin ƙasa da murya ya ce "Ya Allah" yana nan ƙwance yaji iska ta mamayesa baki ɗaya kafin kace wani abu iskar ta ɗaukesa zuwa sama.
Duk farin cikin dasu Shatu suke ciki banda Danejo rasa abin da yake mata daɗi tai, gashi jinin Dada ya matsa ga tunanin dake wanzuwa a cikin zuciyarta. Dada ta kalli Shatu ta ce "Farin ciki za kiyi Halisa ba damuwa ba, da tuni an rabani dake Allah bai ba, akwai ƙaddarorin da suke biye dake, amma duk wahala duk tsanani waya rana zaki zama abar ƙwatance tabbas zaki samu miji