Showing 57001 words to 60000 words out of 197828 words

Chapter 20 - IDAN BA KE 1 TO 2 COMPLETE By Na'ima Suleiman Sarauta Nimcey luve .txt

12 Dec 2024

9335

ya sauka akan Halisa wacce ta cure waje guda tana barci, ya tsaya cak tare da kallon Umar-khan, Umar ya nufi ɓangaren Ummul babu jimawa suka dawo tare, Ummul ta kallesa ta ce "Malam za a fita ne?
Ba kaci abincin kirki ba?" Ya ɗan ɗauke kai zuwa hanyar fita yana faɗin. "Sanyi zai illata ta, a sauya mata waje" sai a lokacin Ummul ta lura da Halisa.
"Tom babu damuwa, Allah ya tsare" ta nufi wajan Halisa ta shiga tashinta tare da faɗin "Matar Malam, matar Malam" ta buɗe ido tana kallon Ummul ta ce "Maza ta shi ki koma ɗaki, a kwai sanyi zai kama jikin ki" ta buɗe ido sosai ta ce "Anti Zahrah ta dawo ne?" Ummul ta ce.
"Fita tayi ne? ta shi lokacin sallah ma ya yi ai muje ko" har part ɗin Halisa Ummul ta shiga, akan idanunta Halisa tai alwala kana tai Sallah. Ummul ta ce "ƙarfe biyar kizo ɗakina, zan nuna miki yadda ake cikakkiyar sallah, na fara karanta miki Alkur'ani, yanzu ki kwanta wajan ƙarfe 4:30 ki tashi ki wanka ki wanke baki, ki sauya komai na jikin ki, kinji ko?" Ta tura baki sosai ta ce "To wannan duk na mene Ummul" Ummul ta ce "zaki sani ne" ta fice daga ɗakin.
Yaa na fita kai tsaye Al Masjid an Nabawi ya nufa sbd wani karatu da yake dashi na musamman, kuma acan yake son yi Sallah ma, da kuma zaman tattaunawa da za su yi da mahukunta kula da Masallaci harami ana son naɗa Yaa Sheikh Aliyu haydar Aliyu matsayin limamin masallacin Haramin wanda zai jagorancin sallar Taraweeh da Tahajjud, gaba ɗaya azumi saura wata guda ya rage a fara.
Tamkar uwa mahaifiyya haka Yaa Sheikh ya ɗauki Ummul yana ɗaukan minti goma yana magana da ita, tasan kusan komai nasa kuma tasan da yawa abin da Mother bata sani ba, tunda yafi rayuwa a Madina fiye da Nigeria. Sai bayan sallar issha Zahrah ta shigo a gajiye tana tafiya da ƙyar idanunta ya yi jaa, Halisa ta bita da idanu ganin yadda take tafiya kamar yaron da akaiwa shayi. Duk yadda Halisa tasu taga dawowar Yaa Sheikh bata gani ba, barci ya ɗauketa a Main parlour. Ƙarfe 12:30 ya shigo gidan shi kansa a gajiye yake sosai, ganinta a parlourn ya sanya ya tsaya yana binta da idanu, a hankali ya dubi lokaci sai kuma ya shige part ɗinsa.
Kiran sallar asuba ya farkar da ita, da mmki take bin makeken gadon da take kai da kallo, an rufe ta da wani haɗaɗɗan duvet mai ƙamshi ga laushi an kuma rage ƙarfin a.cn ɗakin, ita dai tasan a parlour ta kwanta waya kawota nan? Ko ita ta shigo da kanta.
Ta miƙe ta nufi toilet yadda Ummul ta koya mata haka tayi, tai wanka da ruwan zafi ta shafe jikinta da Vaseline Intensive Care Cocoa Glow Body Lotion.


Shiryawa cikin Abaya ta ɗora hijab a nutse take duba littafan da Ummul ta bata, Ubangiji ya bata fikirar hadda ce, da yawan lokaci ita abu a kanta yake zama, duk wani abu mai muhimmanci bata wasa da shi. Tana zaune taji saukar muryarsa a kunnanta yana data kabbarar sallah, shiru tai bata taɓa tunani muryar shi takai daɗin haka ba sai yanzu. Sallah ta gabatar sannan ta nufi ɓangaren kitchen ta samu tuni sun Bara'at sun fito. 6:30 Ummul ta ce tayi sauri ta shirya za a kaita makaranta, wani tsalle tayi ta rungume Ummul daɗi ya kamata jin za a kaita makaranta abin da take buri a rayuwarta. Ta shirya ta fito tsaf a cikakkiyar ƴar fillonta Ummul na ganinta tai murmushi tana cewa "Kije ki gaida Abban naki" Halisa ta ce "Abba kuma Ummul" ta ce "Eh, uban riƙon ka ai uba ne jeki maza" hannunta ɗauke da yam balls ta nufi ɓangaren shi.
Cikin siririyar murya tai sallama tare da shiga tsaye ta gan shi cikin kyakkyawar shiga mai ɗan kauri sbd sanyin garin da aka tashi da shi, hannunsa goye a bayansa ta ƙarasa cikin da sauri tana durƙusawa har wajan ƙafafuwan shi ta ce.


"Jamɓanduna,
Noi sare,Noi kuɗe" ta jera hausuwar ma'ana _“Ina kwana, ya ya gida, ya ayyuka”_ ya ware gajiyayyun Idanunsa a kanta, yana bin shigar makarantar nata, ta ɗaga kai ta gan shi tsaye ta miƙe tana kallonsa, ya dubi yam balls ɗin hannunta da raguwar na gefen bakinta. "Jiya nai barci baka dawo ba, yanzu kuma wai makaranta za a kai ni inji Ummul" ya jinjina mata alamar _"Eh"_ yana ƙoƙarin juyawa tayi saurin riƙe ƙugunsa da hannu ɗaya ta ce "Miyetti masin, Allah ya ƙara arziƙi"
Ɗan ƙaramin bakin maganar kawai yake bi da kallo, gumi na tsastsafo masa ta goshinsa ta saki kyakkyawan murmushi ta ce "Mijina" da sauri ya kalli cikin idanunta ta ɗauke nata idanun sai murmushi take sbd daɗin zata makaranta.


A hankali ta buɗe baki a taushashe kuma cikin ƙasa da murya ya ce "Matar m......" Maganar ta tsaya sbd yam balls data tura masa a cikin baki ta dinga tsalle tana cewa "Nayi maka wayyo daman ance baka cin abinci" ya lumshe fararen idanunsa tare da nufar kujera har lokacin tana riƙe da shi. Yana zama ta zauna a ƙasa Yaa Sheikh sai mai da numfashi yake sam bai niyyar cin komai ba, bisa dole ya shiga tauna yam balls ɗin bakinsa yana goge zufar dake goshinsa, wanda kuma shi kansa ya san zufar ta mece ce. Ya ɗauki bottle water tare da tsiyayawa a cup bayan ya sha ruwan ya mai da numfashi. Halisa ta ce "nace Ummul tayi maka wani na cinye gaba ɗaya tas" gently ya buɗe idanun a kanta ganin yadda yake bin fuskarta da kallo sosai yasa tai masa kyakkyawar murmushi tana lumshe idanu tare da buɗewa kamar yadda yai, a hankali ya ɗan ranƙwafa daidai kanta ya sanya fararen tafukan hannayensa tare da kama fuskarta da kyau babban hannunsa yasa yaja kumatunta numfashinsa na sauka a fuskarta ya ce.
"Zaki fasa mini kai da surutu Matar Malam, shiru kan na ɗinke bakin......


Not edited
Paid book
₦500
08119237616
Sarautar marubuta.


_Ubangiji ya haɗamu da alkairan da suke cikin jumma'h. Mu haɗu Monday🥰❤‍🔥_Da fararen idanunsa masu tsari yake bin ta da idanu da mamaki, ganin da gaske bata mutsi tsoran da ya yi mata yawa ya sanya numfashinta ya ɗauke, hannunsa basu taushi ya sanya akan fuskarta kamar mai jin tsoran gently ya shiga bubbuga kumatunta amma ko motsi ba tayi ba, ya ɓata fuska ganin tun ba a je ko'ina ba, yarinyar zata fara bashi wahala.
Yatsun hannunta biyu ya kama yaja da ƙarfi yana buga tsakiyar kanta ajjiyar zuciya ta sauke da ƙarfi tana jan numfashi, sai kuma ta fashe da kuka tana riƙe wanda taji kusa da ita sosai cikin fillatanci take faɗin.
"Don Allah ku sakko dani ƙasa zan mutu wayyo Dada wajanki zan dawo" saukar numfashin da yaji yana sauka a fuskarta da ƙamshin da ba zata manta da shi ba ya sanya ta buɗe idanunta wanda ta rufe su saboda tsoro, wanda ta gani take jikinsa ya bata mamaki numfashinta ya kusan ɗaukewa, sbd yadda ya yi mata kwarjini a idanu ga Alkyabbar jikinsa duk ta rufe mata jiki, a jikinsa yaji shi take kallo bai kalleta ba, ya sanya hannu tare da riƙo kafaɗunta da kyau yana zaunar da ita akan kujerar sosai.
Yana daga inda yake ya ranƙwafa sosai tare da miƙa hannu zuwa inda blet ɗin take, kwantaccen sajansa ya shafi fuskarta ta sauke numfashi mai zafi wanda ya sanya Yaa Sheikh daka tawa da kama blet ya jima kafin ya zaro blet ɗin da sauri ya maƙala mata, yana ƙoƙarin janye jikinsa ta ɗora hannunta a tsakiyar tafin hannun shi..
"Uhmmm" ya ce a ransa yana ɗaga idanunsa zuwa gareta ya kalli cikin idanunta ba tare da ya ce komai ba, Halisa ta sake damƙe hannunsa da kyau cikin rawar murya ta ce. "Usako miyetti masin" idanu kawai ya lumshe mata tare da matsawa waje guda.
A fusace Zahrah ta kunce blet ɗin jikinta tare da tashi tayi kan Halisa tana kumfar baki ta ce.
"Ke dan uwarki mijina sa'anki ne da har zaki faɗa kansa da ƙazamin jikinki? Shegiya mara ƴan ci" Halisa ta kalli Zahrah ta ce "To Anti godiya nayi masa fa, kuma dana faɗa ƙasa naji ciwi ba ƙwara na faɗa kan shi ba, kuma ai ban masa nauyi ba ko kaji ciwo?" Ta faɗa tana juyawa tare da kallon Yaa Sheikh, shi gaba ɗaya hankalinsa baya kansu hannunsa riƙe da darija yana dubawa, tuni ya mayar da hiramin kansa baya buƙatar kowa yaga wani sashe na jikinsa.
"Kauuu!!" Zahrah ta ɗauke Halisa da mari tare da nuna ta hannu ta ce "zanci uwar data haifi babarki" ƙarfi da girman zagin yasa Yaa Sheikh kallon Zahrah a zuciyarsa yana Istigifari bai ɗauka wani zai iya zagin ba, ba a taɓa zagi a gaban shi ba, hakan ya zama abu sabo a gare shi. Bai ce komai ya ɗauke kai tare daci gaba da duba jaridar hannunsa, zafin marin yasa Halisa fashewa da kuka sosai tana kifa kanta a cinyarta, kuka take sosai wanda rabin kukan baƙin cikin zagin da Zahrah tayi mata ne. Yaa Sheikh kukan yake ji har tsakiyar kansa jin kukan na neman tarwatsa masa kai yasa ya miƙe tsaye tare da buɗe wata ƙofa ya shiga.
Zahrah ta kasa haɗiye mamakin yadda Yaa Sheikh ya nuna kulawa ga Halisa, haushin abin da ya yi yasa ta huce akan Halisa ɗin.
Sun yi nisa da tafiya sosai wata maid ta shigo cikin wajan tana tambayar Zahrah me za a kawo musu, Zahrah ta karɓi abin hannun matar ta duba, kana ta zaɓi abin da take so. "Nace ko zaki iya sauyawa wannan yarinyar waje?"Flight attendant ta ce.


"Her name please?" Zahrah ta ɗan kwaɓe fuska ta ce "Something Halisa.." ta ɗan danna wani abu a jikinta tare da yin magana bayan ta gama ta ce. "I think ita ce Halisa Sheikh Aliyu haydar Aliyu right Maah?" Zahrah ta ce "No, bana tunanin ita ce her name is Halisa Danejo Rome" Flight attendant ta sunkuyar da kanta ƙasa ta ce "Sorry Maah babu da wani suna a jerin wanda za su yi tafiya yau, Halisa Sheikh Aliyu haydar Aliyu shi ne" A fili Zahrah ta ce "Kan uba" sai yanzu ta tuna sunan Yaa Sheikh kenan, da sunansa akai mata visa kenan?.
"Oh maybe she's the one, zaki iya sauya mata wajan zama?" Matar ta ce "Yes Maa, daman yanzu na duba ta samu sauyin wajan zama tuni" Zahrah tai murmushin jin daɗi matar ta kalli Halisa wacce ko inda suke bata kalla ba sai Ajjiyar zuciya take saukewa.
"Can you follow me please?" Zahrah ta ce "ki mata hausa maybe she understand you" matar tai murmushi ganin yadda Zahrah take kwaɓe fuska ta ce "But she's your daughter?" Wata uwar harara Zahrah taiwa matar ta ce "Kinga alamar ina da ƴar ne?" Ita ma tai murmushi ta ce "Ai babu mmki idan nace miki a tunani zaki haifi yara biyar ma" Zahrah ta kalli jikinta da kyau ta kasa cewa komai, sbd baƙin cikin Flight attendant.
"Halisa biyo ni kinji" a sanyaye duk da tsoran jirgin da take tabi bayan matar har zuwa champer 2 na jirgin. Nan ma dai kujeru biyu ce kawai a wajan ba kowa, ta nemi waje ta zauna cike da tsoro.
Not too long da zamanta ya shigo tare da zama kan kujera da sauri ta sunkuyar da kanta domin a tunaninta faɗa zai mata, sai taga mai kulata ba ƙafarsa kawai ya miƙe. Tana zaune aka turo basket na abinci, zallar fruits ne sai gorar ruwa, aka ajjiye a gaban Yaa Sheikh ita kuma aka ajjiye mata chips da egg sai haɗin salad da ruwa. A hankali ya ɗauki orange ya saka bakinsa ya shiga taunawa cikin nutsuwa, Halisa ta kalle shi bakinta na rawa ta ce.
"Amma wannan abin yabann sha'awa ɗan sammani" ya jita sarai amma yai mata banza sai da orange ya ɗin ya rage guda uku ya ɗauki guda ɗaya zai ƙara sakawa a bakinsa tayi saurin riƙe hannun shi, bai zaici haka ba ya kalli hannunta tare da kallon gefen fuskarta ta langwaɓar da kanta gefe ta ce "Ayya ka sammin bana, ni ma idan kaga abuna zan maka naga kana ta haka da idanu" yabi idanunta da kallo yadda ta lumshe su tare da buɗewa tana gwada masa yadda yake, ta kwance na hannunsa tare da kawai bakinta, ta ɗauka wani daɗi ne a orange ɗin.
Ya sauke numfashi ganin hannunta na neman taɓa dugun gemun shi cikin ƙasa da murya mai sanyi ya ce. "Ci kani" ta yi saurin saƙona tana komawa wajanta, bai ƙara taɓa komai ba a kayan sai ruwa daya sha sosai.
Misalin 10 na dare jirginsu ya sauka a Prince Muhammad bin Abdul'aziz International airport, sai nasarwa ake kowa ya saka blet jirgi zai sauka, ganin bata fahimci me ake cewa ba ya kalleta da kyau, ya riƙa ya saka blet a jikinsa ba damar cirewa kuma sun ɗan bada tazara, a hankali jirgi ya fara girgiza yana rawa Halisa ta rikice daga tai nan sai tayi nan, shuuuuu jirgin ya yo ƙasa tai gaba luuu zata kifa shiru tayi jin an riƙo kafaɗar ta, ya haɗa da gefen ƙirjinsa tare da riƙeta.
Ƙuri tayi masa da idanu ganin nasa idon a rufe ta kasa motsawa shima kuma bai saketa ba, tunda har lokacin jirgin bai gama daidaita ba, balle ya samu damar sauka a titinsa. Ɓangaren Zahrah sosai taji daɗin ganin an ɗauke Halisa yanzu zata samu damar kasancewa da mijinta hankali kwance, sai dai tun tana jiran dawowar shi amma shiru gashi bata da ikon tambayar wani, bisa dole tai shiru. Bata tsammaci abin haka ba, sai ji tayi ana faɗin sun ƙarasu Madina tuni ai. A hankali ta saka blet tasan dai dole tare zasu tafi gida. Jirgi na yin parking ya saketa da sauri kafin ta buɗe ido ya fice daga cikin wajan, ta shiga zare idanu yanzu idan guduwa sukai yaya zatai?. Tana wannan tunanin Umar-khan ya shigo yana murmushi ya ce "Matar Malam tasu muje" ta miƙe tana kallon Umar-khan ta ce "To kai gida kaje ka dawo ne?" Yai dare ya ce "Hhhhhh ai kam na koma Nigeria na dawo" tabi bayansa da sauri ta ce "Kasan me" ya ce "sai kin faɗa" ta lumshe idanun ta buɗe ta ce "A ciki da abin ya tashi sama kawai na faɗa kan Malam na ɗauka zai dukeni kamar yadda anti da dake ni, sai naga kawai ya lumshe idanu ni kam nace masa na gode"


"Uhm" kawai Umar-khan ya ce domin bashi data cewa a wanann batun, suna fitowa Zahrah na fitowa suka kalli juna da Halisa kowa ya ɗauke kai. Bayan sun sauka daga jirgin Zahrah ta kalli motar dake gabansu ta ce "Ina My Excellency?" Ya ce "Yana da meeting ne, sai zuwa 12 zai dawo" Zahrah ta ce "meeting da wannan daren?" Umar-khan ya ce "Manyan mutane daman sai dare suke meeting, muje kada mu ɓata lokaci" Zahrah ta shiga bayan mota Halisa ba haka, Umar-khan na gaba shi da driver.
Wata haɗaɗɗiyar area suka nufa gaba ɗaya mazauna wajan larabawa ne, gidan dake kusa da na Yaa Sheikh sune hausawa, faɗar kyau da tsarin gidan Yaa Sheikh ɓata baki ne, flat gida na zamani, motoci birjik a harabar gidan ga tarin flowers da ɓangaren swimming pool, ga
Wajan tsuntsayen shi kusan duk rubutun gidan da rabci ne, yana da ɓangare na Musamman da yake bawa manyan mutane darasi.
Zahrah ta dubi haɗaɗɗan parlourn mai ɗauke da wasu ƙawatattun kujeru, sai ƙamshi yake, ga wasu fitito masu kyau iya haɗuwa ya haɗu. Umar-khan ya kammala shigo da kayansu ya ce. "Ɓangare uku ne a gidan, wancan ɓangaren Yaa Sheikh na tsakiyar kenan, na gefen dama babu na kowa na hango ma babu kowa, ya ce ki zaɓi wanda kike so, ɗayar ki bawa mai aikin naki" Zahrah ta kalli part ɗin hannun hango taga bayan na Yaa Sheikh yafi kyau dan haka ta ce "Na ɗauki na ɓangaren hango ka shigo mini da kayana ciki" tana faɗin haka ya miƙa mata key ɗin ɓangaren ta amsa hana shigewa ciki. Ya kalli Halisa ya ce.
"Daman girman kine shiga ɓangaren damar" murmushi kawai tayi, Umar-khan ya riga yasan da ɓangaren Yaa Sheikh da wanda Halisa zata zauna a manne suke, domin akwai ƙofa kai tsaye daga ɗakin Yaa Sheikh wacce zata kawo shi ɓangaren Halisa ɗin. Ya ja mata kayan zuwa jiki, ya yi mata bayanin komai da kitchen da banɗaki komai dai, kana ya nuna mata yadda ake amfani da kayan kallon ɓangaren ta.. "Sai da safe Matar Malam" ta jinjina masa kai. Zahrah ma ya kai mata kayan kana ya nufi nasa gidan.
Misalin 1:30 motar Yaa Sheikh tai parking driver ya buɗe masa ƙofa, a hankali ya fito ya ɗan tsaya yana duba ko wanne ɓangare yana yin addu'a sbd ya saba, ganin hadari a garin kuma yasa duk ya rufe Windows na gidan. Ya nufi ɓangaren shi, wanka ya yi ya ɗora jallabiya mai kyau a jikinsa, black tea yake son sha amma bai san yarda zai ba, gashi kuma yasa a sallami masu aikin shi. Haka dole ya zame jallabiyar ya saka kayan barci yana buƙatar hutawa sosai, sbd ya samu peace of mind kwana biyu yana stressed kansa da yawa. Kiran sallar farko a kunan Yaa Sheikh da Halisa domin zamanta wajan mother ta saba da tashin asuba, a hankali ya nufi bathroom tare da sakarwa kansa ruwa mai zafi kana ya yi alwala tare da yin brush, cikin zafin nama ya shirya cikin kyakkyawar shigar shi wacce ya saba, farar jallabiya ya ɗora hirami a kan shi, bakinsa ɗauke da aswaƙ ya nufi Masjid Malik wanda shi ke gabatar da jam'i a can, bayan idar da Sallah ya yi karatu wa jama'a kamar yadda ya saba.
7:00 ya shigo gidan da mmki yake jin parlour ƙamshi mai daɗi, yana ƙoƙarin shigewa part ɗin shi ta ce "Jamɓanduna?" Jin fillatanci yasa ya fahimci ba Zahrah bace amanar shi ce kuma ƴar riƙonsa, ya juya tare da kallon ta, tana cikin wata duguwar riga mai kyau plush pink sai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login